Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 35
Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 35: Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 35. Ko sannu bai ce da Areef ɗin ba ya wuce ya…
3,332 words
Ko sannu bai ce da Areef ɗin ba ya wuce ya fice abinsa, mamaki Areef yake yi, wai me haɗin breast ɗin Rimsha da Lion ne, duk idan zasu yi karo to fa breast ɗin nan nata ne a gaba, sai ya kallesu, wannan wace iriyar kaddara ce? Ya tambayi kansa, suku nasu kaddarar a haka tazo kenan?. Juyawa shima ya yi ya fita, a harabar gidan ya isko Lion ɗin da Mark zasu fita, ga hadari na tasowa, alamar ruwan sama za'ayi, har walkiya ta fara wanzuwa a sararin samaniya, garden ya koma abinsa, shi kuma Lion ya wuce suka fita da Mark, Aseef kuma yana ta shararra barci bawan Allah.
A ɓangaren gidan Hajiyar daɗi kuwa.......
❤️❤️TRIPLETS❤️❤️
E27-28
"Ina muka nufa Areef?" Cewar Aseef, kallon Rimsha dake ta faman kallon titi ya yi, "Sister ina zamu fara zuwa? Super market ko kuma restaurant?". Jin voice ɗinsa sai da ya sanya gabanta ya yi wani mummunar faɗuwa. "Restaurant" ta bashi amsa tana kallon hanya. "On Monday zaki fara zuwa school ko?" Gyaɗa mishi kai ta yi alamar eh, dogon hancinta ya yana faɗin "To kin dai shirya ko?" E ta bashi amsa, shi kam Aseef sai tuki yake yi yana latsa waya, ga shi sai zabga uban gudu yake yi kamar babu gobe, ɗan uwan nasa kuma bai wani damu da ya hana shi taɓa waya yana tuki ba, ya mance cewa nan fa ba Washington DC bane, a Washington DC ne idan aka ga motocin gidansu sun hau hanya, abubuwan hawa ke kaucewa su basu hanya, shiyasa suke yin duk irin tukin gangancin da suke so a kan hanya, dan babu wani abin hawa da zai keta da gabansu, a nan Nigeria kuwa, basu san gidan jajayen wuya suka zo ba, yo ko doka ce a ka kafa ƴan Nigeria irin haka, ai sai sunci uwar dokar sun kora da ruwan mai sanyi daga fridge, koma uban waye yazo wucewa a kan titi ƴan Naija babu ruwansu wucewa zasu yi, idan ya ga dama ya wuce ko ya tsaya matsalar sa ce, su dai sun rigada sun wuce.
Restaurant da suka je jiya, shi yauma suka je, yau dai a nan suka ci abincin, sai kallonsu jama'a suke yi, sun ga masu jajayen kunnuwa, fararen tattabaru, kyawawan gaske, kamar dai ko yaushe sai aikin latsa waya yake yi, yana makale da Heartbeat nasa suna hira, ya hanata ko motsawa, Rimsha da Areef sai zuba hira suma suke yi, cikin natsuwa suka ci abinci, sai dai Aseef bai ci ba, ya ce ba zai iya ba, Areef ne kaɗai ya tayata ci.
Bayan sun kammala Areef ya biya kuɗin suka fito daga wajen suka nufi super market, suna tafiya suna hira, sai bata labarin Washington DC Areef yake yi, tana ta murmushi. Tasha ruwan mamaki lokacin da suka je super market ɗin nan, kayayyakin da take mutuwar so Areef ya rinƙa zaɓa mata, sai tunani take yi a kan waye ya gaya mishi abin da take so kenan, har da takalma high heels irin wanda take so ya kwasa mata, ta sha sayayya iya sayayya ba karya, a nan ne Aseef yake gaya mata ai shi ma ya saya mata kaya, har da abin wuya irin nasu da ya ce zai sa a buga mata, to ya bugo ya zo mata da shi, yana cikin wannan akwaitin da ya ce ta ɗauka jiya bata ɗauka ba, ba ƙaramin daɗi ta ji ba, cike da murna ta ce su koma gida, dan ta je ta kalli kayan, to suka amsa mata tare da nufar wajen biyan kuɗi.
Areef ne ya biya, ma'aikatan wajen suka ɗauka masu kayan zuwa wajen motarsu, a gidan baya suka sanya kayan, kamar yadda suka zo, ita da Areef a kujerar gaba, shi kuma Aseef driver, haka suka sake shiga suka nufi gida, sun manta da batun gyaran gashi.
Suna tsaka da tafiya a hanya daddy ya kira number Aseef, ya sha ruwan mamakin ganin call ɗin daddy da safiyar nan, yana can yana tunanin ko lafiya daddy ya kira shi, sai da wayar ta kutsa matsewa, ya yi maza ya ɗauka tare da sanyata a hand-free dan yana tuƙi. "Hello daddy good morning?".
Wani irin mahaukacin tsawa ya daka mishi wadda ya sanya shi taka birki a tsakiyar titi, saura kaɗan motar dake biye da su a bayansu ta dake su, sai Allah yasa ta kauce, daga Rimsha har Areef sai da kansu ya bugu da jikin glass ɗin motar, saboda irin birkin da ya ja babu excuse.
"Michael wace ce ta ɗauki wayar Romeo yanzun da na kira shi?! Na sake ina kiran shi baya ɗagawa, shin a ina ma kuke tukunnan?!!". A razane ya ɗago yana kallonta, dan yasan ita ce ba makawa, daddynsu bai taɓa yi musu magana cikin irin wannan matsanancin siga mai cike da tashin hankali ba, to menene matsalar?.
Nan take shi ma tsantsar bala'in ɓacin rai ya bayyana a saman fuskarsa, tabbas yasan yau ba ƙaramin yaki za'a sha ba a Washington DC, dan kuwa idan daddy ya san suna Nigeria akwai bala'i ba kaɗan ba, sun ce mishi suna Spain ne wajen James, ba zai taɓa yarda su yi nisa har Nigeria ba, fatansu dai Allah yasa kada ciwonsa ya tashi, shi kansa Areef yau idan ransa ya yi dubu to ta ɓata mishi, ina ga kuma Romeo? Shi da ta ɗaga kiran na shi, Aseef jikinsa har rawa yake yi saboda tsantsar ɓacin rai, ji yake yi yau idan bai ɓalla yarinyar nan ba, ba zai sami kwanciyar hankali ba, yarinya bata ji sam, me ya kai ki taɓa waya ke da akace ki karɓo kuɗi?.
"Daddy am coming". Yana kai karshen maganar ba tare da ya jira me daddy zai ce ba ya yi diff ya katse kiran, a fusace ya juyo da kallonsa kanta, cikin ɓacin rai da kakkausar murya ya fara magana "Me yasa kika taɓa wayar Lion? Kin san abin da zaki jawo mana kuwa?!". Ɗaga mishi hannu Areef ya yi alamar ya yi shiru, ba musu ya yi shirun, da hannu ya sake nuna mishi hanya a kan su tafi sun tsaya a kan hanya, kunna motar ya yi zuciyarsa na tafasa, bawan Allah baya son ɓacin rai sam, amma yau sai da Rimsha ta ɓata mishi rai, shi ma Areef dannewa kawai ya yi dan ko sun ce dukanta zasu yi ma, a cewarsa me zai daka a jikinta, abu kamar ka lometa ka kora ruwa.
Tsantsar bakin ciki ya hana Areef magana, dama kunsan ance mai hakuri, shiru shiru, mai fara'a, bai iya shiga ɓacin rai ba, idan ransa ya ɓaci sai ya jijjiga kowa dake kusa da shi, hakan yasa ya daure ya yi shiru yana karanta
لَا إلَهَ إلَّا اللهُ وحْدَهُ لَا شَرِيكَ لهُ، لهُ المُلْكُ ولهُ الحَمْدُ، وهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيْرٌ. [عشر مرات](١)أو [مرة واحدة](٢).
Dan ya sami zuciyarsa ta yi sanyi cikin ƙanƙanin lokaci, idan ba haka ba, zai iya yi wa Rimsha mari ɗaya ba tashi, dan kule shi, fitinarta ya yi yawa.
Shiru suka yi babu wanda ya sake ce da wani ko uppan, haka har suka isa gida, suna parking na motar ta fito ta nufi cikin gida dan ta je ta yi wanka ta cire kayan jikin nan nata, ice cream ya ɗan zuba mata a kan kayan, har ta kai kofar shiga Palo, sai kuma ta juyo da sauri ta dawo, Areef yana tsaye ya ɗan jingina da jikin motar yana binta da kallo, shi kuma Aseef ya zagaya ta wajen pool a in da yake zaton zai sami Lion a wajen, gaban Areef ta dawo, cikin sanyin murya ta fara magana "Yaya Areef dan Allah kayi hakuri, ba zan sake ba, ka bawa yaya Aseef hakuri, dan naga ransa ya ɓaci sosai, In Sha Allah ba zan sake ba". Tana magana tana murza ƴan yatsun hannunta.
Hannun nata ya kamo cikin nashi, "Ba komai ki rinƙa kula Kinji? Laifi nane da na aike ki ɗakin, da ya kamata naje da kaina ne, laifin ki ke kuma da kika taɓa wayar, ki sani zuciyar Lion ba irin tamu bace, mu muna iya controlling namu, shi kuma ba haka yake ba, idan kika yi mishi abin da ya ɓata mishi rai, a lokacin zai buɗe miki aiki, kuma na sha gaya miki hakan, kada ki kuskura ki shiga gonarsa, yanzu kinga dole zai ɓata rai, ko in ce miki zamu ɓata rai, daddynmu bai san muna Nigeria ba, ba zai taɓa yarda mu zo Africa ba, dan ta yi nisa da shi sosai, yanzu yana tunanin muna Spain ne, shiyasa ya hakura ya daure ya zauna a Usa, daddy ba zai iya nisa damu har haka ba, bai taɓa ba kuma ba zai iya ba, idan har yasan Nigeria muke, ba zai taɓa yarda ba, zai ce sai ya biyo mu ko kuma mu dawo yau yau ɗin nan ba sai gobe ba, kuma kinga akwai aikin da muke yi a nan, yanzu dai shiga ciki, amma dai akwai matsala". Duk jikinta ya yi sanyi da jin maganarsa, ta yi kuskure, su kuma basu son daddy ya ce zai zo Nigeria, dan yanayin jikinsa, tafiya mai tsawo ba karamar wahala zai sha ba, jiki a mace ta nufi cikin gidan dan yin wanka, tana shiga bedroom nata ta wuce toilet.
A ɓangaren Aseef kuwa, yana isa wajen pool ɗin shi kuma Lion yana fitowa zai nufi cikin gida, a tare suka jera zuwa cikin gidan, kwata kwata bai gaya mishi abin da yake faruwa ba, a palon kasa suka rabu ya wuce bedroom ɗin Areef, shi kuma Lion ya haura sama zuwa nasa bedroom.
Yana shiga cikin ɗakin ya ɗan tsaya shiru yana tunanin me ya kawo wannan yarinyar yau kuma ɗakinsa, dan ya tsinci kamshin perfume nata a cikin nasa, dressing room nasa ya wuce. After some minutes ya fito sanye da wandon jeans fara tas zuwa gwiwarsa, sai riga polo t-shirt ita ma fara tas, ba ƙaramin kyau ya yi ba, saman bed nasa ya zo ya zauna, sai tashin kamshi yake yi, ɗan bakin nan nasa kamar ya sanya jan janbaki, sai wani kyalli ɗan bakin nasa yake yi.
Wayarsa ya ɗauka, ya sha ruwan mamaki lokacin da ya kalli miss call ɗin daddy almost 10, shiru ya ɗan yi kafin ya cire password ɗin wayar, ɗan waro idanunsa waje ya yi lokacin da ya kalli an yi picking na first call da daddy ya yi, bai kawo komai a ransa ba, ya yi tunanin ma Aseef ne ya yi picking, cikin kwanciyar hankali ya fara kiran daddyn video call, tamkar jiransa dad yake yi, bugu ɗaya ya ɗauka, fuskar nan nasa a ɗaure tamau, yau ya fito a ainahin dangerous Boss ɗinsa, zuba mishi idanu Lion ya yi yana kallon shi, bai ce ko uppan ba. "Who is she Romeo?" Shi ne tambayar da ya fara yi mishi, shiru ya yi bai amsa ba. "Me haɗinta da kai? Meyasa wayarka zai kasance a hannunta?" Nan ma shiru ya yi bai yi magana ba, sai bin daddyn nasa da ido kawai yake yi.
Tsawa daddyn ya daka mishi "Am i not talking to you?!" Ɗan zaro idanu kaɗan ya yi yana mamakin, wai yau shi daddy yake yi wa tsawa har haka lallai. "Romeo am i your mate?!" Nisawa ya yi kafin gently ya fara magana "Daddy i don't know what to say, because i don't know what you are talking about ".
"Romeo how comes za'a ce mace ta ɗauki wayar ka kuma ka ce you don't know her, how this can be possible?". Shiru ya yi dan shi ba zai iya wannan surutu na daddy ba. "Romeo a ina kuke yanzu haka?" Kai tsaye ya amsa mishi da "Nigeria". "Nigeria kuma?" Jinjina mishi kai ya yi alamar tabbatarwa. "Okey yanzun nan ku haɗa kayanku ku dawo, yau ba sai gobe ba, kuma i really hate this girl that a saw koma wace ce".
"Ba zai yiwu ba daddy, sai na kammala abin da nake yi zamu dawo". Ya yi magana a nitse cikin kwanciyar hankali.
A fusace dad ya miƙe tsaye, cikin fushi da kausashiyar murya ya fara magana, "Romeo I'm your father who born you not your friend or your Triplets!! So is better for you ka san irin maganar da zaka rinƙa gaya mini".
Shi ma a wannan karon ranshi ya ɓaci, baya son hayaniya ko kaɗan, daddy ya zo yana ta wani daga mishi tsawa, a fusace ya miƙe tsaye, cikin tsawa da ɗaga murya ya mayarwa da dad amsa kamar haka "I'm so what dad, am so what if it is you had born me? Take me back to your womb!" Tashin hankali da ba'a sama mata date.
"Romeo are you hard what you said? Are you forget who you're talking with?!!".
"Am talking with father of TRIPLETS so what,?". Babbar magana!!.
Dafe saitin zuciyarsa daddyn ya yi, cikin kunan rai ya buɗe baki da kyar ya furta "Romeo umarni nake baka yau ba sai gobe ba ku dawo Usa". "Daddy ba zan dawo ko'ina ba har sai na kammala abin da nake yi, so ya rage naka ka hakura ko ka ɗauki mataki, ni dai na gama maganata, ba kai zaka rinƙa gaya mini abin da zan yi ba, a matsayina na soja aiki yana iya kaini ko ina, so ba umarninka zan bi a kan aikina ba that's all!!". Shaiɗan da zuciya sun ɗebesa sosai yau
"Romeo so kake yi ka kashe ni ko?". Shiru ya yi dan idan ya ce zai buɗe baki zasu yi kaca kaca da dad ne, saboda babu wanda ya isa ya ce mishi ga abin da zai yi, sai wanda ya yi niyar yi, a cewarsa, daga karshe ma katse kiran ya yi tare da yin wurgi da wayar a saman gado, cikin zafin nama ya nufi waje, kyawawan gashin dake kwance a hannunsa har wani miƙewa suke yi saboda ɓacin rai, Rimsha ta raina shi da har zata ɗauka mishi waya, ga shi tasa dad ya zo yana yi mishi hayaniya a kai, kuma kowa yasan shi mutun ne da baya son magana ma bare hayani ya, ta ja ransa ya ɓaci ya mayarwa da daddynsa magana, duk da cewa su yin hakan ma a wajensu ba wani laifi bane, wai dan yara su mayarwa da iyaye magana, ba su ɗauke shi a matsayin wani laifi ba, domin tun farko a kan hakan iyayen ke renan ƴaƴan, su sunma yi ƙoƙarin da har suke iya dannewa suna yiwa dad ɗin su biyayya, amma ba dan haka ba kowa yasan yadda ainahin rayuwar turawa yake, yara suna da dama da ƴancin yin komai da suke so, doka ce a dokonin kasarsu, ciki kuwa har da rufe iyaye a prison yara suna yi, a takaice dai da yara da iyaye su duk ɗaya ne a wajensu. ALHADULILLAH DA ALLAH YA YI MU A WAJEN DA MUKE YIN KASA DA MURYA A GABAN IYAYENMU, WANNAN MA KAƊAI BABBAR NI'IMA CE A GARE MU.
Yana fita bai zame ko'ina ba sai bedroom nata, lokacin da ya sako kansa ya shigo ɗakin, ita kuma ta fito daga toilet ɗaure da towel a kirjinta, da alama wanka ta yi, ganinsa yasa ta watsa a guje ta koma cikin toilet ɗin, da karfi ta banko kofar har da murza key, rai a matuƙar ɓace ya karisa wajen kofar, da karfi ya sanya kafa ya take kofar, wani irin jijjiga ta yi bata buɗe ba, sake ɗan komawa baya ya yi, a zafafe ya take ta da karfi, sai ga kofar ta ɓalle, ihu ta kurma ganin hakan, takawa ya yi cikin zafin nama ya damko gashin kanta, dama ga shi babu ɗankwali a kan nata, ta saki gashin har baya, jawota ya yi da gashi har zuwa tsakiyar ɗakin, wurgi da ita a kasa ya yi, rai a matukar ɓace ya daka mata tsawar ta yi mishi shiru kokuma ya take ta a wajen har sai ta mutu.
Jin hakan yasa ta miƙe a guje dan ta bar ɗaki, tasan a wannan yanayi da yake ciki tsab zai iya aikata duk abin da ya faɗa.
Wani irin mahaukacin damƙa ya yi wa wuyarta, sosai ya shaƙeta tare da zaro mata dara daran blue eyes ɗin nan nasa, gently ya yi magana. "Waye ya ce ki taɓa mini waya?". Ba bakin magana, sai ma ƙoƙarin jawo numfashinta da take yi domin ta rayu, ita ko da iya idanunsa da ya zaro mata ma ya barta, to zata iya mutuwa, ba sai ya kara mata wani azaban ba, a yau ne ta fara nadamar saninsa a rayuwarta, zata mutu ba tare da ta sake haɗuwa da su mummy ba, da kaɗan da kaɗan ta fara dai na kallo, wani irin duhune ya turnuke idanunta, har lokacin kuma bai saki wuyar tata ba, yau ta kure shi, ya jima yana danne zuciyarsa dan kada ya yi kisan kai, dama ya san duk ranar da ya sauƙe hannunsa a jikinta da nufin hukunci, tofa tabbas sai dai gawarta, tana yi mishi Laifuka da dama yana dannewa saboda Triplets, Imran da kuma daddynta.
"Ba dake nake magana bane?!". Ya mance ba ta yadda za'ayi ta yi magana, ya shaƙeta sosai, sai fafutuka take numfashinta yana gaf da ɗaukewa, idanunta har sun yi jawur da su kamar wuta, ga hawaye wani na bin wani, abin gwanin ban tausayi, sai dai shi ko ɗingon tausayin babu a zuciyarsa, sau da dama yana ɗaukar kowa kamar soja, hakan kuma ba ƙaramin cutar da mutane yake yi ba.
A hankali towel dake jikinta ya warware ya gangaro kasa, yana ƙoƙarin faɗuwa, a zafafe ya sanya ɗayar hannunsa ya tare mata a daidai cikinta, runtse idanunsa ya yi, yarinyar nan tana neman kure zuciyarsa, idan ya biyewa zuciyarsa tabbas zai halakata, gently ya hauro mata da towel ɗin sama ba tare da ya buɗe idanunsa ba, bai kuma saki wuyar nata ba, ya kawo towel ɗin daidai saitin kirjinta, a zafafe ya kuma saki towel ɗin ta zame ta faɗi kasa.
Ba komai bane yasa ya saki face hannunsa da ya sauƙa a saman tula tulanta, ita kanta sai da ta waro dara daran idanunta waje, tamkar zasu faɗi kasa, nan take ta ji ta watsake, a karo na farko ya kallah, yanzu kuma ya taɓa, wayyo Allah wani irin kululun bankinciki ne ya ziyarci zuciyarta, ji ta yi gabaɗaya ta tsane shi, shi kuma wannan taɓasu da ya yi, sun sanya ya ji wani irin mahaukacin shock a jikinsa, daga tafin kafarsa har izuwa tsakiyar kansa sai da ya amsa, ko kusa ko alama bai taɓa taɓa kirjin wata mace ba a rayuwarsa, jinsu ya yi wani iri, sun buga mishi kwakwalwar kansa ba kaɗan ba, wani irin yanayi mara misaltuwa ya ji a jikinsa, gently ya zame hannunsa daga wuyar nata tare da juya mata baya ba tare da ya buɗe idanun nasa ba, cike da ɓacin rai ya sanya hannu ya fara watsa gashin kansa yana ciza lallausan laɓɓansa na kasa.
Yana sakinta ta zube kasa tana tari tamkar maƙoshinta zai fashe, yasan kallon tsiraicin mutun a musulci haramun ne, hakan yasa ya juya mata bayan, kuma saboda hakan yasa ya sake ta, ba dan haka ba yau sai dai a ɗauki gawarta, ita kuma tari take yi tamkar ba zata rayu ba, duk da halin da take ciki bai hanata lallaɓawa ta ɗauki towel nata ta ɗaura ba, gabaɗaya ilahirin jikinta kerma yake yi, ta gama tsorata da lamarinsa, ta sadaddaƙar mutuwa zata yi yau, bawan Allah yana da ƙoƙari wajen ganin ya kula da addininsa, sai idan abu yafi karfinsa ne yake take wa, amma gaskiya yana ƙoƙarin sosai, duk da yake Bature kuma krista a baya, yanzu ya riƙi addinin musulunci sosai, hannu bibbiyu ba wasa.
A wannan hali Areef ya shigo ya same su, nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke dan yasan dama za'ayi hakan, shiyasa ma da ya je ɗakin Lion bai same shi ba, ya nufo ɗakinta dan ya dubata shin tana lafiya.