Kenza eBookz

Sanadin labarina complete novel - Chapter 6

Sanadin labarina complete novel - Chapter 6

Sanadin labarina complete novel Chapter 6: Sanadin labarina complete novel Chapter 6. yace yana maida wayar saitin ta,ya kashe flash din ya shiga daukar ta…

4,400 words

yace yana maida wayar saitin ta,ya kashe flash din ya shiga daukar ta pretending ba dauka yake ba, sai da ya dauke ta sosai sannan ya kunna flash din yayi mata guda daya, sannan yayi ma Safeera ma. Daga nan suka tafi ita kuma ta koma cikin gidan. Suna shiga gida Safeera tayi dakin Mom shi kuma ya wuce dakin sa, ya bude wayarsa ya shiga photos ya zauna zaman kallon hotunan yana admiring kyauwun ta, idanun ta da dan karamin lips dinta shi yafi komai burge shi da ita, yana zaune yana ta kalla Farouk ya shigo, ya fizge wayar yana kallon screen din, kafin ya kalli Isma'il din irin kallon tuhumar nan,

"Kana nufin... No no no it's not possible, wannan ai child abuse ne."

"Inji waye? Rainon ta zanyi."

"Are you serious? Wannan yar yarinyar zaka tsaya jira?"

"Yes of course, menene a ciki?"

"No you most be kidding, ai ba zai yiwu ba."

"Kasan Allah? I'm serious, very very serious. I love her, with every bit of me,love at first sight, so mara algus kenan."

"But she looks so local, beside yarinya ce karama sosai, not your type though."

"Kai kaga haka, ni na san me na gani."

Kifa wayar Farouk yayi a saman gadon yana zama akan couch din dake dakin ya maida kansa baya yana rufe idanunsa sannan yace

"Ba zan iya cigaba da sauraran wannan tale din ba."

"Yafi maka, kuma zan baka mamaki."

"Allah ya bada sa'a, mu namu dai ido ne."

"Yafi dai."

***Monday akayi resuming school, da wuri Isma'il ya tashi ya shirya ya fito falo ya samu Safeera tana breakfast, Mom kuma tana karasa hadawa daddy breakfast dinsa, kallon shi tayi cikin yanayin mamaki tace

"Ina zaka? Kai da baka tashi sai kusan 11, ko kana da morning lectures ne?"

"Safeera zan kai school." Yace yana hayewa saman dinning din, kallon sa duk sukayi da mamaki, ya share ya hau bude warmers din yana lekawa, ba zai iya cin komai ba sai ya dawo dan he's so eager ya ganta baya so su riga su zuwa har su shiga class shiyasa ma ya shirya da wuri ya samu itama Safeera ta shirya. Ajiye ragowar sandwich din hannun ta,tayi ta mike ta sakala school bag dinta a kafadar hannun ta daya tace

"Na gama Mom." Mikewa yayi shima yace

"Oya let's go karki makara."

"Malam Sa'idun fa?Kamar yazo fa tun dazu."

Mom tace cikin rashin gane kan Isma'il din.

"Na hutassheshi, muje kid sis."

"Ok."

Tace tayi ma mom sallama suka fita tare, girgiza kai mom tayi a ranta tasan dole akwai dalilin da zai saka shi fita da safen kawai ya boye mata ne. Malam Sa'idu dake zaune a cikin mota yana jiran ta yaga sun fito ya bude motar da sauri Isma'il yace

"Zan sauke ta Baba, kaje gida kawai."

"Toh toh, shikenan."

Ya tada motar ya fita daga gidan suma suka bi bayan sa. Suna cikin tafiya ya tambaye ta

"Karfe nawa su jidda suke zuwa school?"

"Umm, ina rigasu zuwa gaskiya, kaga suna da yawa sai sun gama shiryawa."

"Good!" Yace yana murmushi

"Na'am?" Ta kalle shi

"No ba komai." Ya basar yana sake rike motar, cikin kankanin lokaci suka isa school din, kudi ya ciro a cikin wallet dinsa ya bata,

"Mom ta bani fa."

