Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 15
Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 15: Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 15. Wanka ya sake yi tare da shiryawa cikin wasu…
3,358 words
Wanka ya sake yi tare da shiryawa cikin wasu kananan kayan, sai dai a wannan karon ba ita ta fitar mashi da kayan ba, shi ya zo ya fitar da kansa, ita tun da ta kwanta ta kasa sake motsawa.
Bayan ya kammala shirinsa tsab, ya kariso gaban gadon, a hankali ya zauna kusa da ita tare da sanya hannunsa ya fara shafa gashin kanta, da yake kwanciyar da ta yi yasa ɗan kwalinta ya zame kasa, gashinta ya bayyana.
"Tashi muje na baki abinci ko matata?". A nutse ya yi maganar, har lokacin taki buɗe idanunta, dan bata san da wani ido zata kalle shi ba.
"Yaya Nawid naƙoshi". "Ban yarda ba, kiyi hakuri kin ji? Na san abin da nayi maki ne yasa kika ce haka, to na tuba bazan sake ba, yanzu dai yinwa nake ji, please ki tashi muci ko?".
Shiru ta ɗan yi Mashi kafin ta ce "Yaya Nawid da gaske ba zan iya ci ba, kai kaci kawai". Ɗan kwantowa kaɗan ya yi tare da ranƙwafo da kansa daidai saman tata, har suna iya jiyo numfashin juna. "Idan baki ci ba, wlh nima ba zan ci ba, dan Allah kiyi hakuri, na ce maki ba zan kara ba kin ji ko?". Ya kai karshen maganar yana mai gangaro da hannunsa zuwa saman wuyarta.
"To yaya Nawid ai kunyarka nake ji ne, ni gaskiya ba zan iya buɗe idanuna na kalleka ba" Murmushi ya yi tare da cewa "To tashi kizo, nayi alkawarin ba zan kalleki ba, zan rufe idanuna ko kuma na kawar da kaina a duk lokacin da na kawo maki spoon ɗin abincin bakinki". To ta amsa da shi tare da miƙewa zaune, shima miƙewa ya yi suka sauƙo daga saman gadon zuwa kasa.
Ita ta zuba masu abincin, sai kallonta yake yi, ya kasa cika alkawarin da ya ɗauka na ba zai kalleta ba, ita kuma taki yarda ta kalle shi.
Bayan ta gama zuba masu, sai ta zauna a gefensa kamar yadda suka saba zama.
Ɗaukar spoon ya yi tare da ɗebar abincin ya kai mata saitin bakinta yana mai tsareta da ido.
"Ni yaya Nawid zan ci da kaina". Ba musu ya juya abincin izuwa bakinsa, ɗaukar nata spoon ɗin ta yi suka fara ci a tare, abin gwanin ban sha'awa da burgewa.
Bayan sun kammalaci, ta miƙe ta kwashe kayan abincin zuwa Palo, lokacin da ta dawo, ta samu yana waya, shiru ta tsaya kusa da shi tana jin muryar macen da ke fitowa daga cikin wayar tasa, wani irin kululun bakin cikine ya turnuke mata maƙoshi, bata bari ya kammala wayar ba ta fusge tare da bin screen ɗin wayar da kallo.
Bata kai ga kallon sunan da ya rubuta ba, sai gani ta yi ya miƙe yana ƙoƙarin kwace wayar, da gudu ta nufi waje bata bari ya kwace wayar ba.
Ba ƙaramin daɗi ya ji ba, ta fara kishin shi, kenan ta fara son shi, dan shi idan baku manta ba, yana ganin kamar dole aka yi mata, kuma hakan ya sa ya zage yake koya mata son shi.
Da sauri ya bi bayanta, a palo ya sameta zaune kusa da Ummi, tamkar ba ita ce ta karɓe mashi waya yanzu ba, kai kallonsa ya yi izuwa kan hannayenta, babu wayar mamaki ne ya kama shi, ko'ina ta kai wayar oho.
"Zo mu tafi ina da magana dake". Ya faɗa yana satar kallon Ummi, make kafaɗa ta yi alamar ba zata zo ba, kashe mata ido ɗaya ya yi tare da ɗan karkata mata kai alamar ta yi hakuri ta zo suje.
Gyarawa ta yi ta kwantar da kanta a saman cinyar Ummi tana mai da kallonta izuwa saman Tv da Ummin ke kallo, ba zata zo ɗin ba kenan.
