Kenza eBookz

Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 28

Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 28

Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 28: Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 28. Shi me fitowa ya yi tare da nufar wajen pool…

3,338 words

Shi me fitowa ya yi tare da nufar wajen pool ɗin dan ya hango Areef a wajen, ita kuma cikin gida ta nufa, dan ta je wajen Imran duk da cewa ba wani shiri sosai suke yi da jelly ba, jelly na kishi da ita, da farko suna zaman lafiya, daga baya da ta fahimci Imran yana bawa Rimshan kulawa sosai, duk wani motsi idan ta yi sai ya tambayeta me take so, tun daga nan jelly ɗin ta fara kishi da ita, ta ja baya da ita sosai, idan ma Rimshar na yi mata magana bata cika wani amsawa ba, sai tayi kamar bata ji ba, hakan yasa Rimshar bata cika shiga harkan ta ba, bata son ma su haɗu sai idan ya zama dole, dan ba zata iya masifar jelly ba, kuma koba komai jelly ta girmeta, ta bata a kallah shekaru 2, sa'ar jehan ce ita, shiyasa bata biye mata, kuma ita Rimsha dama bata iya faɗa ba, bata iya masifa ba, ita dai a barta da soyayya kawai, shi ta fi iyawa, shima ɗin Akila ke kara koya mata.

ASEEF

Da sauri ya karisa ya rungumi ɗan uwan nasa yana faɗin ya yi kewarsa, ture shi Areef ɗin ya yi yana faɗin "Sai yanzu ne kayi kewa na ɗin ko? Tun ɗazun baka yi ba wato? Tukun nan ma ina ka je? Ina ne mai mahimmancin da ya fi maka zama tare da mu a ranar da kazo, bayan kasan muna kawarka sosai? Koma inane ba zaka iya hakura sai gobe ba ko? To yau munyi hannun riga". Ya kai karshen maganar yana mai da kallonsa a kan wayarsa da yake latsawa.

Shiru Aseef ɗin ya ɗan yi, yana tunanin abin da zai gaya mishi da zata sanya shi dariya, yasan bai kyauta ba, yasan suna kewarsa sosai da sosai, amma haka ya tsallakesu ya tafi wajen Akila, ya kasa hakura sai gobe ya je ya ganta, kuma da ya je ya kasa barin wajen nata da wuri, da farko ya yi niyar idan ya je ba zai wuce ya yi minti 30 ba ya dawo, sai kuma gobe ya je su ga juna da kyau, amma ya je ya yi almost 2 hours a wajen nata, sam ba haka ya so ba, yanzu haka yasan Lion ma bai ji daɗi ba, dan yasan shi ne bugun zuciyarsu, kuma farincikinsu.

"Wlh Areef she is gorgeous". Ya faɗa yana murmushi tare da goya hannayensa a saman kirjinsa.

Da sauri Areef ɗin ya miƙe yana faɗin "Who is she please?". Wani kallon gefen ido ya wurga mishi dama yasan idan ya kawo wannan zance ɗan uwan nasa zai sauƙo. "Wlh she is gorgeous". Ya sake maimaita maganar ta ɗazun.

Cikin zumuɗi ya sake tambayarsa wace ce kyakkyawar, kuma a ina take, son ta yake yi ne ko ya ya. Kara faɗaɗa murmushin nasa ya yi kafin ya sake cewa "Wlh she is gorgeous".

Ɗaure fuska sosai Areef ya yi dan ya fahimci iskanci sabo Aseef yake ji da shi, zai wani tsaya yana gaya mashi she is gorgeous, to waye gorgeous ɗin an tambaye shi yana ta kara maimaita magana ɗaya, ga shi shi kuma a ƙage yake da ya ji wace ce wannan da Aseef yake yabonta haka.

"Aseef ban son iskanci fa, i said who is she ko? Tun ɗazun sai maimaita magana ɗaya kake yi, she is gorgeous, she is gorgeous, to na gaji da jin hakan". Cigaba da murmushinsa ya yi yana faɗin "Wlh she is gorgeous". Areef ya zo har wuya, a fusace ya ɗaga hannu zai kai mashi duka, kaucewa ya yi yana faɗin "Haba mana, kai fa mugu ne, na ce maka wlh she is gorgeous, my cow da na saya jiya a Washington DC mana, wadda Saif ya ce kada a kawo mashi gida, kada na kuskura na zo da ita kasarnan, to ita ce kyakkyawar".

Wani irin harzuƙa Areef ya yi, a guje ya raka shi dan ba zai kyale shi ba, shima da gudu ya wuce zuwa cikin gida, kai tsaye sai bedroom na Lion.

