Kenza eBookz

Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 42

Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 42

Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 42: Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 42. Ɗan zaro idanu ta yi tana tambayarsa wani…

3,323 words

Ɗan zaro idanu ta yi tana tambayarsa wani jarabawa kuma bayan wadda ya rubuta musu suka yi, ko dai ya yi wani bata sani bane? Da yake babu Allah a zuciyar bare ayi zancen kunya, sai ya fito kwaro kwaro ya gaya mata irin abin da yake da buƙata su yi kafin ya bata result mai kyau, a razane ta ce mishi ba zai yi wu ba, kai tsaye shi kuma ya ce mata to ba zata taɓa cin test na shi ba, kullum idan ta yi zero zata samu, idan dai har bata bashi kanta ba, to wlh ta shirya karɓar zero kullum, idan kuma ta shirya bashi kanta ko yanzu ne, to ta shiga toilet na shi dake cikin office ɗin zai zo ya sameta, tsabar rashin kunya har da ce mata ya yi ba zata jima ba, ba zai fi minti 20 ba anyi an gama, kuma kada ta damu ba wanda zai gane, dan ba zai yi mata yadda wani zai gane ba, da gudu ta miƙe ta yi waje dan ma kada ya ce zai taɓata, sai dukan uku uku kirjinta yake yi, har wani sara mata kanta yake yi, yanzu me zata cewa daddy da mummynta akan wannan test ɗin?.

Amma fa yadda Anaya ta yarda da boko ta ke kuma so, da Rimsha bata yi mata hakan ba, da tabbas dan ta ci test nata zata yarda mishi da abin da yake nema, dan dai kunga, da farko da Rimshar ta gaya mata, ba ta ɗauki abin a wani matsala ba, Allah dai ya sota da rahma ya kuma tsareta a yau kam, sai dai bamu san me gaba zata haifar ba.

Kuka ne mai karfi ya kubce mata, a ɗari ta shiga class ɗin nasu, Rimsha na ganinta ta miƙe a razane tana ambatar sunanta tare da tambayarta lafiya, zuwa ta yi ya rungumeta tana kuka ba tare da ta yi magana ba, jijjigata Rimsha ta fara yi tana ambatar sunanta, "Anaya lafiya kuwa? Ki yi mini magana mana, dan girman Allah ki gaya mini kada ki saka na suma, kin ɗaga mini hankali sosai, wani abin ya yi miki ne?".

Cikin kuka ta gaya mata duk abin da ya faru daga A har Z ta feɗe mata biri har wutsiya, daga karshe ta ɗaura da cewa ita test nata ne ma ya dame ta, yanzu Mr Emmanuel ya ce ba zai sake bata result mai kyau ba, ta shiga uku ya zata yi.

Goge mata hawayen nata ta fara yi tana rarrashinta tare da bata hakuri akan kada ta damu dan ya bata zero, ta barshi da Allah, zai saka mata, idan ta je gida ta kwana sallah ta kai kukanta ga Allah, zai yi mata maganin shi, da kyar ta samu ta rarrasheta ta yi shiru, a yau dai basu fita break ba har a ka dawo class, duk sun yi jugum jugum da su, abin gwanin ban tausayi, Rimsha abin ya shiga jininta sosai, ta san ita ma da wuya idan ba zero zai yi ta bata ba, yau duk wani karatu da aka yi musu, bai wani shiga kansu ba, har lokacin tashi ya yi, Rimsha aka fara zuwa ɗauka, tana ganin motarsu ta ce da Anaya ta zo su gaisa da ƴan uwanta, da murna Anayan ta bita suka je, sai dai ga mamakinsu sai suka ga Mark ne kawai ya zo, ta so ta tambaye shi inasu yaya Areef, amma ba sai na gaya muku ba, kun san halinsa sarai, bata ga fuskar tambaya ba, ko kallon in da take ma bai yi ba, Anaya tana ce mishi good afternoon sir, amma ina ko kallonsu bai yi ba bare su saka ran zai amsa musu.

