Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 7
Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 7: Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 7. Cikin natsuwa yake aikin dake gabansa, wato…
3,359 words
Cikin natsuwa yake aikin dake gabansa, wato gyara dark black curly hair sa, tamkar bai san mutun ya shigo cikin ɗakin ba bare har ya yi mashi ɓari, tamkar babu shi a cikin ɗakin, haka ya kasance, amma kuma duk abin da take yi kunsan yana ji tun da shi ba kurma bane.
Tana tsaye a wajen tana kallon kasa ta kasa motsawa, har ya kammala gyaran gashinsa ya shafa Lotion nasa, sannan ya feshe jikinsa da perfume nasa. Bayan ya gama, cikin wannan natsuwa tasa mai ɗaukar hankali ya juyo...........
❤️❤️TRIPLETS❤️❤️
E7-8
Turo bakin nan ta yi kamar biro. "To gwaggo Batula dan ita ta haifi yaya Imran sai ta ce bata son ganina a fitar da nine? To ni dama waye ya ce ma ta so ni? Ni ma ai ba sonta nake yi ba, kuma ba zan zauna ma a gidan nan ba, dan daddy ya taɓa gaya mani she is wicked".
Sosai Hjy Batula ta buge mata baki da ɗan karfi, kuka ta saka masu, har da birgima a kasa, taɓe maki Ammie ta yi tana ganin ikon Allah, wai wannan mahaukaciyar ce matar ɗan ta? Ta tambayi kanta da kanta.
Ita kuwa Aunty a cikin zuciyarta tana jin da ace Mummy Abla ta kyaleta, bata daketa ba, yanzu ga shi ta sake kwaɓe masu komai.
Tsawa Ammie ta daka masu akan su fice mata daga gida tun ransu bai ɓace ba. Waya Hjy Batula ta ciro wayarta ta kira Abbi dan ta sanar da shi abin da yake faruwa, bugu ɗaya ya ɗauki kiran, ba ɓata lokaci ta sanar da shi ga abin da jellyn ta yi, ita kuma Ammie ga reply da ta bata akan ba zata karɓi jelly ɗin ba.
Shiru Abbi ya ɗan yi kafin ya yi magana kasa kasa dan kar daddyn Jelly ya ji, yasan hakinsa sarai idan ya ji zai ɓata rai ya ce an wulaƙanta mashi ƴa, hakan yasa ya yi magana kasa kasa dan zaman lafiya yake so ba faɗa ba, umarni ya yi masu a kan su dawo da jelly ɗin gida, idan suka dawo daga Katsina za su kira Imran, sai su san abin yi.
To ta amsa da shi, ta yi wa Ammie sallama tare da riƙo hannun jellyn ta miƙar da ita suka nufi waje, wani irin matsiyacin kallon banza Ammie ta bisu da shi, sai da suka ƙurewa ganinta ta koma saman sofa ta zauna tare da ɗauko wayarta.
Number Imran ɗin ta fara laluɓa dan ta kirashi, ta bashi umarnin akan idan ma ya auri jelly to ya saketa ko ta tsine mashi albarka, sai dai kash a kashe ta sami number, ta ji babu daɗi sosai, saman sofa ta ɗaura wayar ta cigaba da kallonta.
Su kuma bayan sun je mota, sosai Hjy Batula ta yi wa Jelly faɗa tare da nasiha, ta kara mata da cewa, in dai bata girmama Ammie ba, to tabbas yaya Imran ba zai taɓa sonta ba, zai dai'na kulata, zai yi watsi da ita, domin yana Kaunar mahaifiyarsa shi ma, shiru ta yi tana sauraron Hjy Batula tamkar wata mumina, yadda kasan an mata sauƙar karatun Al Qur'ani mai girma a kanta, tsit ta yi, sai da mummy Abla ta gama nasihar, ta tada mota dan su tafi.
Suna kama hanya ita kuma Aunty ta ɗaura nata nasihar, dan jelly sai an bita a hankali, ta karfi ba zata taɓa yi wu wa ba, idan ka zare mata ido, ita ma zare maka zata yi, bata da tsoro ko kaɗan, ga uban rashin kunya tamkar a kanta a sauƙe shi.
