Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 79
Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 79: Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 79. Sam daddy ya hanasu wucewa, shi dai ya kafe…
3,373 words
Sam daddy ya hanasu wucewa, shi dai ya kafe lallai baya son bakaken fata, sai da ya ga ran zakunan nasa wato Lion da Areef ya ɓaci, face nasu ta sauya, ya san ba zata yi musu kyau ba, sannan ne ya shafawa kansa ruwan sanyi ya bawa Michael hanya, amma fa ya kuduri niyar wlh sai ya rabasu, dan shi bazai yi mix na jini da kowa ba face ƴan uwansa...... E akwai kura in dai haka ne kam.
Wucewa Aseef ɗin ya yi zuwa bedroom ɗin Lion, a hankali yake tafiya gudun kada ya faɗi, sai shessheƙar kuka Akilar take yi, ita kuma Rimsha tana cikin bedroom nata suna zuba dirama da Jehan a kan zuwa wajen Lion ta yi dare haka, dan jiya a kullace da Rimshar ta yi barci, ta jirata har wajen 11 bata dawo ba har barci ya yi awon gaba da ita, da safe kuma Rimshar ta tafi school basu haɗu ba, dama jiranta take yi ta dawo school sai ta gaya mata uban da take zuwa yi wajensa har dare haka? To shi ne diramar da suke yi, Rimsha dai ta kafe akan ita wlh babu wani abin da take yi bayan kai mishi abinci, ita kuma Jehan ta ce karya take yi munafuka, kai abinci ne sai ta shafe awa huɗu a can, to wlh ba zai yiwu ba, ta shiga hankalinta da kyau idan ba haka ba sai ta yi mata ɗan iskan dukan mutuwa sai dai duk abin da zai faru ya faru.
Da yake ita ma Rimshar akwai zuciyar sai ta ce "Kinga ne Jehan duk wannan magana ba ni zaki yi wa ba, ki je ki sami Yaya Saif ɗin ki gaya mishi, domin shi ne mai tsayar da ni, kuma ni ban isa in ce mishi a'a ba, so kila idan kika yi mishi magana zai ji sai ya dai'na tsayar da ni". "Rimsha ba zan yi mishi magana ba dan bani da wani haɗi da shi! Ke kuma na isa in saka ki kuma in hana ki, wlh idan kika sake wuce minti 30 a wajensa sai ranki ya ɓaci!!". Ta yi maganar cikin fushi da ɓacin rai, dan kuwa abin ya kona mata rai yadda jiya Rimshar ta jima bata dawo ɗaki ba har ta yi barci, wannan ma fa bata san cewa tare a garden ɗin suka kwana ba, ta yi tunanin Rimshar ta dawo cikin dare bayan ta yi barci kenan.
Miƙewa Rimshar ta yi tare da riko hannuta zuwa palon sama, dai'dai lokacin kuma Lion da Areef sun hauro sama bayan sun gama case da daddy Areef ya kai shi masauki, shi ne suka nufo bedroom ɗin Lion ɗin dan su tattauna a tsakaninsu su ukun.
Da hannu Rimsha ta nunawa Jehan ɗin Lion tana faɗin "Wannan shi ne yaya Saif, sai ki gaya mishi ya dai'na rikeni ina jimawa a ɗakinsa". Ko kallon in da suke Lion ɗin bai yi ba ya wuce zuwa kofar bedroom nasa yana knocking a hankali dan Aseef ya rufe kofar da key, ita kuwa Jehan ta sha jinin jikinta sosai ganin Lion, ashe bata ga komai a hoto ba, a zahiri ma kwarjininsa yafi yawa, wani irin azababben tsoronsa ne ya dira mata a ranta, dan kuwa bata ga wajen wasa ba, dan ma ko kallonsu bai yi ba, Areef ne ya tsaya yana tambayarsu me yake faruwa? Ba ɓoye ɓoye Rimshar ta gaya mishi abin da yake faruwa.
Da hannu ya yi wa Rimshar alama a kan ta koma bedroom nata bari ya yi magana da Jehan ɗin, a lokacin kuma Akila ta buɗewa Lion kofar bedroom ɗin ya shige abinsa. Wucewa Rimsha ta yi ta koma ciki, juyawa ita ma Jehan ɗin ta yi da nufin ta koma ciki, da sauri ya riko hannunta yana faɗin "Wai ke meyasa kika cika faɗa da neman rigima ne?". Harara ta watsa mishi tare da fisge hannunta ta juya zuwa ɗakin dan ta je ta jibgi Rimsha akan ta kawota gaban Lion, haka kawai ta sanya ta sai faɗuwar gaba take yi tun da ta ganshi, dan haka ba zata kyaleta ba wlh.