"To shikenan bani wayata fita dama zan yi, kiran da ki ka ga anyi mani nan, wata patient a ka kawo a asibiti, abin na gaggawa ne, kuma ni kaɗai ne zan iya dubata, dan haka zan je wata kila na dawo yau, wata kila sai safiyar gobe". Ya kai karshen maganar yana miƙa mata hannunsa akan ta bashi wayar.
Ɗan satar kallon Ummi ta yi kafin ta miƙe tsaye ta nufi hanyar ɗakin nasu ba tare da ta yi magana ba, murmushi ya saki while ita ma Ummi murmushin ta yi, tana faɗi a ranta cewa, ai ba zata sake shiga tsakaninsu ba, jiya haka suka yi mata, a kitchen suna aiki ya shigo wai zai taya su, A'AFIA na ɓare maggi zata saka a miya, da ya sanya hannu zai taya ta, sai ta ce "Ummi ki ce yaya Nawid ya bar mani kayana bana soz bai iya ba, baya ɓarewa dukka, yana barin sauran Maggi a ciki". Ita kuwa Ummi sai ta shiga, ta ce ya bar mata kayanta, ai kuwa kafin ta gama ɓare maggin nan ita da kanta ta ce "Yaya Nawid to ɗauka muyi bibbiyu". Daga nan Ummi ta fita harkarsu, bata shiga faɗarsu, yanzu ma da ta shiga ta ce A'AFIA bazata je ɗakin ba ko makamancin haka, ai da sun sake bata kunya, tun da ga shi dai ta miƙe ta wuce ɗakin dan kanta, so ba'a shiga tsakanin mata da miji, idan ma mace ta kawo maki kukanta akan mijinta, kiyi mata addu'a kawai ki bata hakuri, wlh idan kika kuskura kika tayata zaginsa da faɗar laifinsa, tofa zata iya biye maki a lokacin tun da sun yi faɗa da mijin, amma kuma da zarar sun shirya, ki tabbatar abin da kika faɗa na zaginsan nan tsab a kunnensa zata gaya Mashi, idan munafuka ce ma, wlh sai ta kara da karya, kuma zata yi ta riƙe ki a rai na kin zagi mijinta, haka dayawan mata suke, Allah dai yasa mu dace mu kuma gyara.
Bin bayanta ya yi, a tsakiyar gado ya iskota ta kwanta ruf da ciki tare da kifa kanta a kan pillow.
Saman gadon ya haye shi ma, a hankali ya sanya hannu ya ɗago kanta, Subhanallah zaro idanuwansa waje ya yi yana kallon yadda take hawaye sharɓa sharɓa.
"Aafia lafiya kike kuka? Me ya faru kuma?" Ya yi maganar fuskarsa ɗauke da damuwa tare da kulawa a gareta sosai.
Shiru ta yi mashi ba tare da ta yi magana ba. "Dan Allah matata ki gaya mini, shin nayi miki wani laifi ne?" Ya kai karshen maganar tare da ɗagota da kyau ya mannata da kirjinsa.
"Yaya Nawid kwana fa ka ce zaka je kayi a asibitin, kuma fa ai naji mace ce fa ta kira ka, daman kenan akwai number mata a wayarka?". Allah sarki da yake ta jima tana som shi, hakan yasa take bala'in kishin kayanta, shi kuma bai san hakan ba.
"Am so so sorryyyyyyyyyy Matata, na tuba, yanzu dai to tashi muje Asibitin tare domin ki ganewa idanunki, ayi komai a gabanki, mu je tare kuma mu dawo tare ko, amma ki yi shiru dan bana son kukanki". Cikin sauri ya ɗago tana kallon shi, jin ya ce zasu je hospital a tare, ba ƙaramin daɗi ta ji ba, ganin ta tsare shi da ido ne yasa ya jinjina mata kai alamar tabbatar mata da abin da ya ce.
Cikin sauri ta diro kasa saga saman, ta nufi waje tana murna, miƙewa shi kuma ya yi ya hau shirin zuwa hospital ɗin.
Tana fita ɗakin jelly ta wuce, har lokacin Ummi tana Palo tana kallonta. Hijabin jelly ta ɗauko tare da wasu kayan, doguwar riga abaya fara tas, da mayafinta, ta sanya rigar, ta ɗaura mayafin a matsayin ɗan kwali, ta ɗaura ɗan hijabin please call me ɗin a saman, shi ma hijabin fari ne tas, ta yi kyau sosai abinta.
Lokacin da ta dawo ɗakin shi ma ya kammala shi, hannunta ya riƙo a kan su tafi, karɓar jakar hannunsa ta yi tare da rataya shi a kafaɗarta, suka nufi waje.