"Eh ku kara ke da Jidda, ku siya duk abinda kuke so."

"Ok thank you." Ta karbe ba tare da ta kawo komai ba, ta shiga school din bayan ya ja motar a tunanin ta, ya tafi. Gefe ya samu yayi parking ya zauna zaman jiran zuwan su, idanun sa na kan duk me wucewa ta cikin layin, har zuwa sanda suka iso, ya bude murfin motar da sauri ya fito ya tsaya jikin motar yana kallon su, a in da yake tsaye ba zasu ganshi ba amma shi yana kallon su, Amira ce ta fara fitowa sai ita, cikin uniform din nasu navy blue da white Hijab wanda yayi matukar yi ma yar fuskarta kyau, tamkar yar tsana haka ya ganta, gashin da ke kwance a gaban goshin ta ya fito sama-sama wanda ya karawa kyakyawar fuskar ta kyau. Wani abu yaji ya tsirga masa, ya jingina sosai da motar dan ji yake tamkar yana yawo a gajimare, yana nan tsaye har suka shige cikin school din sannan ya sauke ajiyar zuciya ya fada motar ya bata wuta ya fita daga cikin line din a guje.

[03/10, 21:27] Mss Xoxo: ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

😄😄😄😄😄😄😄

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [05/10, 16:20] Billyn Abdul 2: *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*

*ZAFAFA BIYAR BACTH A*

1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)*

2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)*

3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*

1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)*

2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)*

_Duk biyar 1500_

*______________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_*

1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)*

2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)*

3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)*

4... _INAYAH_ *(Mamu gee)*

5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)*

_Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_

*YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:*

_ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR*

_BANK NAME:_ *ZENITH BANK*

_ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_*

_SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_

*_07040727902_*

_IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_

*_09134848107_*

*_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**

©®*_*_Hafsat Rano_*_*

Page (11)

***Jidda da Usman ne kawai a falon tana karatun Qurani Baban ya shigo, karo na farko tun zuwan ta gidan da taga Baba a part din nasu, da sauri tace.

"Baba sannu da zuwa."

"Yawwa Hauwa'u, ana ta karatu?"

"Eh."

"Toh Masha Allah, a bada himma ko?"

Daga kanta tayi,ya dauki Usman ya wuce dakin Aunty. Tana zaune jigum duk babu dadi, dawowar ta ciki kenan ta bar jidda ta usman a falon so take ta dan kwanta ko kanta dake sara mata da ciwo zai rage, sai ganin Baban tayi ya shigo dauke da usman. Mamakin ganin sa ya sakata tashi da sauri

"Sannu da zuwa." Tace tana kallon shi, shima ita yake kallo, ta rame sosai tayi haske,

"Kin ganki ko Halima?"

Sunkuyar da kanta tayi k'asa, ya girgiza kai yana daga tsayen yace

"Idan fa baki cire damuwr komai ba fa zamu bata gaskiya."

"Na cire, kai na ne yake ciwo."

"Ehen, kinji ko? So kike sai kin kwanta zaki ji dadi ko?"

" A'ah." Ta girgiza kanta tana jin wasu hawaye masu zafi na neman zubo mata

"Toh bana so, ki dawo yadda kike kiyi rayuwarki yadda Allah ya tsara miki, bakya bukatar fahimtar da kowa baki da hannu a abinda ya faru,duk wanda ma ya zarge ki kansa, ke dai ki tsarkake zuciyar ki."

"In sha Allah, Nagode."

"Madallah, a taimaka min na watsa ruwa na dauko gajiya, sannan a dan bani Lipton kadan."

"Tohm." Tace ya juya ya bar part din, turare ta dan fesa a jikinta tabi bayan sa zuwa part din sa.

***Hannun sa dauke da ledoji niki-niki ya shiga part din Yayan, tana ganin shi ta dalla masa harara, kafin idanun ta su sauka akan hannun sa, daga mata ledar ya dinga yi ta washe bakin ta bayan ta hango ayaba, a gabanta ya ajiye ledojin sannan yace

"Gimbiya Yaya ga shi inji sabon angonki, wato ni."