Da sauri ya bi bayanta zuwa cikin ɗakin, dan yanda ya kallin ta juya a fusacen nan yasan tana iya aikata wani abin ga Queen nasu. Dai'dai lokacin da ya shigo ta ɗaga hannu zata mari Rimshar dan fa a fusace take, rike hannun nata ya yi tare da ɗaure fuska sosai cikin nuna isa ya ce.
"Ki natsu ko kuma na nitsar dake yanzun nan". Ganin ya ɗaure fuska ya koma kamar Lion ne dama kuma ga bala'in tsoronsa da take ji, hakan yasa ta natsun kamar yadda ya faɗa, dan kuwa wlh tsab zai iya ajiye soyayya a gefe ya gyara mata kuskure idan ta yi, yana da wasa da dariya ga waƴan da ya ga damar yi da su, amma fa idan ka yi mishi ba dai'dai ba abin da baya so, wlh tsab zai canza maka daga Areef zuwa TRIPLETS ɗin General Of The Army, yanzu zai yi maka hukunci.
"Our Queen jeki zuwa wajen daddy ina zuwa nima yanzu". Ya yi maganar tare da sakin hannun Jehan ɗin ya nuna mata waje saman gefen gadon a kan ta zauna, bata musa mishi ba ta zauna, dan tasan ko daddy ta kaiwa karansa bai wuce ya ce mata yayanta ne ta bi abin da ya ce ba, so is better kawai ta bin ya fi.
"Ba da wasa nake miki ba, idan kika yi kuskure dukan Rimsha serious ko ni ban isa in tare miki wannan faɗar ba, dan idan garin nan kap zasu haɗu bana jin zasu iya tare miki, idan kika ga Lion bai sumar dake ba, to sai dai idan Rimshar ce da kanta ta shiga tsakaninku, ki sani Lion yana da damar yi miki duk hukuncin da ya ga dama idan kika taɓa ta saboda matarsa ce, akwai aure a tsakaninsu, so baki da damar dukanta, bare kuma da hujjar taki ta zama a kan dan ta je wajensa ne, to ki sani mijinta ne, ita kanta bata san mijinta bane, kuma ban ce ki gaya mata ba, ki kyaleta kamar yadda uncle ya ce kada a gaya mata, abin da yasa kema na gaya miki, dan ba zan iya juran wani abin ya same ki bane, na san in dai kika taɓata a yadda Lion yake yanzu sonta na ɗawainiya da shi ba tare da ya sani ba, tsab zai iya yi miki illah, ba zan iya juran hakan ba ni kuma shiyasa kawai na gaya miki, tun wuri ma ki sani, dan haka ki cire idanunki a kansu babu ruwanki da su".
Hakika ta tsorata da jin cewa akwai aure a kan Rimsha, abin ya girgiza ta, to ya akayi hakan ta faru? Ta tambayi kanta, lallai kuwa abin da mamaki, baiwar Allah Rimsha ita bata ma sani ba, ga shi daddy ya ce kada a gaya mata, ko meyasa ya ce hakan? Ta sake tambayar kanta.
Ganin ta shiga duniyar tunani ne yasa ya hura mata iskar bakinsa a fuska yana faɗin "Faɗa mini ke kuma yaushe kike son muyi aure?". Kallon uku goma ta wurga mishi kafin ta ce "Me kuma aure? Sunan wani abinci ne? Idan ma abinci ne bana ci, dan daga jin sunan abincin ba zai yi daɗi ba".
Da yake shi ma ɗan yi ne sai ya matso kusa da ita sosai, kasa kasa kamar mai raɗa ya fara magana "Yes sunan abinci ne aure, abinci kuma mai daɗi ma kuwa, kuma ko zaki yi yaya sai kinci, kuma ni zan baki da hannuna, dan haka ki fara shirin aure tun yanzu, bari dai Lion ya je lafiya ya dawo lafiya, daga nan sai aurenmu, yanzu bani da kwanciyar hankali yin aure har sai ɗan uwana ya dawo lafiya, ji wani ɗan bakinta a wajen, zaki ga abinci ne iya ganin idonki masifaffa mafaɗaciya kawai, Allah ko har na hangoki kina goye da baby'sna a bayanki, zakuwa ki yi matukar kyau da hakan, Allah ya sanya ki haifi 5 baby's lokaci guda, dan ni ina matukar son baby's Lion ne baya so, shi ma kawai dan baya son hayaniya ne, amma nasan idan baby's nasa ne dole zai so a nawa tunanin".