A Palon suka tsaya suka yi wa Ummi sallama, addu'a ta yi masu tare da fatan nasara da kuma a dawo lafiya, sosai dai ta yi masu addu'a, sai Amin Amin suke amsawa da shi.
Suna fita harabar gidan ya ɗan rungumota a jikinsa, lokacin kuma karfe 6 daidai gari ya ɗan yi duhun mangariba.
Da kansa ya buɗe mata gidan gaba na motar ta shiga, bayan ya mai da marfin ya rufe, ya zagayo ta mazaunin driver, ya shiga ya zauna.
Zuba mata idanu ya yi ba tare da ya kunna motar ba, jin shiru bai tashi motar ba yasa ta ɗan ɗago dan ta saci kallonsa, karaf suka haɗa idanu, ƙasa ta yi da kai tana Murmushi.
"Me ya yasa ki murmushi?". Girgiza kai ta yi alamar babu komai. Matsowa kusa da ita ya yi tare da rankwafo da kansa sai tin tata. "Kin taɓa ganin anyi abu babu dalili ne?". Nan ma dai girgiza mashi kai ta yi alamar a'a.
"To menene dalilin?" Nisawa ta yi kafin ta ce "Saboda kayi kyau sosai ne yasa nake murmushi, amma kuma....." Sai ta yi shiru. "Amma kuma menene? Ki karisar da maganar mana?" "Amma kuma bana son wata ta ganka a haka, bana son taga kyan da kayi". "Kenan kishi kike yi?" Girgiza mashi kai ta yi alamar A'a.
"Menene wannan idan ba kishi ba?" "No yaya Nawid ba kishi bane, kawai ina kula da kai ne, wai ka manta amarka a ka bani ne?" Zaro ido ya yi yana kallon yadda take zaro magana kamar ba ita ba, eyee wato Amanar shi aka bata, kai jama'a, wasa wasa ita ma ta iya magana sosai.
"E kam gaskiya ne, tun da amana ta a ka baki, dole ki kula da ni sosai, yanzu dai bani sumbata sai mu tafi ko? Lokaci na kurewa". Kara faɗaɗa murmushinta tayi tare da matso da ɗan bakinta sai tin kumatunsa da nufin ta sumbace shi.
Sai da ya bari ta kawo bakinta, sai ya juyo da face nasa ta sumbace sa a saman lips nasa, tana ƙoƙarin zamewa ya riƙota tare da zura harshensa a cikin bakin nata, ya fara kissing nata.
Sun ɗan jima a haka kafin daga bisani ya saketa tare da kunna motar yana wani lumshe idanu, kumawa ta yi ta jingina da jikin kujerar motar, ita ma ta lumshe idanunta kamar mai barci, wani azababben son shi ne ke kara ninkuwa a cikin zuciyarta.
A hankali yake tukin, duk bayan minti sai ya juyo ya kalleta, har lokacin idanunta a lumshe. Kasancewar suna tuƙi a hankali sai ya sa basu isa Hospital ɗin da wuri ba.
Har suka isa kuma, ta ki yarda su haɗa ido, a tare suka fito suka jera zuwa ciki, sai janta da hira yake yi, tun bata biye mashi sosai, har ta fara biye mishi, dayawa daga cikin nurses ɗin sun yi zaton kanwasa ce, domin basu san ya yi aure ba, kuma akwai kama ta jini a kan fuskokinsu, idan baku manta ba, da Hjy Turai da Hjy Hadiza ƴa da kanwa ce, dole za'a samu kama ta jini.
Kai tsaye office nasa ya wuce. Bai kai ga shiga cikin office ɗin ba wasu nurse guda biyu suka nufo shi da sauri, basu bari sun gama karisowa ba suka fara gaya mashi halin da matar da zaayiwa aiki take ciki.
Dawo da kallonsa kan Aafia ya yi, cike da kauna ya ce "Ki shiga office ki jirani ko, Bahijja ki raka ta, ki zauna ki kula da ita, ke kuma Ameera muje zuwa ɗakin da aka kwantar da matar". Ya kai karshen maganar tare da wucewa gaba. Wadda aka kira da Ameera ta bi bayan shi, ita kuma Bahijja ta yi gaba tana faɗin "Ke muje ko?".
Binta da kallo Aafia ta yi kafin ta maido da kallonta izuwa kan mijin nata, bata kula Bahijja ba har sai da ya kurewa ganinta, sai binta da kallon banza da raini Bahijja take yi, dan bata taɓa tunanin Aafia matar Dr bane, tun da basu ji labarin auren nasa ba, abu ne da aka yi shi lokaci guda.
Sai bayan ya kurewa ganinta ne ta tura kofar office ɗin ta shige, bayanta Bahijja ta bi, ta je zata zauna a ainahin kujerar da yake zama, Bahijja ta daka mata tsawa akan wai ta dako kujerar da patient suke zama ta zauna, kujerar Dr iya shi kaɗai ne yake zama a kai.
Da yake Aafia ma yar yi ce, ko kallon in da take bata yi ba, domin Bahijja bata kai ta ɗaga idanu ta kalle ta ba, wucewa ta yi ta zauna a saman ainahin kujerar tasa.
"Ke baki da hankali ne? Ina matsayin P.A na oga zan yi maki magana ki ki kulani, kanki ɗaya kuwa? Na gaya maki ba wanda yake zama a kujerar Dr sai shi kaɗai, dan haka ki dawo wajen da patient ke zama ki zauna, idan ba haka ba ranki in ya yi dubu zai ɓaci yanzun nan". Har lokacin Aafia bata ɗago ta kalleta ba, sai ma ɗauko wayarta da ta yi tana latsawa.
Bahijja ta fusata iya fusata, tun da ta kalli Aafia dama ta ji ta tsaneta, bata sonta, tana tsoron ta ce zata yi mata wani abu kuma, ya zamana suna da kusanci sosai da Dr ya yi mata hukunci, hakan yasa ta zauna a patient chair tana cika tana batsewa, ba dan ta so ba ta hakura.
Ita kuwa Aafia ko a jininta, ranta fes, sai ma massage ta yi wa Nawid akan tana son shan black tea kafin ya shigo, yana ganin massage ɗin shi ma ya yi wa Bahijja massage a kan ta haɗawa matarsa Black tea ta bata kafin ya zo.
Ba ƙaramin razana ta yi ba lokacin data ga massage ɗin nasa, wai a haɗa wa matarsa tea, kenan Aafia matar sa ce? Ta tambayi kanta, "Kai ina ba matarsa bace, sai dai wadda yake son aura, tun da bamu ji ance ya yi aure ba" ta sake faɗa a cikin zuciyarta tare da miƙewa ta nufi wajen wani kyakkyawar show glass dake cikin office ɗin, kayan tea ne kala kala a ciki.
Ruwan zafi ta fara jonawa a hitter, kafin ta haɗa komai da zata buƙata a cikin cup mai shegen kyau.
Duk abin da take yi Aafia tana jinta, kawai ɗagowa ta kalleta ne tana ganin kamar bata kai wannan matsayi ba, ta fi karfi kula irinsu Bahijja, dama idan baku mance wace ce Aafia ba, kun san ta akwai ta da jiji da kai, abin da ya faru da ita ne ma yasa ta yi sanyi, ta dawo kamar ba ita ba.
Cikin girmamawa Bahijja ta miƙo mata cup ɗin tea ɗin bayan ta kammala haɗawa kenan, bata karɓa ba, sai ta nuna mata saman table ɗin a kan ta ajiye a wajen, hakan ma sai da ta ɗauki ƴan sakanni kafin ta nuna mata ɗin.
Haushi tamkar Bahijja ta yanka mata mari, wata ƴar siririya da ita kamar bulala ƴar yarinya da ita Dr ya kawota tana yi masu iskanci, cewar Bahijja a cikin zuciyarta.
Ba yadda zata yi, haka ta ajiye mata tare da komawa mazauninta, ta zauna tana mai huci, ko kala Aafia bata ce da ita ba.
Suna a haka har aka yi sallar mangariba da isha, a cikin office ɗin Aafia ta yi sallah kasan cewar akwai komai a ciki, ita kuma Bahijja nata office ɗin na P.A da yake kafin ka shigo cikin office ɗin Nawid ɗin, to a nan nata office ɗin yake, a nan ta je ta yi sallah ta dawo, domin Nawid ya ce ta kula mashi da mata sai ya gama aikinsa ya dawo sannan ta wuce, kada ta kuskura ko ƙuda ya taɓa mashi mata............... To fa🤔
Suna zaune shiru kamar kura me, Aafia ta jingina kai da jikin kujerar tare da lumshe idanu kamar mai barci, ita kuma Bahijja tana ta kare mata kallo, tana son taga dame Aafia ta fita ne?. Mata kenan matsalar mu kenan, kowa so take a ce tafi kowa, da zarar mata sun haɗu zasu fara kallon junansu dan suka da me wata tafi su, kowa da irin rayuwarsa, kowa da kalar baiwar da Allah ya yi Mashi, naki baiwar daban, ita ma tata daban, wata kilama baiwarki ta fi tata tsada, kowa da abin da yafi a halitta da kuma rayuwarsa, so bai kamata ki haɗa kanki da kowa ba, ki sanya a zuciyarki ke fa ta dabance, ke kaɗai ce babu irin ki, sai ki zauna lafiya, kada ki duba kowa, ki sanya kawai ko kin duba ba irinki bace, ki kasance mai duba rayuwarki kullun ba na wasu ba, hakan ne zai baki damar ki zauna lafiya cikin kwanciyar hankali, Allah yasa mu gyara.