"Me karya?"

"Dan aljanna."

"Kai tafi chan, d'ana ne ya siya min ba kai ba, mai alkawarin da baya cikawa tir!"

"Toh ai Yaya kece da rowar tsiya, kinga ai kin bani ba dan Allah na."

Jefa masa pillow din kujera tayi ya chafe yana dariya.

"Bari na dauko mana plate mu bajeshi mu kwashi dadi."

"Naga uban da ya isa ya taba min, wallahi baka isa ba."

"Ni fa na siyo, naji kamshi amma kice ba zaki bani ba?"

"Ai ba dan Allah ka siyo ba."

"Ai shikenan, aci lafiya."

"Ka ja min kofa idan ka fita." Tace tana tattare kayanta, ta shige uwar daki ta bar shi yana dariya.

***Da safe Tariq ya gama shiryawa cikin kananan kaya bakar long sleeve shirt da black trouser ya dora brown katotuwar rigar sanyi akai,hannun sa sanye da handsocks me kauri, sai kafarsa da ya saka socks wajen hudu ya dora brown takalmi. sake gwada kiran wayar Auntyn yayi hannun sa daya rike da cup din tea me zafi, har ta gama ringing ba'a dauka ba, a aljihun wandon sa ya saka wayar ya goya jakar da tarkacen takardun sa hade da system ke cika, ka fito ya hau lift ya sauka kasan building din, ya shiga takawa a kafa zuwa cikin makarantar da basu da nisa da gida, pcap ce akan sa da ta sauko har wajn girar sa, baya kallon kowa tafiyar sa kawai yake yana shirya abinda zai gudanar a ranar.

"Hi."

Ta tsaida shi ganin kamar be lura da ita ba, dagowa yayi ya kalle ta, ta sakar masa murmushi tana kallon fuskar sa

"Hi." Shima ya maida mata kafin ya cigaba da tafiyar sa, da dan saurin ta, ta cimmasa, ta sake tsaida shi

"Baka gane ni ba?"

Ta tambaya ganin yana mata kallon wacece ke? Girgiza kansa yayi, sannan yace mata

"Ban gane ba."

"Okh, mun hadu a library last week har na karba pen dinka nayi signing, ka tuna?"

"Oh yeah, na tuna. Sannu."

"Yawwa, thank you."

"Amm...sauri nake ina da meeting da supervisor dina, bye."

"Bye!" Ta daga masa hannu, ya juya ya cigaba da tafiya, ta tsaya a wajen tana kallon sa har ya shige cikin building din.

"Perfect!"

Ta furta tana jan ajiyar zuciya.

Apartment dinsu daya tun ranar da suka hadu a library ta bishi sai ta ga ashe gida daya suke shi amma yana 5th floor ita kuma tana 2nd, tun daga ranar take min duk wani moves dinsa,shi kadai yake rayuwar sa, sai abokan sa biyu daya shima dan Nigeria ne sai wani dan China, sosai yayi mata har ya zama kullum sai ta makale ta leka shi da safe idan ya fito zai tafi exercise, wani lokacin har chan take bin shi ya gama ta sake biyo bayansa su dawo tare amma bata taba bari ya gane ba. Bata da abinda zatayi a cikin school sai kawai ta koma gida ta kwanta sai da rana take da lectures dama dan kawai su hadu ya sakata fitowa a lokacin. Yau da taji muryar sa sosai sai take jin kamar an saka ta a aljanna, he has something a cikin voice dinsa da ya sakata kusan suman tsaye, very deep and sweet.

****Shigowar aunty kenan daga part din Baba ta dau wayarta, taga missed calls dinsa, ta tuna jidda ma tace ya kira shaf ta manta bata kira shi ba, yanzu kuma ya sake kira bata kusa, tasan shi da naci akan abu ta kuma tabbata magana zai mata akan wani abun tunda har ya sake kira. Kiran sa tayi tana fatan koma menene dai yasa ba babban abu bane, shigar sa kenan library yaji wayar sa da take a vibration na motsi, dubawa yayi yaga Auntyn ce, sai ya tashi ya fito daga ciki dan kar ya damu masu karatu ya sako kasan ya bi ta kofar baya zuwa wani dan karamin garden da yake cikin library din, ya zauna a cikin daya daga cikin kujerun wajen ya kira dan dama katse kiran nata yayi. Yana kira ta daga,

"Tariq?"