Kai tsaye gida suka koma da ita, tun Hjy Batula bata gama kashe motar ba, jelly ta fito ta wuce ciki abinta, da ido kawai Hjy Batula ta bita da shi, tana mugun tausayawa Imran, gaskiya daddyn Jelly ya yi kuskure, ya biye wa sanyata farinciki ya koya mata ɗabiar da barin shi yanzu ba karamin abu bane, ya biye mata komai take yi baya yi mata faɗa, kawai dan ta yi farinciki, to ga shi dai karshe abin da ya haifar masu, bata ganin kowa da girma sai shi daddyn nata da kuma Imran, shi ma Imran ya ci albarkacin son da take yi mashi ne yasa take ɗan girmama shi, daba dan haka ba, shi ma da a sahun marenan wayonta zata sanya shi. TAB AIKUWA AKWAI GYARA BA KAƊAN BA.
GIDAN ABBA💋
Kwance take a saman gatonta bayan ta gama cin abicnin dare ta yi sallar isha kenan, ba abin da take jira face kiran sahibinta, abun begenta, farincikinta, ta lula can duniyar tunanin masoyin nata, sanye take da kayan barci a jikinta, doguwar riga ce launin pink color, ta sanya hular rigar a kanta, ƴan kwana biyun nan da tana samin kwanciyar hankali, har wani ƴar kiba ta yi.
Karan ringing na wayarta ne ya daki dodan kunnenta, hakan kuma ya yi sanadiyar dawowarta daga duniyar tunanin sahibin nata da ta faɗa, cikin sauri ta duba kiran, abin mamaki kuma abin al'ajabi kiran Irfan ne yau kuma ya shigo wayar tata, sai kuma a lokacin ne ma ta iya tunawa da wani abu wai sun taɓa yin soyayya da Irfan, nan take ta ji jikinta ya mutu, wani irin rashin daɗi ta ji.
Jikinta a sake duk ya mutu, haka ta ɗauki kiran nashi. "Yaya Irfan barka da dare". Dogon numfashi bawan Allah ya ja, tare kuma da sauƙewa a hankali. "Heartbeat ina kika shiga ne? Meyasami wayarki? Nazo gida ban same ki ba". Yadda yake maganar kamar zai yi kuka, abin gwanin ban tausayi, bata san lokacin da hawaye suka fara bin kuncinta ba. "Kayi hakuri yaya Irfan ka ji?" Shi ne kawai abin da ta iya furtawa.
"Bakomai Heartbeat ba dai kina nan lafiya ba?" "E ina nan lafiya fatan kai ma kana cikin ƙoƙarin lafiya?". Nisawa ya yi tare da suake ajiyar zuciya "Heartbeat bana cikin ƙoshin lafiya, ji nake yi kamar zuciyata zata fashe ta fito waje a kwana biyun nan da ban jiki ba, please kada ki sake yi mani hakan kin ji ko?". Hawaye take yi sosai, shin me yake shirin faruwa ne, kenan har yanzu Akila bata san soyayyar gaskiya ba, har yanzu ba zata iya tantance wadda take so da gaske da kuma wadda take so dan wani abu ba? To fa akwai gagarumar matsala wlh.
"Heartbeat ya na ji kin yi shiru?" "Kayi hakuri yaya Irfan". "Heartbeat me ya faru kike kuka kuma, subhanallahi dan Allah ki dai'na Kinji? Idan baki dai'na ba zuciyata zata yi mani ciwo". Hannu tasa tana goge hawayen nata. "Kada zuciyarka ta yi ciwo yaya Irfan, wlh na dai'na, ka gani na goge hawayen".
"Good my heartbeat, to yanzu dai gaya mani menene ya sanyaki kuka ƴar kanwar?". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Kai ne ka sanya ni kuka mana" "Subhanallah ni kuma Heartbeat?" Gyaɗa mashi kai tayi tamkar tana a gabansa. "Ni kuma laifin ne nayi da na sanya matata hawaye? Yau wace iriyar ranan bakin cikice a gareni da na sanya matata kuka da kaina? Duk da ban san laifin da na yi ba, ina rokon da ki yi mani afuwa kin ji matar mijinta?".
Turo ɗan bakin nan nata ta yi. "Ni yaya Irfan ka dai'na magana ka yi shiru na ƴan mintoci tukun nan". Shirun ya yi ya biye mata, dama haka take yi wa masoyin ɓoye wani lokaci, sai ta ce mashi ya yi shiru na minti goma, haka zai yi ta zama shiru yana sauraron sauƙar numfashinta, ta koyo hakan ne kuma daga wajen jelly, jelly ce mai wannan sabon iskancin tun tana yarinya, lokacin da suka je Kano, haka jelly take sanya daddy ya rufe bakinsa, ba yadda ya iya haka yake yin shiru har sai ta ce to lokacin magana ya yi, sai ya fara magana, to shi ne ita ma Akila ta koya, sai ta rinƙa cewa Heartbeat nata ya yi shiru kaɗan, yanzu kuma ga shi ta yi wa Irfan, shima ya ɗana.