Miƙewa ta yi dan ta lura Areef fa ya fita iya iskanci, duk wani mannin haukarta to ya ninkata, ko da me ta zo wlh ya fita, Hmmm ga shi Bature babu kunya ko ɗigo a lamuransu, bugu da kari ya yi rayuwa waje daban daban, ai dole ma taga abin da ya minka haka, idan bata yi hankali ba ma ta biye mishi suna magana, wlh watara sai ya gaya mata abin da yafi karfin ƙwaƙwalwarta, rufin asirinta ɗaya idan yana magana ta yi shiru, idan ba haka ba, duk wani amsa da zata bashi, yadda zai fassara shi daban, dan sai ya kara gishiri da su maggi, ya tsara kalmar da kyau kafin ya bata amsa wanda zai sanyata yin shiru bata shirya ba, ga shegen iya magana a wajensa na wuce misali, kai a takaice komai ya haɗa, idan shiru shiru ne ma tsab zaka samu a wajensa, dan wlh bashi da magana sai da waƴan da yaga dama, maganar tasa ta ganin dama ce, wani lokaci ko da Aseef idan bai ga dama ba baya tanka mishi magana idan yana yi mishi, shi ɗan naga dama ne over.
Ganin ta miƙene yasa shi ma ya miƙe yana faɗin "Jiba idanunta a wajen kamar na Aseef, sai ka ce ball, amma suna mugun yi mini kyau fa". Ko sannu bata ce mishi ba ta nufi waje dan ta je wajen daddynta, rufa mata baya ya yi yana faɗin "Wow baby ko ta baya ma ke haɗaɗɗiya ce, gaskiya kin iya tafiya fa, see beautiful shape!" Tsayawa ta yi ta fasa tafiyar haushi kamar ta shake mishi wuya ta yi ta kifa mishi maruka a wannan jajir ɗin kumatun nasa ko zata huce, ashe dama tafiyarta yake kallo dan iskanci, wannan mutumin ɗan iska ne gaskiya, ta faɗa a cikin zuciyarta tana wani zabga mishi harara.
Shi kuwa murmushi ya sakar mata yana jin wani irin tsantsar nishaɗi idan yana tsokanar ta, da gangan ya ce mata hakan dan kawai yaga tana hararsa tana juya dara daran fararen idanun nan nata, ba ƙaramin tafiya da imaninsa suke yi ba idan tana hararsa, so yana ɗaya daga cikin dalilan da yasa yake yawan tsokanarta, da hararar.
"Mu je mana". Ya faɗa yana karewa kirjinta kallo, ga shi babu hijabi a jikinta, daga ita sai doguwar rigar abaya, sai dai ita tana sanya breziya, yanzu ma ta yi amfani da guda ɗaya cikin wanda Akila ta taɓa ɗaukawa Rimsha lokacin da Imran ya kaisu shopping, Rimsha bata taɓa bi ta kansu ba, dan bata sakawa, da vest kawai take amfani, amma ita tana sanyawa dan breast nata sun ciko sosai, dama kun san tana da halittarsu sosai ita ma, so shiyasa take sakawa, hakan kuma ba ƙaramin kyau ya kara mata ba, ya kara bayyanar mata da shape nata, bata sanya ɗankwali ba, dan idan baku manta ba Jehan bata son ɗankwali sai idan ya zama dole, idan baku manta ba kullum faɗarta da mummy kenan a kan ɗankwali, so yanzu ma ta saki kyakkywar gashin nata ba ta ɗaure ba.
Ganin yana karewa kirjinta kallo ne yasa bata da zaɓi dole ta cigaba da tafiya dan ta gujewa kallon da yake yi mata ɗin, cool murmushi ya saki yana mai jin tsantsar kaunarta har cikin ransa, yana son ƴar diramar nan tasa so na wuce misali.
Rufa mata baya ya yi har zuwa bedroom ɗin daddy. Daddy da Rimsha suna saman bed suna hira, yana zaune Rimsha ta tada kai da cikyarsa. Da sauri ta haye gadon tana faɗin Rimsha ta tashi mata bari ta kwanta idan ya so ita kuma sai ta kwanta ta kafofin daddyn, yau ga karfin hali.
Juyowa Rimshar ta yi ta rungumi daddyn tana faɗi wlh bazata tashi ba, ai ko addinin musulunci ya yi hani da ka sami mutun a waje yana zaune ka ce ya tashi ka zauna, koda kuwa ka girme shi to bai kamata ka tashe shi ba, yin hakan zalinci ne, addinin musulunci kuma baya goyon bayan zalunci, ya yi hani da shi, kuma ya tsawatar da babbar murya, dan haka ita gaskiya bazata tashi ba dan magana ake ta addini bata girma ba.
A kule ta ce "To sarkin wa'azi, ban nemi ki yi mini wa'azi a nan ba, dan haka ni ki tashi ko kuma wlh naja kafarki ya yasar dake a kasa, dama can ai ni nake kwanciya a cinyar daddy da Gwaggo, ke kuma mummy wata rana ki haɗa da Gwaggo, dan haka wlh ki tashi tun wuri". Shi dai daddy sai murmushi yake yi abinsa, wato har yanzu da suka girma ma ba zasu dai'na wannan faɗar ba, abu tun suna yara, kamar wasu tom and Jerry. Kai uba mai daɗi kenan, Allah ka sakawa iyayenmu da gidan aljanna.
Hayewa saman gadon shi ma ya yi yana faɗin "Our Queen maza tashi ki bani waje dan dukkanku yanzu ba kafarku ba ne, nawa ne ni kaɗai". Ba musu ta miƙe ta bashi waje, kwanciya ya yi abinsa, shafa lallausan gashinsa daddyn ya fara yi suka fara zuba hira, miƙewa Rimshar ta yi ta nufi waje abinta dan ta leƙo masoyinta tana kewarsa.
Ita kuma Jehan haushi kamar ta kifawa Areef ɗin mari, haka ta matso ta kwantar da kanta a kafaɗar daddyn tana turo baki, daddy dai yana ganin ikon Allah wajen ƴan diramar nan tasa, wato Areef da Jehan sai Allah, yanzu da gangan ya ce zai kwanta a cinyar daddyn dan yaga ta ce zata kwanta, saboda neman tsokana ya wani haye ya kwanta, sam ya manta magana zasu yi da Lion da Aseef, ya zo yana ta neman tsokanar Jehan.
A ɓangaren su Aseef kuwa, lokacin da suka shiga bedroom ɗin na Lion, saman bed ya haye tare da sakin Akilar yana mai cigaba da yi mata sannu, saman bedside drawer ta zauna tana ɓoye fuska dan bata son ganinsa ba riga, wani irin kunyarsa take ji, sosai ya lura da hakan, sai ya ce ta zo.
Ba musu ta haye saman bed ɗin, jawota saman kirjin nasa ya yi yana faɗin "Kunyar kallon mijinki a haka kike ji?". Gyaɗa mishi kai ta yi tana sake ɓoye fuska, "Au kin manta cewa kafin muyi aure kin yi alkawarin zaki yi mini wanka kuma tare zamu rinƙa yi dake kullum ne?". Dukan wasa ta kai mishi a kirjin nasa, cikin tsantsar shagwaɓa ta fara magana kasa kasa kamar mai raɗa.
"To ai ba yanzu ba, sai gaba". Kai tsaye ya ce mata "Sai nayi disvirgin naki?". Zaro idanu ta yi tana mamakin rashin kunya irin tasu, wai su kwata kwata basu san kunya ba, magana sam bata yi musu nauyin faɗa?
(Ni kuwa nace ai Aseef ma mai sauki ne yana da ɗan sauran nasa kunya da kika koya mishi, rashin kunya ai sai Lion da Areef)
"Baki bani amsa ba?". Ya yi maganar yana ɗago haɓarta dan su fiskancin juna, shiru ta yi tare da rufe idanunta dan har ga Allah bata da amsar da zata bashi, ya sanya ma ta kara jin kunyarsa sosai.
"In dai sai nayi disvirgin naki ne zaki fara yi mini soyayyar da kika faɗa to ni gaskiya dole yau zan yi hakan". Ya yi maganar a shagwaɓe sosai, wasa ta fara yi da yatsunta a saman kirjin nasa tana turo baki tare da faɗin "Ni dai Heartbeat ka dai'na faɗin haka dan Allah, Allah bana so". "Bakin so me?" Ya tambaya yana ɗan kama hannun nata ya mayar saman breast nasa.
"Maganar da kake yi mana, bana so ka bari". "Baki son nayi disvirgin naki?". Gyaɗa mishi kai ta yi alamar e, "Why to?" Babu komai ta bashi amsa, "Serious?" Ya yi maganar cikin wata iriyar murya dake nuna tsantar tsokana ta masoya, jinjina mishi kai ta yi almar e da gaske take yi.