"Na'am, barka da safiya Aunty."

"Barka dai, ya karatu?"

"Alhamdulillah, ya karin hakuri?"

"Da godiya, alhamdulillah." Ta fada a sanyaye

"Na kira ranar nayi miki gaisuwa yarinyar nan ta daga."

"Jiddah, eh tafada min sai na manta ban kira ba."

"Mmm... Dama Aunty magana ce nake so muyi."

"Toh ina jinka.*

"Akan maganar abinda ya faru ne, da abinda su Mama suke cewa, kiyi hakuri pls."

"Ba komai ai Tariq, ba komai wallahi."

Shiru yayi kamar zai sake magana sai kuma yace

"Shikenan toh, sai anjima."

"Okh sai anjima."

A sanyaye ta rike wayar, a kasan ranta tana godiya wa Aallah da ya saka akwai mutanen da suka fahimce ta, suka fuskanci halin da take ciki. Mutanen kuma da suke da kusanci da Muhammad idan ka dauke mahaifiyar sa.

[03/10, 21:27] Mss Xoxo: ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

😄😄😄😄😄😄😄

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰

[05/10, 16:20] Billyn Abdul 2: *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*

*ZAFAFA BIYAR BACTH A*

1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)*

2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)*

3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*

1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)*

2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)*

_Duk biyar 1500_

*______________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_*

1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)*

2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)*

3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)*

4... _INAYAH_ *(Mamu gee)*

5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)*

_Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_

*YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:*

_ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR*

_BANK NAME:_ *ZENITH BANK*

_ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_*

_SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_

*_07040727902_*

_IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_

*_09134848107_*

*_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**

©®*_*_Hafsat Rano_*_*

Page (13)

***Wakar perfect wadda Ed Sheeran yayi wadda ake cewa I found a love, for me... ce take tashi a motar tasa a hankali wadda ta saukar masa da yanayin shauki, bi ya shiga yi a hankali tamkar dan shi da ita akayi wakar zuciyar sa fes har yaa isa gida. Yayi parking a tsanake yana cigaba da rera baitin

_ "Cause we were just kids when we fell in love, not knowing what is was,I will not give you up this time.... Darling just kiss slow, your heart is all I own,and in your eyes, you're holding mine... Baby...."_

Sakin murfin motar yayi ya rufe sanda sukayi ido hudu da Daddy yana tsaye yana jin shi yana rera waka, kunya ce ta kama shi, ya hau sosa keyar sa kafin yace

"Good morning Daddy.

"Morning Son, daga ina haka?"

"Nayi dropping Safee a school ne."

"You...?" Ya nuna shi da hannu

"Yaushe ka fara kai ta school ban da labari."

Dariya yayi yana cigaba da sosa keyar tasa, murmushi Daddy yayi amma yasan dole akwai abinda ya sakashi chanja mind dinsa haka,

"Ka kyauta sosai."

"Nagode Daddy."

Sai suka jera zuwa cikin gidan a tare tamkar wasu abokai.