Shiru ya yi ta zama har tsawon lokacin da ta ɗeba mashi, kafin ya yi magana, a lokacin kuma ta gama tikar kukanta ta share hawaye. Cigaba da hira suka yi, sun biya bashin tsawon kwanaki da suka ɗauka basa waya, sai misalin karfe 10 ta ce mashi tana jin barci, ba dan yaso ba suka yi sallama bayan ya yi kissing na wayar yana faɗin zai yi kewarta, ita ma kissing na wayar ta yi tana mai kara tabbatar mashi a yanzu ma har ta fara kewarsa, da haka suka yi sallama ba dan sun so ba.
Saman bedside drawer ta ɗaura wayar, sai kuma me? Sabon kuka ta rushe da shi, ita kanta ta bata san dalilin yin kukan nata ba, tamkar wata karamar yarinya haka take tiƙa wannan kuka, while ita kuma Ammie tana can tana cika tana batsewa, ta tasa Abba a gaba a kan lallai sai ya nemo mata Imran a daren nan, duk in da ya shiga, maza Abba ya nemo shi, a cikin daren nan zai rabu da jelly dan uwarsa, mamaki Abba yake yi, kullun idan zata zagesu sai dai ta ce Uwarsu ba dan ubansu ba, Ammie duniya mai zaman kanta.
Har karfe shaɗaya ta buga Akila na kuka, kuka kuma da bashi da dalili. Sai misalin karfe shaɗaya da rabi sannan wadda nake da tabbacin saboda shi take yin wannan kukan ya kirata.
Ƙin ɗaukar kiran ta yi, tamkar ya yi mata wani laifin, ashe dai yasan me ya aikata, dan haka sai shi da kansa ya yi received call ɗin, da kansa kuma ya sarrafa wayar tata, ya kara Volume yadda zata ji shi sosai.
"Am so so sorryyyyyyyyyy my heartbeat, ba zan sake ba, dan Allah ki yi shiru Kinji?" Cigaba da kukanta ta yi tamkar bata ji me ya ce ba.
"Wayyo matata, please amin afuwa, dan Allah ki yi shiru, wlh ba zan sake ba, zan iya jurar komai amma ban da hawayenki".
"Meyasa tun ɗazun baka kirani ba?" Ta faɗa can kasa kasa cikin muryar kuka.
"Kiyi hakuri zafin kishi ne yasa ban kiraki ba, na barine sai zuciyata ta ɗan sauƙa, amma na tuba ba zan sake ba, kuma fa heartbeat harda kissing na wayar ke ma kika yi ko? Amma ba komai yanzu dai daina kukan, shi ne babban abin da ya fi damuna". Turo baki ta yi kamar biro, kasa kasa take kunkuni ta yadda ba zai ji ba, tamkar wata ƴar baby, irin idan aka daki yarinya ta gama kukan nan, irin wannan kunkuni da suke kasa kasa da ƴan surutai, shi ita ma take yi.
Hakan yasa ya saki cool murmushi. "My Heartbeat sarkin rigima, to ko dai sai nazo na goyaki ne?". Lumshe idanu ta yi tana murmushi tare da rufe fuskarta ga hawaye a fuska.
"My heartbeat yau kuma ni ake jin kunya?". Gyaɗa mashi kai kawai ta yi alamar e.
"To shikenan ki cigaba da jin kunya ni bani da wata damu, abin da na sani dai shi ne, a ranar da muka yi aure, a ranar zan cire maki kunyar tas na watsar, yanzu dai duk ba ma wannan ba kin ci abinci?".
"E naci kai fa ka ci ne?" "A'a My Heartbeat, ni ban ci ba, kuma ba zan iya ciba har sai naji voice naki, yanzu zan ɗauko muci tare, kina bani a baki". Kayatatcen murmushi ne ya bayyana a kan fuskarta, ba komai ne kuma ya haifar mata da murmushin nan ba face yadda ya yi maganar, tamkar wani ɗan yaro, ya iya shagwaɓa sosai da sosai.
"My Heartbeat Murmushi yana yi maki bala'in kyau". "To dan Allah nima ina son ganin Murmushinka ka ji Heartbeat ɗina?". A shagwaɓe ta yi maganar.
"My heartbeat na yi maki alkawarin zaki ganni, yau ba alhamis ba?" E ta amsa mashi da shi. "To ranar Wednesday zan kawo maki kaina har gida domin ki ganni da kyau, ki kare mani kallo son ranki, ki ɗaukeni videos, ki yi mani hoto, ki ji murya, kiyi yadda kikeso dani gabaɗaya, amma kuma da sharaɗi!".
