Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 90
Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 90: Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 90. Gabaɗaya ɗakin jikinsu ya yi sanyi, daddyn…
3,346 words
Gabaɗaya ɗakin jikinsu ya yi sanyi, daddyn Rimsha da yake ta ƙoƙarin ya ga sun yafe wa mahaifiyar tasu dan a nashi hangen ba ita ce mai laifi ba daddynsu ne da laifi, amma sai ga shi yau kuma ta yi wani abin da duk mai hankali ya san me hakan yake nufi, kenan da gaske tana tsafi? Kenan ba kungiyar matsafa ɗaya ta shiga ba ne ko ya ya abin yake? Wannan chain da aka cire a wuyar Akila chain ne mai matuƙar haɗari, yana haɗe ne da guba mai karfin da samun maganinsa yana da matuƙar wahala a duniya, sannan an tsafe chain ɗin sosai ta yanda ba wan da zai ga ne cewa na tsafi ne, Aseef ya taɓa chain ɗin har ya ɗaura mata a wuya lokacin da zasu fita zuwa wajen cin abinci, amma lafiya lou ya ci abincin ba tare da wata tangarɗa ba, ita kuma ɗan shafa chain ɗin da ta yi tana ta cewa ya yi kyau ya yi kyau tana yaba kyautar surukar tata tana murmushi, shi ne musabbabin kunnuwar gubar dan dama saboda ita aka yi shi, dalilin kenan da ya sa tana fara cin abincin poison ɗin ya hau kanta ta fara fitar da kumfa, dan ita jinin Hajiya Umaiya ce ma yasa abin bai yi mata kaca kaca lokaci guda ba, da su Rimsha ne izuwa yanzu namar jikinsu ma sai ya zama green color saboda karfi gubar nan haɗe da tsafi, ba sai na gaya muku ba, kun san jinin Hajiya Umaiya baya taɓuwa, yanzu ma dan abin mai bala'in karfi ne yasa ya jijjiga Akilar har haka, amma babu wani ciwo da ya ji mata daga ta ciki, babban nasarar da suka yi kuma lokacin da ta faɗi tana fitar da kumfa a palo, sai ya zamana Aseef ɗin ne kawai ya ɗauketa, daddyn Rimsha ya taɓata lokacin da suka shigo da ita ɗaki, amma shi saboda ya yi askar na safe sai abin bai shafe shi ba, an yi sa'a Jehan bata taɓa ta ba, da wlh sai gawa, su dai jinin William ɗin su suka taɓa ta, shiyasa duk abin bai kama su ba, dan ba dan su aka haɗa ba, dan bakaƙen fata dake kewaye da su aka yi.
Jugum jugum suka zauna a cikin ɗakin, shi kuma daddynsu Lion ya koma wajenta dan ya cigaba da bata kulawa, duk wannan abin da suke yi Aseef yana kwance idanunsa biyu, amma ko motsi baya yi, daddyn Rimsha ya tsorata sosai, tunaninsa kuma damuwarsa ɗaya shi ne Allah yasa kada su ja ƙwaƙwalwar Aseef ta koma kamar ta baya, sai tayarwa da bawan Allah hankali suke yi, suna jefa shi cikin masifa da bala'i, lokacin aurensa da Akila ya sha dakyar bawan Allah nan, yanzu kuma sun sake jefa shi cikin masifar da ta fi ta baya, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, a garin haukarsu na cewa basu son bakaƙen fata ga shi zasu kashe ƴaƴan nasu da kansu, dan kuwa a ƴanda TRIPLETS suke a yanzu, wlh duk wanda aka ce ta mutu daga cikin matansu, to fa sai ta Allah da wuya idan suma basu mutu ba ko wani abin ya same su, dan fa sun kamu da muguwar soyayya mara jin magana, bata sauraron maganar kowa sai na masoyan nasu, fatan mu dai Allah yasa waƴan nan masu jajayen kunnuwa su gane gaskiya su hakura kawai su kyale TRIPLETS da farincikinsu wato matansu. Sai addua'o'i daddyn Rimsha yake tofa Aseef ɗin, amma ko motsi bai yi ba, kuma idanunsa biyu yana kallon kowa a cikin ɗakin, yanzu ma sam ya dai'na hawayen da yake yi tamkar ba shi ba, sai dai jawur ɗin da idanun nasa suka yi kamar wuta ne zai nuna maka yana cikin tsananin tashin hankali.
Areef yana fita waje Lion ya ce mishi "Ka bani amsar tambayar da na yi maka, meyasa kake magana da ita?". "Nothing kawai dai ina so ne naga ko da ba zan je kusa da ita ba, in rinƙa kiranta a waya mu gaisa, in kuma ji idan tana buƙatar wani abin, shi ne kawai yasa nake kiranta". "To meyasa ka gaya mata Aseef ya yi aure?".
Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Seriously Lion ban gaya mata Aseef ya yi aure ba, ba mu yin irin wannan hirar da ita, gaisawa kawai muke yi sai in tambayeta ko tana bukatar wani abin, amma ana gobe su dad zasu zo Nigeria ta ce mini zata bawa John gift ya kawowa matan da zamu aura a matsayinta na suruka, ni ban tambayeta waye ya gaya mata zamu yi aure ba, dan ban cika jan magana da ita ba, ban kuma ce mata a'a ba, sai na ce mata to kawai zan gayawa John ɗin ya je ya karɓa, bayan mun gama magana da ita na sanar da TGA ya ce da John ya je New York ya karɓo mini saƙon, so ni daga nan na fita harkarsu, ban san ya karɓa ko bai karɓa ba, ban san ya suka yi ba, ban kuma san menene ta ba shi ba, so ban san ya aka yi ya bawa matar Aseef ba".
Nisawa Lion ɗin ya yi kafin ya ce da Rimsha dake kwance a jikinsa "Ina kyautar da John ya baki?" Ɗan ɗago kai ta yi tare da yin shiru tamkar mai tunani dan ita ta manta ma da in da ta ajiye abin. Zuba mata idanu suka yi daga shi har Areef ɗin suna kallonta, wani irin giyar soyayyarta ne take kara fusgar Lion, musamman da ta ɗaga dara daran idanun nan nata sama tana tunanin in da ta ajiye chain ɗin, hakan ba ƙaramin tafiya da imaninsa over ya yi ba.
"Sister kin manta da ni ko?" Cewar Areef, sauko da idanunta a kansa ta yi tana ƙoƙarin yin magana Lion ya rufe mata baki yana faɗin ta bashi amsar abin da ya tambayeta first tukun nan. "Yaya Saif kyautar da John ya bani fa ina ga yana gida cikin drawer kayanmu, dan zan tafi school ne da safe ya bani, sai na kai ɗakinmu na ajiye na tafi, daga school kuma sai nan muka zo ai, so yana cikin drawer". "Da ke da waye ya bamawa?".
Kwantar da kanta a saman kinjin nasa ta yi tana faɗin "Lokacin ni da Jehan ne kawai a palon saman, ya bawa Jehan ɗin ta ce bata buƙata, na ce ta karɓa mana ta ajiye ta ce mini bata yi ra'ayi ba kuma ba zata karɓa ba, shi ne ni na karɓa dukka biyun har da natan a kan idan na dawo daga school zan lallaɓata ta karɓa".
Nauyayyar ajiyar zuciya Areef ya sauke, shi dai masifar Jehan ta yi mishi rana ato, shiyasa yake bala'in son masifar nan tata, dan kuwa tana tsare kanta daga shiga bala'i sosai, da yanzu irin Rimshar ce ita, ai da ta karɓa ta koma ɗaki ta buɗe kwalin ta ciro shi ta saka a wuyarta, ai da tana ciro shi ma zata zube kasa kafin a kawo mata wani taimako ta mutu, amma sai Allah yasa ita ɗin ba komai ne take kulawa ba, wannan abin ya yi mishi daɗi, ya ji ya kara sonta sosai, wlh da Rimsha ba school zata tafi a lokacin ba, da tsab zata je ɗaki ta buɗe kwalin ta cirosu dan ta ga menene a ciki ki, kai Jehan duniya ce, mace mai jan aji da tsare gida da halin ko in kula ga masifa da faɗa ma ta yi a rayuwar nan, musamman irin ita Jehan ɗin da idan ka iya zama da ita zaku zauna lafiya, raini ne bata so, bazata shiga harkar ka ba, kai ma kada ka shiga tata, abin da yasa kenan bata karɓi kyautar John ɗin ba, saboda a cewarta babu wani abin da masu jajayen kunnuwar nan zasu bata da bata da shi, ita tafi karfin wani ma ya yi mata kyauta, bare ma yanda suke dirama da Areef ai ba zata karɓa ba dama.
"Areef sai ka je ka ɗauki chain ɗin dukka biyu ka haɗa dana matar Aseef ɗin ka kai mini bedroom na sai na dawo, na gaji da wannan bala'i na daddy da mummy, amma bari na dawo duk sai na yi maganinsu, ka ajiye komai yanda ya dace sannan ka kwantar da case ɗin sai na dawo, ka da ka sake kiranta a waya kuma daga yau, za mu yi waya anjuma!!". Okey ya amsa mishi da shi, sannan suka yi sallama.
Cikin shagwaɓa ta ce "Yaya Areef wato ma katse kiran ka zaka yi ko? Ina jiran ku gama magana shi ne har da cewa yaya Saif sai anjuma kenan?". Tana magana har da turo baki, "Sorry our Queen, ai naga kamar baki tare da ni ne shiyasa na ce bari na barki sai kin sauko ki ɗauki wayarki". Areef sarkin iya magana a dunkule, nan ma magana ya gaya mata daga ita har Lion ɗin, dan Lion ne ya ce mishi zasu yi waya anjima abin da bai taɓa ce mishi ba, hakan na nufin yanzu lokacin matarsa ce kenan, ita kuma ta wani lafe a saman kirjin mijin nata tana wasa da yatsun hannunsa ta ce wai zata yi magana da shi, lallai sun raina mishi wayo nema, shi ne ya yi musu magana a dunkule, wai sai ta sauko ma'ana sai sun dawo cikin hayyacinsu sai ta neme shi, kai Areef ba dai iya magana da sa ido ba.
"Kai yaya Areef ɗazun fa na yi maka magana". Miƙa mata wayar Lion ya yi tare da sauketa daga jikinsa ya miƙe ya nufi waje, dan hiran Areef da Rimsha sai su, so yana son ya yi magana da sojojinsa. Shigewa cikin bargo ta yi suka fara zuba hira da Areef ɗin, yana magana yana nufar bedroom nasu dan ya je ya kwaso chains ɗin.
Yana shiga ita kuma Jehan tana fitowa, ta sha wanka fes tamkar ba ita ce ya gama ruwan hawaye ɗazun a ɗakin Aseef wajen Akila ba, ta shirya cikin wani shegen dogon riga mai bala'in kyau launin pink color, ta yafo mayafinsa a kanta, kyau iya kyau ta yi, bata yin make up, saboda su natural beauty ke garesu ita da Rimsha, halittar idanunsu ma tamkar waƴan da suka sa kwalli, lips nasu pink color ne sosai irin na Naurat, gashin gerarsu tamkar an zana, ga dogon hanci har baka, kyakyawan kuma bakin saje kwance musu a gefe da gefen fuskarsu, to me zasu kara a face ɗin nasu? Ai babu, komai normal ne.
Tare mata hanya ya yi yana tambayarta da ta yi wannan uban kyau haka ina zata je, ko sannu bata ce mishi ba, ɗaure fuska sosai ya yi dan kishinsa ta motsa shi ma, ta zauna ya yi irin wannan haɗuwa haka kuma ta ce zata fita yana tambayarta ba zata ba shi amsa ba, to wlh bata isa ba, cikin nuna isa ya ce ina zata je?!.
Jin yanda ya yi maganar babu wasa a lamuransa ne yasa ta ɗago ta kalle shi, wani irin dukan uku uku kirjinta ya yi ganin ya ɗaure fuska sosai, cikin sanyin murya ta ce "Zan je ne daddy ya kaini wajen yin lalle da gyaran jiki". Tana magana tana turo ɗan bakin kamar wanda aka sanya magana dole.
Katse wayar da suke yi da Rimsha ya yi tare da gyara tsayuwarsa a bakin kofar yana kare mata kallo. "Malam ka bani hanya na wuce". Duk in zata yi magana da shi bata taɓa kallon cikin idanunsa ta gaya mishi magana, a'a tana kallon kasa take duk wannan rashin kunya da take yi mishi, bata da kwarin gwiwar iya kallon cikin idanunsa.
"Please kada ki yi lallen kin ji ko? Wlh dukkanmu TRIPLETS ba mu kaunar wannan abin ko kaɗan, idan kika yi zan yi amai sosai, akan hakan kuma ranar Saif ya yi wa sisterta mummunar hukunci, dan ta yi lalle, haka Allah ya yi mu, kyama yake bamu sosai da sosai".
Kallon sama da kasa ta yi mashi kafin ta ce "To ni dama ina ruwana da ku? Ko dai ina da wani relationship da kai ne? Ni dan Allah bani hanya na wuce hai, kada ku so lalle dan Allah" A karshen maganar tata sai ta yi da Hausa yanda ba zai ji ba, ta ce "Ai ko dan na ganka cikin bakin ciki, wlh dole sai na yi lalle, ba dai yau na ji abin da baka so ba? To kana tsaka mai wuya, lalle kullum ba fashi, iskancin banza dana wufi, ba Saif ba zan ga uban da ya isa ya hukuntani a gidan nan dan na yi lalle". Ta kai karshen maganar tana jan tsaki tare da raɓawa gefensa ta nufi hanyar fita daga ɗakin.
Cikin sauri ya sha gabanta yana faɗin "Seriously i can't believe it gaskiya, ki ajiye zancen lallen nan dan ba zan yarda ba, in fact baza ma ki fita ba".
"Wai kai uban me muka haɗa da kai ne da kake addabawa rayuwata? Me na tare maka? Meyasa sai ni kaɗai ka takurawa a duk waƴan da suke cikin gidan nan?".
"Because I love you mana, shiyasa nake takura miki, kuma ba zan daina ba har sai ranar da kema kika furta mini kalmar you love me, idan kuma kika ki, to for sure za'a ɗaura auren mu this week, ni wlh na fi karfin ma naje neman aure, sai dai nasa a ɗauko mini yarinya a kawo mini ita, ni kuma na turawa babanta sadaki tare da bawa Sultan umarni akan ya ɗaura auren kawai, amma ke abin da yasa nake binki a hankali, saboda kaunarki nake yi ba so ba, kuma saboda ke ƴar uncle ce, dole nayi abin da zai sanya uncle na farinciki, amma ban da haka wlh nafi karfin neman soyayyar mace!".
"To dama waye ya kiraka a nan? Ba sai ka kara gaba ka nemi wata matar ba, ni dai ma ce bana.....". Ta kasa karisa maganar saboda nauyi da kalmar ta yi mata, a kullum mummynsu tana ja musu kunne a kan su tinkari mutun baki da baki su ce basu son shi, saboda ɗan adam ba abin yarda bane, zuciya bata da kashi, karya ne a duniya ka ce kasan mutum 100, hakan ba zai yiwu ba, ka dai san abin da ya yi niya ka sani dangane da shi, amma mutum shi kaɗai yasan zuciyarsa ya san wanene shi, so kuskure ne babba ka ce da mutum baka son shi a gaban idanunsa, baka san me zai iya aikata maka ba, ko a bayan idanunsa ma bai kamata ka faɗa ba, dan maganar tana iya koma mishi, idan baka son shi sai ka bar abin a ranka kai kaɗai kada ka kuskura ka gayawa wata or wani, Allah kasa mu dace.
"Meyasa baki karisa maganar ba?". Ya tambaya yana matsowa kusa da ita, shiru ta yi bata ba shi amsa ba. "Jehan ni fa wannan faɗar ta ki ma kara saka mini kaunarki yake yi a cikin zuciyata". A duk lokacin da furta kalmar sunan Jehan, har cikin ranta take jin sunan, ya iya kira tamkar a bakinsa aka halicci sunan, idan ya kira har wani sanyi take ji a zuciyarta, sai dai kuma bai cika kiran sunan ba, sai idan zai yi mata magana serious ba wasa ba, shi ne zai ambaci sunan dan ya san idan ya ambata, zata natsu ta bashi hankalinta.
(Bari mu bar waƴan nan ƴan diramar mu je mu leƙa su Meesha mu dawo, kafin nan kila Jehan ta tafi wajen lalle, dan fa ta ce sai ta yi🤣 ana life a TRIPLETS wlh, yau abin nema ya samu, Jehan ta gano abin da Areef baya so, Malam Areef ka shiga uku👊🤣🤣 zamu dawo nan da ƴan mintoci, dalili tasa dole mu bar wajen nasu yanzu.)
Lion yana fita daga cikin bedroom ɗin nasu ya ci karo da Mark dake zaune saman chair dake kusa da bedroom ɗin nasu ya yi shiru, bawan Allah Brady ya kwace mishi waya ya kai wa Rimsha. Ko kallon in da yake Lion ɗin bai yi ba ya wuce wajen sauran sojojin dan ya yi magana da su, ita kuma Rimsha ta kwanta tana ta yi mishi taɓe taɓe a wayar tasa, Brady ya koma saman table yana cinye abincin da ta gudu ta bari, ga wayar Mark a saman table ɗin, ɗan kaniyar kare bai mayar mishi ba, yabar Mark ɗin a cikin tunani.
A haka Lion ya shigo ya samesu, sam bata san da Bradyn a cikin ɗakin ba, a tunaninta ya bi Lion, cikin harshen Spanish ya ce da Bradyn ya ɗauki wayar Mark ya mayar mishi da kayansa, haushi ya ɗan yi alamar amsawa kenan kafin ya ɗauki wayar da sauri ya nufi waje.
Shi kuma Lion saman bed ɗin ya hau tare da sanya hannu ya karɓi wayarsa, hotonsa take ta faman kallo abinta, hannu tasa ta rufe idanunta tana murmushi, ta ji kunya ya kamata tana kallon hotonsa a karo na biyu kenan yau kawai. Yatsa ɗaya ya sanya mata a ciki dimple nata da suka lotsa yana kallon ɗan bakinta da take zuba murmushi, ga fararen hakwaranta da suke tas tamkar audiga, kamar bata taɓa cin wani abin ba saboda haskensu.
Shiru suka yi almost 5 mins a haka kafin ta ɗan zame hannun nata a hankali ta buɗe idanunta ta saci kallon shi, karaf suka haɗa idanu, da sauri ta mayar da hannayenta dukka biyu a saman face ɗin nata tana cigaba da murmushi, hannu ɗaya ya kai ya zame hannun nata yana faɗin ta buɗe idanu.
Turo baki ta yi tana faɗin "Yaya Saif Allah kunyarka nake ji, ni ba zan iya buɗe idanuna na kalli cikin naka ba". Sunan kunyar ma yau ya fara jinta, dan haka sai ya ɗaura hannunsa a saman lallausan kumatunta tare da rankwafowa kanta yana faɗin "Open your eyes i said". Tamkar zata yi kuka ta waro idanun nata waje tana turo baki kamar biro, yaya Saif ɗin nan nata ya cika takurawa mutun, a cewarta.
Zubawa laɓɓansa idanu ta yi tana kallon yanda suka yi ja sosai, shi kuma ya zuba nata idanu ido yana kallon kwayar idanunta, kiran sallar da wayarsa ta fara yi ne yasa ya ɗan kawar da kallonsa izuwa kan wayar tasa, lokacin sallah ya yi, mikewa ya yi dan baya wasa da lokacin sallah sam, kome yake yi da lokaci ya yi zai ajiye dan gabatar da sallah, shi yasa akoda yaushe yake yin nasara a kan makiyansa, saboda baya jinkiri wajen gaishe da ubangijinsa, shiyasa ubangiji ma baya jinkiri wajen biya mishi bukatunsa, wannan faɗi ne na Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, matukar zaka yi aikin Alkhari da bautar Allah a kan lokaci, to shi ma ubangiji zai zama mai amsa maka buƙatunka a kan lokaci, sallah ba abin wasa bane ƴan uwa, shi ne aiki na farko da ake fara bincika a ranar tashin kiyama, idan ta yi kyau, to fa ana sa ran ka tsira, idan bata yi kyau ba, kofar azabarka ce ta buɗe, Allah ka bamu ikon yin sallah a kan lokaci.
After some hours, bayan sun yi sallar isha, Mark ya kawo musu abinci, kin ci ta yi, shi kuma ya ci ya ƙoshi dan bai san cewa fushi take yi ba, da ya ce ta zo taci abincin, sai ta ce mishi ta ƙoshi, dan haka sai ya ci kayansa kuma ita ta yi serving ɗin shi.
Bayan ya kammala ta haɗa kayan abincin zata fitar da su ya ce ta barsu a wajen Mark ya zo ya ɗauka, kuka ta saka mishi tana turo baki, idanu ya zuba mata yana kallon ikon god, sai da ya ga da gaske take kukan nata ga hawaye wani na bin wani ne yasa ya ce "Lafiya dai ko?". Kara sautin kukan nata ta yi tana cigaba da turo baki.
Ɗan dafe kansa ya yi, shi dai bai san yaushe Rimsha ta dawo irin Aseef ba, yarinya sai shagwaɓa kamar ba gobe, amma dai tana burge shi over idan tana yi, har wani sanyi yake ji a cikin zuciyarsa.