***Tun daga ranar kullum shi yake kai Safeera school Malam Sa'idu ya dauko ta, kuma kullum sai ya labe yaga zuwan su Jiddah. Be taba bari sun ganshi ba, a hakan ya sha daukar ta a hoto dan a yanzu hotunan ta da yake dasu a wayar sa ba zasu kirgu ba, duk da yayi ma kansa alkawarin sai sun shiga ss3 sannan zai mata maganar a time din yana da yakinin zata karbe shi, hannu biyu su fara soyayyar su wadda ya tanadar mata da zazzafar soyayya. Duk sanda yake free idan a daidai lokacin short break dinsu ne sai ya siyo abubuwa ya kai ma Safeeran school yace ita da jiddah, duk da ko be fada ba ma taren zasu ci amma sai ya sake jaddadawa har Safeera ta fara suspecting dinsa, he care so much akan jiddah har ya fita ma, duk sanda suka zauna a gida sai yayi mata maganar Jidda, me tayi a school yau, me tace hirar su kenan duk sanda suka zauna ko zai koya mata assignment. Bangaren Jiddah kuwa sosai take picking karatun fiye da yadda kowa yayi tunani, duk da kusan kaso hamsin cikin dari Safeera ce dan kaf class din babu me kokarin Safeera shiyasa kawancen su ya taimakawa jidda sosai ta fanni daban -daban, hatta yanayin yadda take magana da yanayin shigar ta Safeera take kwaikwayo, shiyasa cikin kankanin lokaci ta washe a cikin class din har take iya tsayawa a tsakanin yan class din tana jin itama daidai take dasu. Abubuwa da yawa tare Mom din Safeera take siya musu na gyara da gayu,tun tana jin kunyar karba har ta dawo bata jin komai. Wani weekend tace ma aunty zata je gidan, bata hanata ba sai dai dole ta rakata har gidan ita da Usman, anan suka gaisa da Maman Safeera sannan ta bar Jiddan, suka ce zasu kawota. Murna wajen Safeera ba'a magana, da farko ganin irin gidan ya saka jikin jiddan sanyi amma kuma yanayin yadda aka karbeta ya saka ta sakin jiki dan hatta masu aikin gidan sun san labarin Jidda a bakin Safeera da Isma'il, ita kanta mom kamar zata goya ta dan murnar ganin ta, labari ya kare yau dai taga Jiddan da Safeera take bala'in so kuma kwarai ta yaba da nutsuwar ta shiyasa taji dadi da ya kasance irin kawayen da yarta take mu'amula dasu. Kamar wanda aka jeho haka Ya Isma'il ya shigo gidan,waya suke da Mom tace masa Jidda tazo ai ba shiri yayi sallama da su Farouk ya taho gida yana Allah Allah ya iso bata tafi ba. A dakin Safeera ya iske su, ya tsaya daga bakin kofa yana yin kasa da idanun sa sanda suka hada ido da Jidda a lokacin da take kyalkyala dariya, dariyar da ta saka bugun zuciyar sa tsaya chak na dan wasu dakiku.

"Ya Isma'il." Safeera tace tana mikewa daga kan gadon

"Look who's here."

"Jidda." Ya kira sunan ta kamar wani dolo

"Na'am, ina wuni?"

"Lafiya lou, ashe zaki zo da gaske."

"Umm.." Tace tana wasa da hannun ta, hannun ya kalla yaga yatsun ta zara-zara, juyawa yayi da sauri ya bar kofar, Safeera ta dawo ciki suka cigaba da hirar su, daga nan suka dauko books din Safeeran sukayi karatu, wajajen karfe biyar Mom tace Ismail suje su kai ta, kafin ma ta rufe baki ya mike cike da zumudi, kallon sa tayi, ya dauki car key din motar ta, ya ajiye nasa sannan yace

"Bari na jira su a mota." Yayi gaba yana kada key din motar, tashi Mom tayi taje dakin ta, ta hadowa jiddah sha tara ta arziki tun daga kan underwears zuwa turare da kayan kwalliya, sai atamfa da veil, sannan ta saka mata 5k a cikin envelope ta fito ta iske su a dakin Safeeran tace su taso, turo baki Safeera tayi cikin shagwaba ya hau bubbuga kafarta kamar zatayi kuka

"Dan Allah Mom ki bari sai anjima 😭."

"A ah kar dare yayi, ni nayi ma Maman ta alkawarin zaa kawota, gwara ido na ganin ido ko Jidda? Kar babanku ya dawo yayi fada."

"Eh." Jidda tace tana yafa dan madaidacin veil dinta

"Allah ni...." Ta cigaba da buga kafarta, dariya kawai Mom tayi ta mikawa jidda kayan ta russuna har kasa ta sa hannu ta karba tayi godiya

"Kuje yayanku yana mota yana jiranku, sai yaushe Jidda?"