Ɗan zunguran Rimshar ta yi kasa kasa ta ce "Rimsha a ina kuma kika samo Bature? Ko dai ɗan uwan ki ne? Dama kuna da ƴan uwa turawa ne?". Da yake bata taɓa bata labarin TRIPLETS ba, ita tana da siriri sosai, iya hirar school kawai take yarda su yi ban da na gida, wani lokaci har faɗa Anaya ɗin take yi mata ta ce wato ba zata bata labarin ƴan uwanta bako, sai dai ta yi murmushi ta ce zata bata mana, da haka suke rabuwa. Yanzu ma murmushi ta yi tare da shigewa cikin motar tana faɗin "Idan nazo gobe zan gaya miki, amma dai ba ɗan uwana bane, soja ne mai yi wa su yaya Areef girki". Ɗan sake leƙo shi Anaya ɗin ta yi, har ga Allah ya yi mugun shiga ranta, ta ji tana bala'in son shi, shi kuwa Rimsha na shiga ya kunna motar ya wuce suka bar Anaya tsaye tana ɗaga musu hannu.

Suna fita school ɗin uncle Shitu na danno hancin kan nasa motar, ya zo ɗaukar Anaya, Rimsha hankalinta na kan jakarta tana ɗan duba takardunta, bata gan shi ba, sun yi saɓani.

Uban gudu sosai Mark yake shararawa a kan titin nan, suna mantawa nan a Nigeria suke, ba Washington DC ba ne, Allah ya tsare suka isa gida lafiya lou, yana kashe motar a parking space ta riga shi fitowa ta nufi cikin gida, binta da kallo gateman ya yi, babu kowa a palon kasa, kai tsaye sama ta nufa.

Tana saka kafarta a saman benen shi ma yana sako kafarsa Brady na makale a bayan shi, dan bashi da wajen zama sai ya ɗane bayan Lion ɗin, ya iya tsiya sosai karen nan, baya taɓa yarda ya tafi da kafafunsa in dai ba dole ba, tun yana ɗan jariri Lion ya saba da goya shi a baya, shiyasa da ya girma ma yaki dena hayewa, ko Lion ya ce ya sauƙa ya tafi da kafa sai yaki kamar wani yaro, duk wata tsiya karen nan ya iya shi sanka sanka, da alama garden zasu je, yana ganinta ya diro kasa daga bayan Lion ɗin, kunsan karnika da shegen son shinshina mutun su ji ko daga ina ya fito, kun san su kamshi suke bi.

Ganin ya diro kasa yasa ta fara ja da baya da baya, ko sannu Lion bai ce mishi ba, bata ankara ba sai ji ta yi ta buge mutun ta baya, da sauri ta juya dan ganin waye ne.

Areef ne daga shi sai singlet da three quarter, yau garin ana zafi, rana ta take, kallon Lion dake ta tafiyarsa ko kallon in da suke bai yi ba ya yi, shi kuma Brady duk da Areef ya zo bai dena nufota ba, zuba mishi ido Areef ya yi sai da ya kariso wajen yana ƙoƙarin fara shinshinarta, wani wawan mari Areef ɗin ya kai mishi a kumatunsa, da karfi ya daka haushin da ya sanya Lion da ya yi gaba juyowa dan ya ga me ya same shi.

Kara mishi wani marin Areef ɗin ya yi, cikin harshen turanci ya tambaye shi me Rimsha ta yi mishi da yake takura mata a gidan nan? Ta shiga harkarsa ne? Ko kuma ta taɓa kula shi ne? Sit ya natsu tamkar yaro da aka nitsar ake yi wa faɗa da nasiha mai ratsa jiki, kun san fa suma dabbobi suna jin magana sosai,. Abin ya ɓatawa Lion rai, dan me akan wata Rimsha za'a marin masa Bradynsa, dan haka cikin harshen turanci ya ce da Brady "B fight for your ride!". Yana kai karshen maganar ya fice daga palon abinsa.

Ai kuwa tamkar alluran soja ya yi wa Brady ɗin, nan take ya daka haushi tare da yin tsalle ya haye jikin Areef ɗin ya fara kai mishi yagushi a fuska, ba ji ba gani yake yagushin shi, ƙoƙarin kama hannun nasa Areef ya yi, amma ina yaki yarda ya bada damar yin hakan, daga jikin Areef ɗin ya sake daka tsalle zuwa jikin Rimsha dake tsaye a wajen, ita ma yagushi ya fara kai mata ta ko'ina, yana yi yana daka uban haushi kamar ba gobe, da ganga kuma Lion ya ce mishi hakan, dan yasan Areef ba zai iya kama shi ta sauƙi ba, horon sojoji gare shi, ya horu ba karya, idan baku manta ba na gaya muku mafaɗaci ne na a mutu, kama shi ba abune mai sauki ba, yana da wayo over, dama shi Lion ɗin ne ya ce mishi ya rinƙa jin maganar TRIPLETS nasa, shiyasa yake raga musu, yanzu kuma tun da an ce ya kwaci ƴancinsa ai shikenan.