"Tom shikenan naji ba zan yi yau ba, amma gaba zanyi idan na sami lafiya, dan gaskiya ba zan iya kyaleki ba, ina son in karɓi virgin ɗina sosai". Yatsa ta ɗaura a saman lips nasa alamar ya yi shiru, ta yi hakan tana gyara kwanciyar a jikin nasa da kyau, ɗan bakin nasa ya buɗe tare da capko yatsar nata ya fara ɗan ciza a hankali yana shafa bayanta har zuwa kumatunta in da ta sha marin daddy.
"Am so sorry my rigimati". Ya faɗa tare da cire yatsar tata daga bakin nasa, nisawa ta yi kafin ta ce mishi babu komai ai daddynsa tamkar daddynta yake, so yana da damar da zai iya dukanta kamar yanda zai dake shi shi ma, dan haka kada ya damu ita ta yafewa daddyn tun lokacin.
Rungumeta ya yi sosai yana mai jin tsantar farinciki tare da jin wani azababben kaunarta yana kara ratsa shi, ita ma rungume shi ta yi tana murmushi.
"Can I kiss you?". Ya yi mata maganar cikin raɗa a kunne, ɗan ɗagowa ta yi suna kallon juna, zubawa lips nasa idanu ta yi, sun kara ja sosai alamar ya ɗan cizasu saboda daɗin rungumarsa da ta yi. Gera ɗaya ya ɗaga mata yana faɗin "Do you love it?" Ya yi maganar yana nuna mata lips ɗin nasa.
Kai ta gyaɗa mishi alamar e tana son lips ɗin nasa, dan ba karya suna da kyau sosai, akwai abubuwa da ya kasace a jikin TRIPLETS iri ɗaya ne sak babu banbanci, ciki har da kafarsu, lips nasu da sauransu, dama kunsan dole a sami hakan dan mahaifa ɗaya ba wasa ba, hakan yasa duk wanda ya gansu sai ya ji lips nasu ya burge shi, dan fa ba karya akwai kyau, shiyasa Rimsha take yawan kallon na Lion, sai dai ita fa Rimsha na Lion ɗin ne kawai yake burgeta, bata taɓa ɗaga ido ta kalli na TRIPLETS nasa ba, ita dai nasa kawai. SO KENAN, NA KOWA BAYA BURGETA SAI NASA, YANZU KUMA SUN ZAMA MALLAKINTA BA TARE DA TA SANI BA.
Yana ƙoƙarin fara kissing nata Lion ya yi musu knocking na kofar, sauka gadon ta yi ta je ta buɗe mishi, ko kallon in da take bai yi ba ya shige cikin ɗakin, bayansa ta biyo ta zo ta zauna a saman bedside drawer.
"Kai my rigimati, ni kizo ki kwanta a jikina kamar ɗazun hai". Ya yi maganar a shagwaɓe, ɗan satar kallon Lion dake ƙoƙarin fito da A box daga mazauninsa ta yi, kafin ta grigiza mishi kai alamar a'a bazata zo ba tun da Lion yana nan.
Kukan shagwaɓa ya saka mata yana faɗin "Wai ke meyasa kike yin wannan abin ne? Ni fa bana son wannan kunyar". Shiru ta yi bata yi magana ba. A gefensa Lion ɗin ya zauna tare da fara duba shi bai ce musu ko sannu ba, dan shi bashi ne a gabansa ba, lafiyar ɗan uwan nasa ne a gabansa, shi ne abin da ya fi damunsa.
Haka suka kasance har ya kammala duba shi tare da yi mishi alluran barci sannan ya miƙe ya fice gabaɗaya daga bedroom ɗin ya koma garden dan ya kwanta ya huta. Yana fita ita ma ta haye saman bed ɗin kusa da mijin nata ta kwanta, dan tana tsoron ta koma bedroom nasu daddy ya sake dawowa.
💋AFTER SOME HOURS❤️
Da misalin karfe 8 na dare, taci wankanta ta tsara kwalliya kamar me, ta yi kyau sosai, sai tashin kamshi take yi, yau barci take ji sosai saboda ta gaji, ga shi gobe akwai school zasu yi Exams na karshe, jibi partynsu, dan haka sai ta sanya kayan barcinta riga da wando launin white color masu masifan kyau, akan idan ta dawo daga wajen Lion kawai ta kwanta abinta ba sai ta tsaya shiri ba, kayan barcin jikinsu yana da tsantsi sosai ga laushi, hijabi har zuwa gwiwarta ta ɗauko ta sanya a jikin nata tare da kara fesa perfume nata sannan ta fito ta nufi kitchen dan ta ɗauki abincin Lion ta kai mishi, ita kuma Jehan tana wajen daddy suna hira, Aseef ya koma bedroom nasa shi da Heartbeat, Areef yana bedroom ɗin daddynsa suna hira.