Yana zuwa ya faɗa saman bed yana dariya har da riƙe ciki, idan ya tuna yadda Areef ya ɗaure fuska dan ya ji shanuwa ce kyakkyawar ba abin da yake zata ba, sai ya kara tuntsurewa da dariya.

Saif yana zaune a gefen bed ɗin, jikinsa na sanye da farar jellabiya, ya ɗaure gashin kan nan nasa, fuska dai kamar kullum, a fusace, a ɗaure tamau, tamkar hadari, yau dai rubutu yake yi a cikin wani takarda mai girman gaske, mai kama da diary, sai tashin fitinannen daddaɗar kamshi perfume ɗin nan nasa yake yi, ko kallon in da Aseef ɗin yake bai yi ba.

Shi ma Areef yana shigo kan gadon ya faɗa yana faɗin, "Allah ka tashi muje ka fara frog jump dan ba zan kyaleka ba". "Ni ban iya frog jump ba, amma tun da Lion ya iya zai karɓa mini tun da ni pleasure'nsa ne, ba zai bari na sha wahala ba". Yana magana yana turo baki, jan gashinsa da karfi Areef ɗin ya yi kamar yadda Lion yake yi mishi shima.

A shagwaɓe ya sa ihu yana turo baki tare da kumbura kumatu, ko sannu Lion bai ce musu ba, ganin bai kula su ba yasa Areef hakan bata yi mishi ba, dan ya fi son yaga yana takurawa Lion ɗin sosai, yana sanya shi yin magana. Sakin Aseef ɗin ya yi, ya koma kusa da Lion ɗin dan ya saka shi magana, shi baya son ya ga ɗan uwan nasa yana zaune shiru, ya fi son yaga yana sanya shi magana ko ba yawa.

"Lion wai ya batun bed guda ukun nan ne? Ka sanya a zo a zuba mana su a nan mana, dare fa yana yi". Ko sannu bai ce mishi ba, dan wlh ba zasu zauna mishi a ɗaki ba, yanzu ma ya yake karewa da su bare kuma a ce sun dawo ɗakin, ai hawan jini zasu saka mishi, yasan ko zai mutu sai sunyi ta saka shi magana.

Shima Aseef miƙewa ya yi ya dawo ɗayan gefen ɗan uwan nasa, suka saka shi a tsakiya kamar masu shirin bashi shawara mai mahimmanci, har lokacin bai ɗago ya kallesu ba, Allah ne kaɗai yasan abin da yake tunani da kuma abin da yake cikin zuciyarsa, duk yadda suke da saboda da Lion ba zaka taɓa gane ina ya dasa ba, ba zai taɓa baka wani sign da zai nuna maka alamar in ya dosa ba, sai dai kai kayi ta hasashe dan kanka, harta su dad nasa hasashensa kawai suke yi a kansa, ɗan gara ma Triplets ɗin nasa, suna iya cankan abu daidai a kansa, yanzu haka sai Allah kaɗai yasan me yake rubutawa, ko sun duba ma, ba zasu gane kan zancen ba, tun da ba littafi ne karami ba, shiyasa basu sha wahalar duba abin da yake rubutawa ɗin ba, ga shi da shegen good handwriting kamar computer, ga bala'in iya rubutu da sauri, kafin su karanta layi ɗaya, ya sake rubuta wani layi ɗayan ya wuce wajen.

A ɓangaren Rimsha kuwa, kofar ɗakin Imran ta nufa, da sallama ɗauke a bakinta ta tsaya a bakin kofar tana jiran izinin shigowa, daga ta cikin ɗakin jelly ta amsa mata da "To ƴar anace, yaya Imran yana wanka, idan kina son yin magana da shi, sai ki jira shi a waje ai". Ta kai karshen maganar tana jan tsaki.

Har cikin zuciyarta maganar ta yi mata zafi, kuma hakan ma kaɗan ne daga maganganun da jelly ɗin ke gaya mata, yanzu ma da tasan baya cikin ɗakin ba zata je wajen ba, dan tana jin zafin maganganun jelly sosai, kuma kunsan halin jelly, number 1 ce a rashin kunya.

Rai a ɓace ta juya ta koma cikin ɗakinta, tason ta yi magana da Imran akan zuwa gyaran gashin nan nata, dan kan nata na damunta, ta kuduri niyar ba zata sake zuwa wajen Imran neman wani abin ba, dan tana zargin da gangan ɗazun jelly ta ce mishi lallai su je gidan Abbi, dan kawai ta ji yace zai kai Rimshar gyaran gashi, shi ne ta bijiro da nata dan kada a kai Rimshar, ta yanke wa kanta hukunci zata rinƙa fita da kanta ta je tunda yanzu ta yi free, zata tambayi Akila sunan anguwar da ake gyaran gashin dan ta rinƙa kai kanta da kanta kawai zai fi mata.

Tana shiga bedroom nata zuciya cike fal da tunani, toilet ta wuce dan ta yi wanka, bayan ta kammala ta shirya cikin ɗaya daga cikin ɗinkunan da Imran ya yi musu, dogowar riga ce ɗinki ya zauna mata sosai a jikinta, fesa perfume nata ta yi tare da ɗaukar wayarta ta nufi garden na gidan.

Tana zama cikinta ya fara kukan yunwa, shiru tayi tana sauraron yadda cikin nata ke ƙu,lu,lu,lu, wato kuman yunwar kenan, tunani take yi a irin rayuwar da zata shiga yanzu kuma, ji take yi tamkar ta roƙi Areef yasa a mayar da ita kusa da daddynta, ko kuma ta koma gidan Akil, wani ɓangare na zuciyarta ne ya bata amsa da ita ma Umaisha kishi take yi da ke ai, tamkar zata yi kuka tuna hakan da ta yi, a kule ta ce wai me yake faruwa da ita ne? Ko wace mace sai ta ce tana kishi da ita, to ita tace tana son mazansu ne? Abin gwanin ban tausayi, can wani ɓangare na zuciyarta ya tuna mata to ko dai ta koma gidan Abbi ne?, Nan ma ɗayar ɓangare na zuciyar tane ya bata amsa da anya zata iya yin nisa da Saif kuwa? Anya zata iya jure wuni guda ba tare da ta ganshi ba kuwa? Anya hakan zai yiwu kuwa? Bama Saif ba, shima Areef anya zata iya rabuwa da shi kuwa?, Tuna hakan yasa ta fara ruwan hawaye, ga yunwa, ba wadda zata iya gayawa tana ji, yaya Imran ne kawai, shi kuma yanzu jelly ta yi musu tsakani.

Tana cikin wannan hali sai ga jelly da Imran sun nufo garden ɗin, sunci kwalliya, Imran na sanye da kananan kaya, wato wandon jeans baka da t-shirt blue, ita kuma jelly riga da skit ne a jikin nata, skit ɗin ruwan kasa da ratsin fari, riga fari, kayan sun ɗan kamata, amma ba sosai ba, ba karya sun yi kyau sosai, yau Imran ya sanyata dole sai ta saka ɗankwali a kanta, hakan yasa bata ji daɗi ba, sai turo baki take yi, ita a dole ta ji haushi.

Ganin su yasa ta yi saurin goge hawayen fuskarta tare da ƙaƙalo murmushi dole dan kada Imran ya gane komai, tasan yana yi mata iya iyawarsa, baya bari ta shiga kunci, yanzu ma duk abin da yake faruwa tsakaninta da jelly bai da masaniya a kai, idan ya sani zai ɗauki mataki, ba zai bari hakan ta cigaba da faruwa ba, idan baku manta ba, kunsan jelly da iya makirci da kirsa, to bata yi wa Rimsha abu a in da ta san Imran ɗin zai gani ko kuma ya ji, sai ta faki idonsa take tsula tsiyarta, ɗazun ma da yake toilet ta yi wa Rimsha wannan maganar, ta san cewa ruwa na zuba, karar ruwan ba zai bari ya ji maganar ba, shiyasa ta yi.

Ganinta a garden ɗin yasa shi sakin kayatatcen murmushi yana faɗin "Rimsha yaushe kuka dawo?" "Yaya Imran yanzu ba jimawa muka dawo". Kusa da ita ya zo ya zauna "Ai mun dawo daga gidan Abbi na tambayi Areef ina kike, sai ya ce mini kun fita ke da Aseef, fatan dai kun dawo lafiya?" Jinjina mishi kai ta yi tana faɗin "Lafiya lou Alhadulillah".

"Kina jin yunwa ko?" Ɗan satar kallon Jellyn ta yi kafin ta gyaɗa mishi kai alamar e "Am so so sorryyyyyyyyyy, gaskiya rayuwar gidan nan akwai wahala a gareki, ke baki iya cin abincinsu ba, su kuma basu son warin naki, ni kinga na iya cin abincinsu dan a kasarsu nayi karatu, amma ba komai ai kwanaki kaɗan ya rage mana a nan ɗin, zaki jure ko?" Gyaɗa mishi kai ta yi alamar e.

"Good to tashi ki ɗauko mayafinki mu je gidan Akil a tare, tun da dai ke kince baki son abincin restaurant, ai aiki ya gammu da yawon zuwa gidan Akil ko gidan Abbi ɗaukar abinci". Ɗan motsa lallausan lips nata ta yi tamkar wadda take son yin murmushin, nan take dimple nata dukka biyu suka lotsa, wani irin fitinannen kyau na ɗaukar hankali ta kara, tana ƙoƙarin mikewa ta nufi cikin gida dan ɗauko mayafin nata, sai ga Aseef da Areef sun jero tamkar wasu taurari, sai walwali suke yi, Lion ya gaji da surutunsu ya haɗasu da Allah su fita mishi a ɗaki, sanin girman Allah yasa suka hakura suka kyale shi ya sha iska, ba dan haka ba, yau ba zasu rabu da shi ba.

Har wani daddaɗar nauyayyar ajiyar zuciya ta sauƙe ganinsu, ta rasa me yasa take jin tsantsar farinciki idan ta gansu, ta rasa me yasa take jin duk wani damuwarta ya gudu da zarar ta yi tozali da kyawawan fuskokinsu masu ɗauke da annuri ta murmushi. A ɓangaren shima Areef, ganin ta a wajen yasa ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya da ta sanya Aseef juyowa yana kallon shi.

Gefenta ya je ya zauna shi kuma Aseef ya zauna a wani kujera na daban, ita kuma jelly tana ta faman kumbura kuma tu, ita a dole ta ji haushin kula Rimsha da Imran ya yi.

"Our Queen me yake damunki? Waye ya taɓa mana ke?". Cewar Areef, da kallo ɗaya ya yi mata abinku da jami'i, tuni ya fahimci akwai abin da yake damunta.

Ɗan zaro idanu Imran ya yi yana kallonta, har lokacin kuma shi dai bai ga alamar wata damuwa a face nata ba, shi ma Aseef da kallo ɗaya ya yi mata ya ga damuwa kwance a cikin idanunta, da yake idan baku manta ba, Triplets akwai baiwa, akwai kwakwalwa, sun gaji brain wajen Dr William jacop.

"Yaya Areef babu abin da yake damuna fa". Ta yi maganar tana kara ƙaƙalo murmushi a kan fuskar tata, dan ta tabbatar musu da babu komai ɗin.

Kallon Areef Aseef ya yi while shima Areef ɗin shi yake kallo, daga bisani suka juya suka kalli Imran wadda shima ya tsaresu da ido sosai, yana kallonsu, yana son sanin me yake damun kanwar tasa.

"Yaya Imran mu tafi ɗaki barci nake ji" muryar Jelly ce ta katse musu shirun da suka yi suna tunani, kallonta gabaɗayansu suka except Areef, shi dawo da kallonsa a kan Rimsha ya yi, a nan ne kuma ya fahimci jelly ce matsalar gimbiyar tasu, domin kuwa wannan magana da jelly ta yi, ta sake jefa fuskar Rimsha cikin damuwa da tunani, fahimtar hakan yasa ya ɗan yi shiru yana tunani mafita, tabbatas ba zai taɓa yarda da duk wani abin da zai sanya Rimsha cikin ɓacin rai ba, zai yarda da komai a gidan amma ban da hakan.

"Rimsha me zaki ci in sayo Miki". Cewar Imran, ya yi maganar ba tare da ya tanka maganar jelly da ta faɗa na su tafi ɗaki ba, sai dai bai gama rufe baki ba jelly ta kuma katse shi da su tashi su tafi ɗaki, ta yi hakan ne kuma dan kada Imran ya sahowa Rimsha abinci ko ya ɗauketa su fito, kishi kumallon mata, ko wace mace tana da shi, sai dai na wata ya fi na wata, ayi wa Jelly uzuri, ta ga hankalin yaya Imran ɗin ta na ƙoƙarin rabuwa biyu ne, ta ga yafi kula da Rimsha sama da ita da take matarsa, kuma take gani ita ta kasance kanwarsa, Rimsha kuma babu abin da ya haɗa su tun da bata ma san waye bappan nasu Hosain ba.

"Jelly ki bari bari na je ya sayowa Rimsha abinci ko na ɗauko mata a gidan Akil, ki je ɗakin ki kwanta ina zuwa". Babu kunya bare tsoron Allah ta sa mishi kuka wai cikinta na ciwo, shi dai Areef binsu kawai yake da ido yana karantarsu, shi kuma Aseef ganin tana kuka yasa ya tambayi Imran ɗin menene matsalar, Shi Areef duk da baya jin Hausa, zama yau da gobe da su, yasa idan suka yi magana yana fahimtar in da maganar ta dosa, sannan kuma yana karantar yanayinsu, ta hakan yake gane a kan me suke maganar.