Sai ihu Rimsha take yi ta zube kasa tana birgima, ganin zai yi mata illah sosai ne yasa Areef ɗin nufarsa a zafafe, ransa a matukar ɓace ya yi ƙoƙarin kama shi, da yake yasan idan ya kama shi ba zai yi mishi da daɗi ba, sai da ya bari ya iso yana ƙoƙarin damko shi, sai ya daka wani uban tsalle ya haye saman kan Areef ɗin ya rufe mishi idanu da gashin jikinsa, kokawa suka fara yi ba kaɗan ba, a tsatsan ɓacin rai Areef ya yi wurgi da shi, ya bugu da jikin bango ya faɗi kasa, wani mahaukacin haushi ya sake dakawa tare da miƙewa ya yi wani girgiza, a guje ya sake mufarsu, Areef bawan Allah ba zai iya faɗa da shi bane saboda ciwon dake kirjinsa, bai gama warkewa ba, shiyasa ma Bradyn ya bashi wahala, baya iya ɗaga hannunsa sosai dan a gefen kafaɗa ne ciwon take, kuma Lion yana sane da hakan ya ce Bradyn ya kwatan wa kansa ƴanci, yasan a yanzu haka Brady zai ji musu ciwo sosai, da dai Areef yana da lafiya ne, da wane kaniyar Brady ya iya taɓasu ma, tuni zai yi wurgi da ɗan banza ko ya murɗe mishi wuya ya mutu kowa ma ya huta da masifarsa.

Yana nufosu da gudu Aseef da ya fito tun ɗazun ya zuba musu idanu ya sha gabansa, shi kuma Areef bama ta su yake yi ba, ya duƙa yana rarrashin Rimsha da Brady ya yagushiwa hannu, fuskarta ya so yagusa da waƴan nan shegun faratun nasa masu tsini, shi ne ta sanya hannunta ta tare face ɗin nata yagushin ya sauƙa a hannun nata, sai jini yake yi, shi ne Areef ya tsugunna yana bata hakuri tare da riƙo hannun nata yana dubawa.

Shi kuma Brady, faɗa suka fara yi da Aseef gadan gadan, sai wani ƙoƙarin yagushin Aseef yake yi, ai kuwa Aseef ya yi wurgi da ɗan banza, da gudu ya sake tashi ta nufo shi, a karo na biyu kuwa, maƙogoronsa Aseef ɗin ya damko, da karfi ya shaƙesa tare da zare mishi ido, cikin harshen turanci dai ya ce mishi "Au ka manta ni na sayo ku kenan? Da ni zaka yi faɗa? Ko Areef da ka jiwa ciwo dan bashi da lafiya ne mara kunyar banza, idan baka rabu da mu ka bar palon nan ba Allah sai na murɗe maka wuya ka mutu mun jefar da banza". Haushi ya daga mishi da karfi, mari shi kuma ya kifa mishi a fuska tare da damko hannayensa dukka biyu ya sake yin wurgi da shi a jikin bango, a wannan karon dai a hankali ya yi haushin, alamar ya jigata kuma ya wahala, ko kallon in da yake Aseef ɗin bai yi ba ya nufi su Areef dake ta faman yi wa Rimsha sannu.

Kusa da ita shi ma ya zo ya tsugunna tare da kamo hannun nata yana mata sannu, sai kuka take yi, shi ma Areef ya sha yagushi a fuska ba karya, miƙar da ita Aseef ya yi a kan suje ya saka mata magani, ba musu ta bi shi, shi kuma Areef ya ɗauka mata jakar school nata, suka karisa hayewa saman suka bar Brady kwance a kasa yana mayar da numfashi, ya wahala, ba karamin buga shi da bango Aseef ya yi ba, dan ma ya yi sa'a Areef ba shi da lafiya ai da murɗe wuyarsa zai yi ya mutu, dan yanzu tun da ya fara takurawa Rimsha Areef ɗin baya son shi, ita kuma abin da bata gane ba, idan ta gansu kada ta gudu, in ta gudu sai sun bita, amma da ta gansu zata zura a guje dan tsoro.

Sun zo zasu shiga ɗakin Lion ɗin ta tsaya, kallonta suka yi "Lafiya Rimsha?" Areef ya tambaya, cikin muryar kuka ta ce "Yaya Areef ina tsoron shiga ɗakin yaya Saif ni kam, zan zauna a nan palo kawai". Ɗan lumshe idanunsa ya yi tare da sake warosu a kanta, da hannu ya yi mata nuni da ta shiga ba damuwa, bata son yin musu da babban mutun, dan haka sai ta shiga kawai.

A saman bakin bed nasa Aseef ya zaunar da ita tare da ɗauko A box, saman bedside drawer ya ɗaura A box ɗin kafin ya fara buɗe wa yana duba magani, zama gefenta Areef ya yi, Aseef ne ya yi musu dressing na wajen tare da taimakon Areef ɗin, shi ya nuna mishi maganin da zai yi musu amfani da shi da sauransu.

Rimsha ta sha kuka ba karya, dan maganin yana da zafi, sai rarrashinta suke yi, Aseef ya rakata har ɗaki sannan ya dawo, a ɓangaren Lion kuwa, sam bai ji daɗin saka Brady da ya yi da ya yi faɗa da Areef ba, dan kuwa yasan tsab zai yi wa Areef lahani, amma ba yadda ya iya zuciya ce ta ɗebe shi, ya ji babu daɗi yadda Areef ɗin ya fifita Rimsha da ya sani jiya jiya a kan Brady da suka jima.

(kai gaskiya Lion da sauranka, saboda wakalanci dan baka ɗauki ɗan adam da daraja ba shi ne zaka ce kare ya fi ta, a fifita kare sama da mutun kenan? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, wannan rashin sanin darajar mutun har ina? Gaskiya ya kamata ace Lion ko ba yawa ne ka san darajan mutun.)

A ɓangaren Imran kuwa, lokacin da ya fita, pharmacy ya je ya haɗo mata magunguna ya dawo, har lokacin barcin wahala take yi, kiran Akila ya yi a waya ya tambayeta ina dollyn Jellyn, ta gaya mishi tana nan, ta bawa mai gadi ya zai fi kula da ita, dan wata rana idan tana da class ta tafi school babu mai bawa dollyn abinci, okey ya amsa mata da shi tare da ce mata zai zo ya ɗauka da daddare, tom ta amsa mishi da shi, ruwa mai sanyi ya tsaya a palo ya ɗauko mata tare da komawa cikin bedroom ɗin nasu, gefenta ya zauna jikin nata ya tsananta zafi over, har lokacin sai ajiyar zuciya take sauƙewa, wani irin mugun tausayinta da so da kaunarta ne suke kara ratsa shi, a hankali ya fara ƙoƙarin tashinta dan ta sha magani, yana yi kirjinsa na dukan uku uku dan yasan za'ayi dirama ba karya.

Da yake bata da lafiya sosai, sai bata wani bi ta kansa ba, ko da ta tashi, kuka kasa kasa kawai ta sa mishi, rarrashinta ya rinƙa yi tare da bata magani, karɓa ta yi ta watsa a baki, shi kuma ya sanya mata ruwa a baki, bayan ta gama ta koma ta kwanta tana kuka kasa kasa, yau dai bakin tsiwa ya mutu murus, kukan ma baya fita sosai. Kusa da ita ya kwanta, sai rarraahinta yake yi, da haka har wani barcin ya ɗauketa, kun san mai zazzaɓi da yin barci minti minti, shiru ya zuba mata idanu yana kallonta yadda take barci tana ajiyar zuciya, zubawa ɗan bakin tsiwar nan idanu ya yi, a hankali furta "Allah yasa daga haka bakin ya yi sanyi".......... To nima dai da Amin na amsa maka dan gaskiya idan bai yi sanyi ba akwai matsala kana ruwa.

A ɓangaren Rimsha kuwa, uniform nata ta cire tare da wucewa toilet dan ta yi wanka, har lokacin hannun nata yana ɗan yi mata zogi kaɗan kaɗan. Bayan ta gama wanka, ta shirya cikin doguwar riga abaya baka ta haye gado, yunwa take ji amma tana tsoron fitowa waje, a wannan hali Areef ya shigo ya same ta, lallaɓata ya yi ta miƙe su je su ci abinci, bata yi mishi musu ba dan yunwa take ji dama, tsoro ne ya hanata fita.

A palon kasa suka isko Aseef saman table yana jiransu, zama suka yi, kamar dai yadda suka zauna da safe, sun sakata a tsakiya, Mark ne ya zo ya yi serving nasu, bata musa ba, ta ci abincin nasu, yau kam ma kusan irin abincin Nigeria ne, shinkafa ce tasu ta can zara zara, sun dafata koriya shar, ta ji nama ba karya, sai wasu daga cikin kayan lambunsu da suke amfani da shi da sauran ingredient nasu, ta ci sosai dan ba karya ta ji yunwa, bayan sun kammala suka miƙe Areef ya ce ta zo su je garden, ba dan ta so ba ta bisu, yanzu tsoron Lion da Brady take yi sosai ba karya.