"Wataran." Tace tana murmushi

"Kice ma ba zaki sake zuwa ba." Safeera ta fada tana hararar ta

"Sorry mana."

Tace tana kallon ta, shiru tayi dan taji haushin tafiyar da jiddan zatayi, ta bude wardrobe dinta ta dauko veil ta dora akan inner cap din dake kanta ta zura slippers suka fito hannun ta rike da ledar kayan da Mom ta bawa jiddan. Yana zaune a mota ya hango sun fito, ya cire lock din motar ya fita ya budewa Jidda baya ta side din driver, ita kuma Safeera ta shiga gaba, ta sama Mom ta hango duk abinda ya faru, ta girgiza kai kawai tayi murmushi dan dama tana suspecting Isma'il din son yarinyar yake, sai dai bata tabbatar ba sai yanzu da taga abinda ya faru, sakin curtains din tayi bayan sun fice daga gidan. A hankali sosai ya shiga driving din kamar baya tafiya ma, sanyi da wakar da ke tashi motar ta saka duk basu lura da yadda yake tukin ba, maimakon ya wuce gidan su Jiddan kai tsaye sai ya tsaya dasu sahaibco stores ya siya musu chocolates masu yawa da ice-cream sannan suka cigaba da tafiyar wahainiya har suka iso ba dan ya so ba, yayi parking suka fita tare da Safeera ta rakata har cikin gidan sannan ta dawo suka tafi gida.

***A harabar gidan sukayi kicibis da Mama, tana fitowa daga part din Yaya wanda tun sanda tazo gidan be fi sau biyu taga Maman a bangaren Yaya ba, kallon ta Maman take dan ta kwana biyu bata ganta ba, sai taga tayi shar da ita ta kara wayewa tamkar ba ita ba, durkusawa tayi a tsorace ta gaida Maman, ta amsa kamar taga kashi ta wuce ta bata sake ko kallon ta ba. Bata ji komai ba dan dama ba wai suna haduwa bane tunda ba zuwa wajen ta take ba, haka kuma ko a compound din gidan basu cika haduwa ba dan idan Mama na gida ko yaushe tana part dinta itama kuma Jiddan ba yawo take ba wajen Yaaya kawai take zuwa shima ta dayar hanyar take bi taje ta dawo. Ita har ga Allah tsoron Maman take dan ba karamin kwarjini take mata ba musamman da taga hatta Aunty ma shakkar ta take shiyasa ta shafawa kanta lafiya bata taba shiga part din ta ba ko da wasa duk nacin su Amira sun gaji sun hakura dan ita bata cika son shishigi a in da ba'a son ta ba. Rayuwar ta, ta chanja a dan lokacin nan babu abinda zata ce sai godiyar Allah dan ko a haka Allah ya barta ta gode dan bata yi tunani ko hasashen ta a irin wannan rayuwar ba, rayuwar ta ta baya ta tuna ta girgiza kanta ta furta alhamdulillah, daga haka ta wuce wajensu ta samu Aunty tana bude kayan da Mom din Safeera ta bata cike da yabawa dan ba karamin kaya tabata ba masu kyau kuma da tsada, ita kanta Auntyn tayi mamakin gidan su Safeeran dan yadda suke babu girman kai ba zaka taba zaton haka gidan su yake ba

"Bafa karamin kaya matar nan ta baki ba jidda, ko wannan atamfar Babba ce wallahi."

"Taki ce ai atamfar Aunty."

"Tawa?" Ta waro ido tana daga

"Eh cewa tayi na kawo miki."

"Kai, kai hadda ni kuma?"

"Eh."

"Kai amma naji kunya, Nagode zan kirata dama in sha Allah nayi mata godiya, hade kayan ki kai daki."

Toh tace ta tattare kayan ta kai daki sannan ta dawo suka zauna da Auntyn suka cigaba da hira. Daga nan ta kira musu Baffa suka gaisa sannan suka tashi don yin sallar magriba da aka soma kira a wasu masallatan.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull