Kenza eBookz

Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 4

Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 4

Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 4: Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 4. Miƙewa ya yi daga rumfar da ya yi mata ya zuba…

3,363 words

Miƙewa ya yi daga rumfar da ya yi mata ya zuba mata ido sosai, yana kare mata kallo, tabbas ta kara kyau sosai, amma kuma ba abin da yake tunanin ɗin bane, kawai dai kyau ne na tsantsan kula da take samu daga gare shi.

Ganin ba abin da yake tunani bane yasa ya shafa shafaffen cikinta nata tare da haɗe fuskokinsu, kasa kasa ya ce "Jelly ita kaɗai Allah ya bani, ina bala'in son yara, wlh idan na kalli yara a hannun wasu, ji nake tamkar in je in kwacesu, ya Allah ka bani baby a wannan haɗuwar tamu da zamu yi yanzu". Ya kai karshen maganar yana yana mai hauro da hannunsa zuwa saman kirjinta.

(Tofa shi kuma Romeo ba abin da ya tsana kamar yara, ga wasu kuma a nan suna nema ido a rufe, Allah ya shirya Romeo da rashin son yara)

"Daddy nima ina son yara wlh, musamman ma kanana suna da kyau kamar me". A hankali hankali ya fara shafo breast ɗin nata yana faɗin "Musamman ma idan a kace yaran sun yi kama dake ba, wlh ba ƙaramin kyau za su yi ba".

Zata yi magana ya capko bakin nata tare da zura mata harshensa cikin tata ya fara kissing nata.

Shiru ta natsu tana biye mashi, yanzu idan da sabo, ta gama sabawa da jarabarsa, tun abin yana damunta har ya dai'na, ta rungumi kaddararta na hakura da jararrabar mijin nata, sai dai kuma shi ba kamar sauran irin mazanmu na yau da kullun bane, mafi yawancin maza suna ɗauka jima'i shi ne kawai aure, shi ba haka yake ɗauka ba, tabbas yana da jarabar tsiya, amma kuma yana ƙoƙarin ya zama cikakken miji, yana ƙoƙarin ya yi koyi da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, domin Annabi har wanke wanke yana taya su Nana A'isha, Nana A'isha da bakinta ta ce har ƴar tsere suna yi da Manzon Allah (S.A.W) a gida, ya kama maza su sani ba iya biyan buƙatarsu a wajen mace, da ciyar da ita da shayar da ita ne kawai ya zamana hakki a kansu ba, ya kamata su nemi sanin tarihin fiyayyen halitta domin su samu gobe mai kyau, ga dai misali akan daddyn Jelly, yana balain kaunarta, yana kula da ita, yana faranta mata, ya mai da ta tamkar wata sarauniya, to yanzu ku gaya mani me ya ragu da shi da yake yi mata hakan? Wlh babu abin da ya ragu da shi, sai ma karuwa da ya yi na samin ɗumbin lada wajen Ubangiji, ya yi koyi da Manzon Rahma, ba ko wani namiji ne zai iya yin hakan ba, amma yana da kyau ku rinƙa kwatantawa koma yayane, domin a rage wasu matsalolin na cikin rayuwar aure, kuma, mata na juyo gare mu, yana da kyau mu gyara halinmu, misali akan Aunty, Ayla, da kuma Umaisha, irin halinsu yasa dole mazajensu ke kyautata masu, hakuri, juriya, riƙo da addini, kyautata mashi, kome ya ce matukar bai saɓawa Allah ba cene mashi to, kuma kiyi mashi a lokacin, kada ki yi gardama ko ki yi musu da shi, ki daure ki jure ki yi biyayya, ko da baki samu jin daɗi yadda kk so a nan duniya ba, ki sani a lahira zaki more, zaki huta, zaki ji daɗi fiye ma da yadda ki ke so ɗin, kada ki yarda ki yi biyu babu, babu duniya kuma babu lahira, kada ki yi koyi da irin halinsu Ommu, ki tabbatar kin yi koyi da halin ɗaya daga cikin waƴan nan Aunty, Ayla, ku kwatatan ku yi tunanin me yasa mazansu ke kyautata masu? Meyasa suke kaunarsu? Saboda sun nunawa mazan nasu cewa sune sarakunansu, sune sama da su, ko wani namiji yana son girmamawa, dan haka mu gyara, Allah Ubangiji yasa mu dace.

STORY💋

Sosai ya more kayarsa ko in ce suka mori juna, domin kuwa yanzu ita ma ta kware sosai, ya koya mata, ta zama irinsa.

Sun jima kwance manne da juna yana zuba mata kalamai tare da shagwaɓa kamar wani yaro, ya zama tamkar ƙaramin yaro a gaban matar tasa, ba ya wani damuwa da zancen zata raina shi, dan yasan ba haka take ba, shiyasa yake zuba mata shagwaɓarsa son ransa, kuma da yawan maza ba wai basa son yin hakan da matansu bane, kamar yadda na faɗa a baya, gani suke yi kamar idan suka yi hanan da matan nasu, matan za su rainasu, wannan dalili yasa suke tsare gida abinsu, wani ma da ya fara hakan sai ta fara ce mashi ragon namiji, to ƙalu bale garemu mata, ko yau a ka haifi namiji to fa sama yake da ke, ko da kuwa kin kai shakara hamsin, Ubangiji ne ya fifitasu akan mu, mune a kasarsu, ba lallai sai miji bama, ko wani irin namiji sama yake da mace, to ina ga kuma ance mijinki? Wadda shi ne Annabi ya ce, da bawa yana yi wa bawa sujjada, to da tabbas zai yi wa mace umarni ta rinƙa yi wa mijinta domin girmamawa, tabbas Allah ya girmama miji sosai akan mata, ko me miji zai yi maki bai kamata magana ta raini ta shiga tsakaninku ba, tun da Ubangiji da kansa ya bashi wannan girma da kuma power, yana da kyau mu kula da hakan dan kada mu zo duniya a banza kuma mu koma a banza, Annabi ya ce mata sunfi yawa a wutar jahannama, wannan magana kuma kunsan tabbas haka ne, innalillahi wa inna ilaihir rajiun......😭 Ba kuma komai ne yasa mata suka fi yawa a wutar jahannama ba fa ce kin bin umarnin mazajensu, zagin mazajen da kuma rainasu, hakan yasa suka fi yawa a wuta, to dan Allah mai karatun littafi na, kada ki bari ki zama ɗaya daga cikin irin waɗan nan mata, nasihata a gareku shi ne, ku yi hakuri ku daure ku danne, da ki cuci mijinki, wlh gwara shi ya cuceki, kuma ki yi wa Allah ki yafe mashi tare da yi mashi addu'a shiriya, tabbas Allah baya barci, yana ganin komai da yake faru, sai ki ga sanadiyar yafe mashi da kika yi, Allah ya baki gidan aljanna ko da kuwa baki yi aikin shigarta ba, to dan haka ina mai mana nasiha akan hakan, sannan kome zaki yi ki tabbatar domin Allah zaki yi, dan ki samu wannan rabo ta ni'imar Allah, idan ki ka yi domin wani, to ki sani wanin bashi da wuta kuma bashi da aljanna, to is better for you ki yi domin mai wuta da aljanna, dan ki shiga cikin aljannar, Allah Ubangijin ya sa mu dace, ya kuma bamu ikon gyara kura kuran mu, ina kara jaddada mana, muji tsoron Allah, a duk in da muke, mu san Allah yana ganin mu, kuma mutuwa bata da tabbas, tana iya zuwa a ko da yaushe, tana iya ɗaukarki kina tsaka da cin abinci ko aikata wani abin, ace mutuwa ta ɗauki mutun yana aikata saɓon Allah, ina zai tsaya da wannan bala'in,. Akan abin da kika mutu za'a tasheki, kada ki manta a ranar gobe kirayama tabbas ba ke zaki yi magana ba bare ki yi karya, hannun da kika aikata sharri ko alkhairi, shi ne zai yi magana da izinin wadda ya halince shi da mu baki ɗaya, shi zai faɗi abin da kika aikata da shi, haka zalika sauran sassa na gaɓoɓin jikinki, to dan haka mu kiyaye, fatana shi ne mu gudu tare, mu kuma tsira a tare, Allah kuma ya sa hakan Amin, ba zan so ace mai karanta littafi na ta kauce hanya ba, zanji zafin hakan fiye da tunanin mai tunani. YA ALLAH KASA DUK MASU KARANTA BOOKS NA, SU KASANCE NA KIRKI DAN KA HAƊA MU A ALJANNA, IDAN MA AKWAI WANI HALI MARA KYAU DA SUKE YI A ƁOYE, YA ALLAH KA YAFE MASU, KASA SU GYARA DOMIN MU KASANCE A TARE A ALJANNA, INA SON MASU KARATUN LITTATAFAINA💘💋❤️.

STORY💋

Sai da ya ga ta fara yi mashi barci a jiki sannan ya ce ta tashi su je su yi wanka, make mashi kafaɗa ta yi, cikin shagwaɓa da magagin barci ta ce "Ni barci nake ji daddy".

Shafa kanta ya yi yana faɗin "Babyn daddy, ki hakura na yi maki wanka sannan ki yi barcin ko? Bana son ki yi barci da najasa a jiki, Annabi ya tsawatar akan hakan, ya hanemu da hakan, domin hakan babbar barazace ga lafiyar ɗan adam, idan bawa yana cikin najasa fa to komai yana iya faruwa da shi baby, ciki kuma harda asiri, tsafi, aljanu, shaiɗanu, da dai sauransu, dan haka ki daure daddy ya yi maki wanka, in yaso sai ki zo kiyi ta barcinki har sai time da kike so, ni kuma zan yi zaman jiranki har sai kin tashi daga barcin sannan mu fita unguwar ko?".

Duk jikinta ya mutu da jin nasiharsa, hakan yasa ta miƙe, jikinta duk a mace saboda barci, haka ta diro kasa daga saman gadon, sannan suka nufi toilet.

After some minutes, ya fito riƙe da hannunta suka nufi gaban mirror, dukkansu suna ɗaure da towel, da alama dai a tare suka yi wankar.

Lotion ya shafa mata kafin nan ya sanya mata kananan kayanta tare da fesheta da perfume nasa masu daɗin Kamshi, sannan ya ruƙo hannunta suka wuce saman gado yana faɗin. "To jeki kwanta bari na shirya na zo mu kwanta sai zuwa anjima mu fita ko?".

Gyaɗa mashi kai kawai ta yi kafin ta wuce ta haye saman gadon, shi kuma, ya wuce ya nufi gaban mirror dan ya shirya.

Kafin ya gama shiri ya dawo, har ta yi barci abinta. Kusa da ita ya zo ya kwanta yana fuskartar sama, kamar mai yin wani tunani.

Can kuma kasa kasa ya furta "Ina son sanin su waye iyayenki? Ina son sanin a ina suke? Meyasami babanki? Meyasa mamanki ta rayu dake cikin kunci da wahala duk da cewa ta ce mahaifinki yana da kuɗi? Ina buƙatar waƴan nan amsoshi wadda kuma nasan mamanki ce kawai zata iya bani su!".

Shiru ya sake yi yana mai jin tsantsar kaunarta yana kara ratsa shi, tabbas yana bala'in kaunarta, amma kuma yana tsoron samun haihuwa da ita ba tare da ya san tushenta ba, in fact a matikar tsorace yake a duk lokacin da ya haɗa jiki da ita, jarabace kawai irin tasa yasa yake kusan tar ta ɗin, domin kuwa yana ji a jikinsa tabbas tana da alaƙa da su mummyn jelly, damuwarsa ɗaya kada ya kasance wadda ta haramta ne a gare shi ne, yasan mumyn jelly bata da ƙanwa, to yaya abin yake kenan?.

Da wannan tunane tunane barci ya kwashe shi, sai wani sauƙe ajiyar zuciya yake yi cikin barci, ita kuwa, Baiwar Allah, cikin kwanciyar hankali take zuba barcinta, numfashinta na fita a hankali.

GIDAN ABBO.

Tun da suka isa gida, Aafia ta kasa sakin jiki da su, sai wani ƴan kame kame take yi, ba yadda Ummi bata yi ba, amma ina, A'AFIA taki yarda ta saki jikinta, da suka ga haka, sai suka kyaleta, ɗakin Jelly Ummi ta kaita kafin ta dawo ta fara sallamar ƴan biki, shi kuma Nawid ɗakinsa ya wuce abinsa, ya je ya yi wanka ya kwanta yana tunani irin auren da aka yi mashi, gabaɗaya ya mance da zancen Abbo, ita ma Ummi bata kara tambayar ina Abbo ɗin ba, bata kara neman numbersa ba, abin kamar ba lafiya ba, duk sun mance Abbo kam.

Gabaɗaya jama'ar da suka zo bikin Ummi ta sallamesu akan anriga da an ɗaura aure an wuce wajen, taki nunawa bakin waje Aafia, ƴan uwanta kawai ta nunawa ita tare da yi masu bayanin abin da ya faru na canjin Amaryar da aka yi, ba karamin daɗi suka ji ba, sun kuma yi alkawarin zasu yi gangami suje su gaishe da Abbi, sannan su yi mashi godiya, sosai Ummi ta ji daɗi, amma kuma har yanzu tana tunanin Jelly, kewarta na nan a cike a cikin ranta, Allah ya jarabceta da son jelly ba kaɗan ba.

Har karfe 10 na dare Abbo bai dawo ba, babu shi babu labarinsa, haka zalika su kuma, ba wanda ya sake zancen shi, da alama ya rufe masu baki ne, ya kuma mantar da Nawid abin da ya faru a daren shekaran jiya.

Ummi da kanta ta shirya Aafia tsaf, ta yi mata kwalliya tare da bata kayan da ta sayawa jelly wadda zata sanya a ranar shiganta ɗakin miji, da yake Aafia ɗin bata da wani ƙiba, sai kayan suka zauna mata a jikinta sosai, danƙareriyar lace ce, milk color, kwalliyar jikin lace ɗin nan an yi sune da manya manyan zanen fulawa blue color, sannan an zuba mashi wasu shegun Stones masu bala'in kyalli, kuma stones ɗin sun daku da jikin lace ɗin sosai, lace ne mai shegen tsada, sai wani walwali yake, manya manyan abubuwan hannu na gold ta sanya mata a hannu wadda sun kasance nata ne da ta jima da saya ta ajiyewa matar ɗan nata kwaya ɗaya tilo a duniya zai aura, bakaramin kyau Aafia ta yi ba, sai dai idanunta da suka yi ja, alamar ta ci kuka ta ƙoshi, wani dankareren sarkar gold Ummin ta sake ɗaukowa ta sanya mata a wuya, sannan ta bata duk wasu kayan gyara da HJY BATULA ta haɗawa jelly bata gama shanyewa ba, ba musu ta ƙarɓa ta sha, komai Ummi ta ce mata, bata cewa A'a, sun zama kamar raƙumi da akala, a takaice dai, da kayan da aka sayawa Amarya jelly, da shi aka yi wa Aafia amfani, humra masu shagen daɗin kamshi Ummi ta sanya mata.

Amarya fa masha Allah, ta yi kyau tamkar ka sace ta ka gudu da ita, sai tashin kamshi take yi, mayafi Ummi ta rufa mata sannan ta riƙo hannunta suka nufi bedroom ɗin Nawid.

Da sallama suka shiga cikin ɗakin, sai hawaye Aafia take yi kasa kasa a cikin mayafin, domin kuwa yanzu a duniya babu abin da take tsoro biyun namiji, tamkar yadda take tsoron mutuwa, haka take tsoron haɗa ido da angon nan nata, jikinta sai kerma yake yi, Allah sarki baiwar Allah, ta ɗanɗani bakar azaba a hannun ƴan kidnaping, abin ya zauna a zuciyarta, hakan ya haifar mata da razana a cikin ƙwaƙwalwarta, wannan yasa kuma take mutuwar tsohon maza, ciki kuma har da angon nata, wato Dr Nawid, mutumin da take mutuwar so, yau ya zama mallakinta amma tana ji tamkar kabari aka kawota shiga ɗakin nan nasa da suka yi.

Lokacin da suka shigo yana zaune a gaban laptop nasa yana aiki, ya yi wanka yana sanye cikin kayan barci masu kyau brown colar, idanunsa na sanye da medicated glass, hannunsa na riƙe da pen ga kuma tarin takardu a gabansa, laptop ɗin nasa kuma tana ɗaure saman table dake tsakiyar bedroom ɗin nasa, shi kuma yana zaune saman wata sofa irin wadda ake sanya guda biyu a cikin bedroom ɗin nan.

Jin sallamar Ummi yasa ya ɗago kansa yana amsawa, cike da kulawa ya yi Maganar.

Karisowa cikin ɗakin suka yi, a gefensa Ummi ta zaunar da Aafia, ɗan gyara zama ya yi ta yadda Aafia ɗin zata zauna da kyau, sannan ita kuma Ummi ta koma ɗayar sofar ta zauna.

Wani irin razana A'AFIA ta yi lokacin da Ummi ta zaunar da ita kusa da shi, jikinta har wani kerma ya fara yi, kasa ta yi da kanta tana cigaba da hawayenta, abin gwanin ban tausayi, daga Nawid har Ummi ba wanda ya lura da tana hawaye, saboda mayafin ya rufe mata fuska, kuma ta sunkuyar da kanta kasa.

Nasiha sosai Ummi ta yi masu kafin ta yi masu sallama ta fice daga ɗakin. Ji Aafia tayi tamkar ta tashi ta bi bayanta, amma ba halin yin hakan, saboda bata da amsan da zata basu idan suka tambayeta lafiya.

Ummi na fita ya juyo da kallonsa kanta, cike da kulawa ya ce "Sannunki?". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Ina wuni?" Ta faɗa cikin muryar kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro.

Maganar da ta yi tasa ya gane tana kuka, dan haka sai ya juyo da kyau suna fuskantar juna, hannu ya sanya ta buɗe mayafin nata, cikin sanyin murya ya fara magana "Kiyi hakuri, nasan wata kila kema baki so na, wata kila akwai wanda kike so, kila ma har kunyi alkawarin aure, amma ina son kiyi hakuri mu yi wa iyayenmu biyayya, Ummina tana masifar sonki, ke kuma Abbinki yana suna da har ya bani ke, ba zan taɓa mantawa da shi ba, ki dai'na kuka, na miki alkawarin zan riƙe ki hannu bibbiyu, ba zan taɓa saki cikin kunci ba, duk duniya idan kika cire iyayena, yayanki Prof shi ne mutun na uku da nake so, to ko dan Imran zan sanya ki farinciki, yanzu dai dan Allah ki daina kuka kin ji ko? Abar batun dangantakar da yake tsakanin Ummi da Aunty Hadiza, ke kanwata ce domin da ni da Prof duk ɗaya ne, dan haka ki ɗauke ni a matsayin Prof Kinji?".

Kara tsananta kukan nata ta yi sosai, domin ita kaɗan tasan ciwon da yake a cikin zuciyarta.

Dogon numfashi ya ja tare da sauƙewa a hankali, kafin ya sanya hannu ya riƙo hannayenta, yana ƙoƙarin yin magana, a razane ta kwace hannayen nata, jikinta ya kara tsananta kermar da yake yi.

Bai damu ba, domin yasan waye Imran, yasan shi da addini sosai, so yana tunanin gabaɗaya kannensa haka suke, shiyasa da ta kwace hannunta sai ya yi tunanin ko dan irin faɗan da ake musu a gida tun suna yara akan kada su bari namiji ya taɓa su ne.

Cire medicated glass ɗin face nasa ya yi, sannan ya ajiye pen ɗin hannunsa, cikin natsuwa ya fara yi mata nasiha tare da nuna mata cewa shi mijinta ne, ko ya taɓata ba wani matsala, dan haka kada ta damu, har lokacin kukanta kawai take yi bata kula shi ba, da alama kuma bata cikin natsuwarta.

Ganin hakan yasa ya jawota jikinsa ya rungumeta yana ɗan bubbuga bayanta, jin nasihar da ya yi mata ne yasa bata tashi daga jikin nasa ba, ta kwanta ta cigaba da kukan da take yi.

"A'AFIA baki so nane yasa kike yin wannan kuka haka?" Ya yi maganar can kasa kasan maƙoshinsa, tayi kuka sosai, ta kasa magana, sai dai kuma ta ɗan rage kukan nata yanzu.

Hannu yasa ya ɗago haɓarta yana kallon face nata, idanunta a runtse, shiru ya ɗan yi na ƴan mintoci kafin ya ce "Dan Allah me zan yi maki ki dai'na wannan kukan ne? Ni bana son kukan nan, ke amana ce a wajena, sannan kanwata ce ke, kuma matata, idan baki so na ne, ki gaya mani, ni nasan ta yadda zanyi wa Ummi bayanin ta fahimceni, kuma nasan shima Prof nasan zai fahimceni, sannan Abbinki ma zai fahimta, auren dole bashi da wata faida, ni nasan zama da wanda baka so babban ciwo ne, ba kowace zuciya zata iya jurewa ba, to kada ki damu, idan baki sona ko kuma kina da wanda kike so, ki gaya mani kinji kanwata?". Ya kai karshen maganar yana cire mata mayafin jikinta.

Girgiza mashi kai ta fara yi, amma dai ta kasa buɗe baki ta yi magana. "Bakiso na ne kike girgiza kai?".

Sake girgiza mashi kai ta yi a karo na biyu.

"Kina sona?" Nan kuma shiru ta yi mashi bata motsa ba. Shiru shima ya ɗan yi kafin ya zame mata mayafin nata gabaɗaya ya ajiye a gefe.

"To meyasa kike kuka?". Sake girgiza mashi kai ta yi, bai takura mata lallai sai ta yi magana ba, domin kuwa yasan ba zata iya yin magana ba, saboda kukan da taci ta ƙoshi.

Bayanta ya fara shafawa a hankali hankali yana jin yanayi mai daɗi a tattare da shi, ita kuma tun tana sassauta kukan nata har ta dai'na gabaɗaya, sai ajiyar zuciya na wadda ta ci kuka take sauƙewa.

Sun ɗan jima a haka, har barci ya fara ɗaukar ta, "Muje ki kwanta a gado ko?" Can kasa kasa ta jiyo voice nasa.

Kasa miƙewa tayi daga jikin nasa, domin kuwa duk jikinta a mace, zuba mata ido ya yi yana mai jin wani irin yanayi da ba zai iya fassara shi ba a tattare da shi.

Readers Also Read