Suna a haka har Dr ya shigo, jin shigowarsa yasa Bahijja ta ɗago kai tana bin shi da kallo, ita kuma Aafia bata motsa ba.
"Mrs Nawid kin yi barci ne?". Sai lokacin ta waro idanunta a kansa. Cool murmushi ya sakar mata "Am sorry na barki zaune ko? Amin afuwa ba zan kara ba, aikin ne ya bani wahala yau, yanzu dai muje gida ko? Dan naga har karfe 9 ta yi". Ya kai karshen maganar yana zame hand gloves da suke hannayensa.
"Yaya Nawid jikina ya mutu barci nake ji, ba zan iya tashi ba fa". Tayi maganar cikin sanyin murya.
Tamkar wasu Tv haka Bahijja ta mai da su, abin haushi kamar ta shaƙe Aafia har sai ta mutu sannan ta saketa take ji, shi kuwa tamkar bai ga Bahijja ɗin ba, ta matarsa kawai yake yi.
"To idan ma ba zaki iya tashi ba, ai ni zan iya ɗaukarki cak ko?". Yana magana yana nufar in da take. "Yaya Nawid ina da nauyi fa". Ƴar dariya ya yi kafin ya ce "A hakan? Yadda kike yar siririyar nan? To idan ma kina da nauyi, ni kuma ina da karfi" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e tana da nauyi duk da take ƴar siririyar.
"To bari na gwada maki ki gani ina da karfi". Hannu yasa yana ƙoƙarin ɗaukarta, cikin sauri ta ce "Wasa nake yi, zan iya tafiya". Girgiza kai ya yi yana faɗin "A'a ni ban yarda ba, dan haka kawai ɗaukarki zanyi gara ma ki tsaya". Yau Bahijja dai taga ikon Allah, tambayar kanta take yi, dama Dr haka yake? Dama yana dariya? Dama yana magana har haka? Wato sune dama yake ɗaurewa fuska kenan? Lallai yau taga abin mamaki.
Shi kuwa ɗaukarta ya yi kamar yadda ya faɗa suka nufi waje, daidai zai fita ya ce da Bahijja ta rufe mashi office da duk abin da ya dace shi ya wuce gida, daga haka ya fice da ita a kafaɗarsa. Da Ido kawai Bahijja ke binsu da shi har suka fita.
Tun da ya fito duk in da ya wuce nurses sai sun kalle shi sun sake waigawa, ba ƙaramin mamaki ya basu ba, sai tambayar kansu suke yi akan yaushe ya yi aure, dayawa daga cikinsu dai sun san bashi da kanwa, shi kaɗai ne wajen Umminsa, to a ina ya samo wannan yarinyar kuma?.
Shi kam bai bi ta kan kowa ba, kai tsaye motarsa ya wuce da ita, sai ɓoye fuska na rashin kunya take yi. A gidan gaba ya zaunar da ita, ya zagayo mazaunin driver ya shiga.
Kasancewar parking space ɗin akwai ɗan duhu, babu haske sosai, sai bai kunna hasken motar ba, ya lallaɓa a cikin duhu ya jawota jikinsa, sosai ya matseta tare da zura hannunsa ta samar wuyar rigarta zuwa ciki.
Bata hana shi ba, kuma bata tashi daga jikin nasa ba, breast nata ya kama ya fara shafasu a hankali yana wasa da su, hannayenta tasa dukka biyu ta rungumo shi, hakan ba ƙaramin daɗi ya yi mashi ba, yanzu ta yi accepted na shi kenan, nan take ya fara wasa da ita sosai son ranshi, bata hana shi ba kuma bata taya shi ba, ta yi shiru tana sauraronsa.
Har sai da agogon hannunsa ta buga masu karfe 10 ya yi, sannan ya saketa yana mai da numfashi tare da lumshe idanu, ita ma sauke numfashi take yi a hankali hankali, alamar ta karɓi saƙon nasa.
Sun ɗauki ƴan mintoci a haka, wadda a kalla zasu kai 10mins. Da kyar ya iya jan motar suka nufi gida.