"Sharaɗin ne?" Ta faɗa cikin zumuɗi. "Idan nazo gida, ko a gaban waye zan gaya maki ina son ki, sharaɗin shi ne ba zaki gudu cikin gida ba, zaki tsaya mu kalli juna cikin ido, ki zuba mani shagwaɓa, ki yi alkawarin yin hakan, idan ki ka yi alkawarin yin haka, to nima zan yi alkawarin tabbas zanzo".
"Nayi, ba dai alkawari ba? To nayi maka, tabbas ba zan gudu ba, zan tsaya mu sha hira ". Ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ce "Ina nan zuwa my Heartbeat, nima ai nafi son ganinki fuska da fuska, hakan zai fi, yanzu dai tsarabar me kike so na kawo maki?".
"To ai baka gaya mani kasar da kake ba bare na san me da me ne a kasarku har nace ka kawo Mani". "Heartbeat kasarmu ɗaya, a Nigeria nake ai". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Tom tsarabar goriba zaka kawo Mani ". To ya amsa mata da shi.
Mamaki ne ya kamata, wai har da wani cewa to, shi kuma bai kawo komai a ransa ba, ita kuma ta dage shi ba ɗan Nigeria ba ne, shiyasa ta yi mashi wayo dan ya gaya mata kasarsa ta hanyar cewa da ta yi bata san kasarsa ba, bare ta san tsarabar me zai kawo mata, amma ya ce a Naija yake, ta ce goriba ya ce mata to, anya kuwa da gaske yake yi? Anya ya san wannan goriba kuwa? Amma dai zata gani ai, ba dai ranar laraba ya ce ba, to shikenan ai.
Ta nutsa duniyar tunanin can ta tsingayo zazzakar muryarsa kasa kasa yana faɗin "My heartbeat ki zo na baki abinci a baki kin ji ko?". "Ka bari sai ranar Wednesday idan kazo sai ka bani a baki ɗin". "Are you serious?" Tabbatar mashi da hakan ta yi, sosai ya ji daɗi kamar me, suna hira yana cin abinci a nutse, sai wuraren karfe 2 na dare suka yi sallama cike da kewa da kuma masifar kaunar juna, ba dan sun so rabuwa ba, dare ne kawai ya yi, daren ma dan ita yake tausayawa yasa ya hakura, baya son ta kasa tashi tayi sallar asuba.
GIDAN LION💋
Dare misalin karfe 8, Rimsha, Imran, da kuma Areef, suna zaune a palon sama, Areef dai Alhamdulilah jiki ya yi kyau sosai da sosai, waƴan nan shaiɗanun matsafa sun sake shi da karfin ikon Allah, amma anci kwakwa fa, Lion ya sha baƙar wahala ba kaɗan ba, su TGA sun yi nasarar tarwatsa kunjiyar tsafinsu Josephine ɗin, sai dai sun rasa sojoji da dama, ciki kuma harda babban yaron TGA, shi ma TGA ɗin ya ji ciwo sosai a kefen cikinsa, yanzu haka yana gadon asibiti. To sai dai muche Alhadulillah, an gama da shegun matsafa, yanzu Josephine da Areef sun fita daga koma.
Sai hira suke yi cike da kula, da kuma girmama juna, massage Lion ya yi wa Imran akan RIMSHA ta kai mashi abinci, da alama yau ya ji yunwa sosai, bawan Allah yau yasha wahala sosai gaskiya, kawai mutun ba zai taɓa gane hakan a kan face nashi or a yanayinsa bane, domin kuwa kullum a siffa ɗaya yake idan baku mance ba, amma yau saboda waƴan nan ƴan iska matsafa na jikin Areef ya sha wahala over, dan sai da ya yi wa Areef ɗin dannar yankar rago kafin ya samu ya fara yi mashi addua'o'i da karatun Alqur'ani mai girma, ba ƙaramin dambe suka sha ba, Imran kam guduwa ya yi tun da Areef ya maka shi da kasa sau ɗaya, ita kuma Rimsha tana ɗaki tana sallah tana kuka tana riƙon Allah da ya bawa Areef ɗin lafiya.
Yanzu dan ance ta kai mashi abin bata damu ba, dan tana ganin ɗazun sun wanye lafiya, a shirmenta wai ta fara gane me Saif yake so, yarinya yarinya ce, har izu yau TRIPLETS nasa ma sun kasa iya tantance abu guda ɗaya da yake so bayan kaunarsu, sai ita ce wai ta gano me yake so, to fa mu dai je zuwa.
Miƙewa ta yi ta nufi kitchen, binta da kallo Imran ya yi, ciro wayarsa ya yi domin ya kira tailor da ya bawa ɗin kin kayansu, ya ga ji da kallonta da shigar riga da wando, yana tsoron abin da zai je ya dawo, baya son su yi aikin danasani.
Tabbatar mashi tailor ya yi akan tabbas rana ita yau azo a karɓi kayan, to ya amsa da shi kafin su yi sallama, ajiye waya ya yi suka cigaba da hira da Areef.
A cikin zuciyarta ta yi sallama a bakin kofar kitchen ɗin, annabi ya ce katabbatar da kana yin sallama ne a in da aka san darajar sallama, a in da ake amsata, kada ka yi sallama a in da za'a walakanta sallamar, to shi Mark ai bai san darajar Sallama ba, kuma ba amsata zai yi ba, shiyasa take yi a cikin zuciya, karisawa cikin kitchen ɗin ta yi, sannu ta yi mashi, tamkar babu shi a cikin kitchen, kamar dai yadda suka saba, bai ɗago kai daga abin da yake yi ya kalleta ba, haka zalika, bai amsa sannun da ta yi mashi ba, kamar wani mai aljanu, ɗazun ya yi mata magana da bai taɓa yi ba, yanzu kuma ta yi mashi yaki amsawa, to Allah ya shirye shi.
Wucewa ta yi ta wanke hannunta kafin ta ɗauki abin nasa, har lokacin tamkar babu Mark a cikin kitchen ɗin nan, ficewa ta yi abinta, sanye take da wandon jeans baki ya kamata da ga sama har kasa, jikin wandon akwai kyalli sosai farare a jiki, sai ta sama kuma, top mai dogon hannu ta sanya, launin maroon color, ba karamin kyau ta yi ba, kamar kullun hijabin ɗan karami mai taken please call me ne a jikinta, bakin hijabi ne kalar wandon, kafarta na sanye da takalma flat shoe Maroon color, sai tashin kamshi nata perfume ɗin take yi.
Sallama ta yi mashi a bakin kofar ɗakin, yana zaune saman sofa set yana latsa wayarsa, jin ya yi shiru ne yasa ta kutsa kai cikin, tana mai kara kwaɗa wani sallamar.
A wannan karon ma saura kaɗan ta saki tray ɗin abincin saboda razana da kallonsa da ta yi, sai dai Allah yasa ta riƙe abincin da kyau sosai, hakan yasa bai ɓare ba. Sanye yake da kayan barci, wando dogo har kasa, sai riga mai guntun hannu, damatsan hannunsa suka firgitata, domin gajartar hannun rigar ta bayyanar da su a waje, kamar dai kullun kunsan yana tashin wannan fitinannen kamshin nasa, da alama yau barci yake ji da wuri, Shiyasa ya buƙaci abicnin da wuri haka, ga alamar hakan ka a face nasa, sai lumshe idanu yake yi, gashin kansa a kwance, ta zubo mashi a fuska kasancewar ya sunkuyar da kai a kan wayarsa.
A in da ta saba ajiye mashi abin cin, a nan ta ajiye mashi, saboda neman magana irin nata har da wani ce mashi good evening, ai ko tamkar babu shi a cikin ɗakin bai amsa ba.
Ganin hakan yasa kawai ta fara zuba mashi abinci, sai da ta zuba rabi ya sauƙo daga saman sofar ya dawo wajen da yake zama dan cin abincin, ya zauna, abin da ya bata mamaki shi ne kafin ya zauna sai da ya yi bismillahi, tana jiyoshi ya yi kasa kasa, kenan hakan ya nuna duk wasu dokoki da wasu abubuwa da suka danganci addin dan korar shaiɗan a kusa da mutun kenan yana yi, kuma yasan su fa, amma meyasa baya amsa sallama na? Ta tambayi kanta, abin da bata sani ba shi ne, kamar yadda ya yi wannan bismillahi yanzu, to fa haka yake amsa mata sallamarta, sai dai maganar tasa ce idan ba'a kusa da shi sosai kake ba, ba ji zaka yi ba.
Bayan ta gama zuba mashi ta tura mashi abincin a gabansa, ba ɓata lokaci ya ɗauki spoon ya fara cin abincin nasu, wani irin kalar green ne abinci, ita ko kallon abincin ma bata son yi, sai mamaki take yi, abin cin wani gubar wani, su kuma nata abincin ne suke jin ko da me sun yafe cin shi.