Kanta Imran ya yi yana tambayarta ko lafiya, kuka take yi tsakaninta da Allah, hawaye wani na bin wani ta dafe cikin nata.

A hankali Rimsha ta faki idanunsu ta miƙe tana son barin wajen dan kada zuciya ya ɗebeta ta kifawa jelly mari, dan kayan haushin jelly ya isheta, sanin halinta da zuciya yasa bata son haɗuwa da Jelly'n, dan bata son suyi faɗa a matsayinsu na ƴan uwan juna.

Sosai Areef ya ji babu daɗin hakan, dan yasan Rimsha bata da wanda yafi Imran, shine farincikinta a yanzu, amma wata tazo tana kutse a tsakaninsu. Tana miƙewa ya riƙo hannunta, da sauri ta juyo duk da ta san shi ɗin ne, girgiza mata kai ya yi alamar a'a ta dawo ta zauna, ba musu ta koma ta zauna, shi kuma Imran ya ɗauki jelly a kan zai kaita ɗaki ya rarrasheta ya dawo.

Suna barin wajen Rimsha ta fara hawaye, tana mamakin jelly yarinya yar karama da ita ko a ina ta koyi wannan banza hali na kirsa da makirci oho, ɗan riƙota a gefen kirjinsa ya yi, yana goge mata hawaye tare da bata baki, da mamaki cike fal ransa Aseef ya miƙe ya dawo kusa da su dan ya ji wai shin menene matsalar.

Ɗan langwaɓar da kanta a gefen kirjin nasa ta yi tana mai jin bakin ciki a cikin zuciyarta, zama a gefenta a in da Imran ya tashi Aseef ya yi, fuskarsa ɗauke da damuwa ya fara tambayar me yake faruwa, ba ɓoye ɓoye Areef ya sanar da shi duk abin da ya fahimta, cikin sauri ta ɗago kanta daga gefen kirjin nasa, tana kallon face nasa, mamaki take yi waye ya gaya mishi abin da yake damunta, kashe mata ido ɗaya ya yi yana faɗin "Kina mamaki ne? Ina kaunarki ai, dole na iya gane me yake damunki, kuma duk da bana jin yarenku, ina fahimtar akan me kuke tattaunawa, yanzu dai jeki ɗauko mayafinki muje wajen cin abincin, Aseef zai ja mota, Lion ba zai hanani fita ba, dama abin da yasa yake hana fita, dan ni kaɗai ne, kada na fita wani abin ya same ni, ko kuma na fama ciwona, yanzu Aseef yana nan, babu abin da zai faru In Sha Allah, kuma daga yau kada ki sake tambayar Prof wani abu, duk abin da kikeso, Aseef yana nan idan ni ba na kusa, kin ji ko?".

Gyaɗa mishi kai ta yi alamar e ta ji. "Yanzu nauyinki a kan mu yake, dole mu kula dake tamkar yadda zamu kula da kanmu, Aseef ɗauko makullin mota ka sanar da Lion zamu je restaurant, ke kuma jeki ɗauko mayafi". Kusan a tare suka miƙe Ita da Aseef ɗin, hannunta ya riƙo suka nufi cikin gida yana tambayarta shekarunta, 14 years 3 months ta bashi amsa, sai mamaki yake yi, ƴar karama da ita, lallai akwai kura.

A palon sama suka rabu, ita ta shiga ɗakinta, shi kuma ya shiga ɗakin Lion. Jim kaɗan suka fito kusan tare, sake riƙe hannunta ya yi a cikin nasa yana faɗin "Wannan abin da kuke rufe jikinku da shi, ba karamin kyau yake yi muku ba". Sai murmushi take yi ba tare da ta yi magana ba suka nufi waje.

A yadda suka bar Areef haka suka dawo suka same shi, yana ganinsu ya miƙe a kan su tafi, fitowa balcony ɗakinsa Lion ya yi dan yaga tafiyarsu, yana ji da ƴan uwan nan nasa over, har ga Allah bai so Areef ya fara fita yanzu ba, saboda jikin nasa da saura, amma shi kuma yana bala'in son yaga ya fita, ya son ganin cikin Naijan nan ya take, Hakan yasa Lion ɗin ya hakura kawai ya kyale shi su fita.

Readers Also Read