Zaune suka isko shi yana waya da daddynsu, daddy ya ce yana son ya zo Nigeria, shi kuma ya ce a'a ba yanzu ba, daddy ba zai iya jure rashinsu a kusa da shi ba, amma hakan ya hakura ba dan ya so ba, Brady na kwance a jikinsa, ya sha wahala ne yasa ya lafe a kirjin Lion ɗin tare da lumshe idanu.

Ita da Areef kujera ɗaya suka zauna, shi kuma Aseef kusa da Lion ya je ya zauna yana wani murmushi, yana son gayawa Lion ya je ya nema mishi auren AKila, amma ya fi son ya sami lokaci na musamman ya gaya mishi.

(Jama'a Lion da zuwa neman aure, Wayyo cikina anya kuwa wannan abin zata yuwu?🤣 Ba gara ma Areef ɗin ba, kuma dai ji yadda Lion yake cewa Imran ya kula da waƴan nan halittu🤣 wayaga Lion a wajen Abba ya je neman aure🤣)

💋GIDAN ABBA💋

❤️❤️TRIPLETS❤️❤️

*Duk wace ta karanta mini littafina ba tare da ta biyani hakkina ba Allah ya isa ban yafe ba, sai Allah ya tsayar da mu ranar da bata da abin da zata biyani face ladarta*

E35-36💋

💋GIDAN ABBA💋

Tun da Ammie ta shaki kamshin perfume ɗin Lion sabuwar rayuwa ya shigeta, duk wasu aljanun dake gidan da wasu dodannin sun gudu, rayuwarta ta bayane ya fara dawo mata, Baiwar Allah ashe duk rayuwar da tayi tsawon shekarun nan bata cikin hayyacinta, bata sani ba, yanzu ne ta dawo normal.

Wani daddaɗar kamshi air freshener ne yake tashi tun daga cikin babban palon kasa har zuwa harabar gidan, ko'ina na palon a tsananin gyare yake tsab, sai tashin kamshi ko'ina yake yi, har wani kyalli kayan cikin palon suke yi saboda tsantsar gyara da suka sha, gidan shiru da alama Akila ta tafi school.

Baki ɗauke da sallama Abba ya shigo cikin palon, ko kaɗan babu alamar mamaki a kan fuskarsa, domin kuwa shi ma yanzu ya dawo cikin hayyacinsa, abin da yasa kuma bai yi mamakin gyara palon da aka yi ba, saboda already yasan Ammie ba kazamiya ba ce, mace ce mai bala'in tsabta na amutu, akwaita da son gyara, ga bala'in son kamshi, shiru shiru bata son hayaniya, sai dai fa idan ka taɓota, zaka gane annabi ya faku, bata da fara'a sosai, amma ba laifi tana ɗan murmushi, yanzu gabaɗayansu ita da Abba sun dawo cikin hayyacinsu sanadiyyar turaren Lion........NASAN KOWA A ƘAGE YAKE DA YA JI TARIHIN AMMIE, TO KU GYARA ZAMA IN SHA ALLAH TARIHINTA NA NAN TAFE NAN BA DA JIMAWA BA, NIMA NA ƘAGU NAJI MENENE MATSALARTA? ME TAYIWA WAƳAN NAN SHAIƊANUN ALJANUN SUKE AZABTAR DA ITA HAR HAKA, GA DUKKAN ALAMU DAI SUN NUNA MUTUNIYAR KIRKI CE A RAYUWARTA TA BAYA, TO MENENE YASA HAKAN YAKE FARUWA DA ITA? KU KASANCE DA ALKALAMIN FATEEMA ZAHRA DAN JIN YADDA KOMAI YA WAKANA.

Sama ya nufa yana mai shaƙan kamshin air freshener mai bala'in daɗi da yake fitowa daga cikin bedrooms nasu, a ƙage yake da ya shiga cikin ɗakin nasu, ɗakin Ammien ya fara nufa, baki ɗauke da sallama ya shiga, tana zaune saman dadduma ta idar da sallar azahar tana addu'a, ko'ina a cikin ɗakin nan a gyare yake tsab, ga azababben daddaɗar kamshi da kuma sanyin Ac mai ratsa zuciya yana tashi.

Readers Also Read