Kenza eBookz

Triplets book 4 Complete - Chapter 16

Triplets book 4 Complete - Chapter 16

Triplets book 4 Complete Chapter 16: Triplets book 4 Complete Chapter 16. Ya yi shiru ya kasa amsawa, sanyayyar muryarta ta sake dakan dodan kunnensa.…

3,351 words

Ya yi shiru ya kasa amsawa, sanyayyar muryarta ta sake dakan dodan kunnensa. "Yaushe zaku dawo?" Shi ne tambayar da ta sake yi mashi.

"Kina son na dawo ne?". Jinjina mashi kai ta yi tamkar tana a gabansa, sannan ta ce "E ina so". "Why kike son na dawo?". Shiru ta ɗan yi kafin daga bisani ta amsa da "I want to see you close..." Sai kuma ta kasa karisawa.

Dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali kafin ya yi kasa da murya sosai ya ce "Meyasa kika kasa karisa maganar? Kina kewata ne?". "E a'a ni dai kawai ka dawo"............ Ji wata amsa, wai e a'a kai Jehan duniya ce.

Murmushi kaɗan ya yi yana faɗin "Sai after one week zan dawo". Shiru ta yi, sai kuma ta katse kiran. Shiru shima ya ɗan yi yana ɗan murmushi, almost 2 mins, sannan ya sake kiranta.

Kira na farko bata ɗaga ba, sai a na biyun ne ta ɗaga. "Ya naji kin katse kiran kuma?" Ya tambaya yana kokarin ciro wata igiya da ya gani a wajen kusa da Ac.

Muryarta kamar na mai kuka, da alama kuka ta yi, ta fara magana kasa kasa. "Na ji kace sai after one week zaka dawo ne, shi ne na barka sai bayan one week ɗin". "To me kuma ya sanya ki kuka?". A takaice ta ce "Ni ba kukan da na yi!".

"Am so sorry my baby, wasa nake yi maki, naja kin zubar da hawaye a banza, idan na dawo dole zan biya hawayen nan, ai nima ba zan iya yin kwana ɗaya ba tare da na ganki ba, anjuma kaɗan zan dawo, me kika ajiye mani?".

Sam bata san time ɗin da murmushi ya subce mata ba, ga hawaye a face nata falala. "Duk abin da kake so". Ta bashi amsa tana goge hawayen nata. "Are you serious?". Jinjina kai ta yi tana faɗin yeah.

"Okey tom shikenan, idan na dawo zan gaya maki abin da nake so ɗin, amma yanzu Please give me a kiss". Ya kai karshen maganar cikin wata iriyar murya mai kama da na shagwaɓa.

Kafewa ta yi a kan ita bata iya kiss ba, jinjina kai ya yi yana faɗin "Ba zan yi maki dole ba, ki kula mani da kanki kin ji ko? Ko palo ma ni bana son ki fito, ba dan daddy da mummy ba, ai da ba zan barki ma a gidan ba, amma dai ki kula sosai kin ji my pleasure?".

Kamar daga sama ya ji ta sumbaci wayar, sannan ta katse kiran ba tare da ta amsa mashi ba. Murmushi ya saki yana mayar da wayar a cikin aljihunsa, sannan ya nufi baban Muneer da yake kwance shame shame a cikin jini.

Ɗaure shi ya fara yi, shi kuma Imran, mikewa ya yi tare da ciro wayarsa ya nufi waje yana faɗin "Nima dai bari na ji voice ɗin tawa pleasure ɗin, da dai bani da ita ne sai ka yi mani gori".

Ko sannu bai ce mashi ba, ya ɗaure baban Muneer, sannan ya mikar da shi tsaye yana faɗawa Irfan su tafi ko?.

Ko da suka fito, ma'aikatan dake companyn, sun yi ƙoƙarin hanasu tafiya da shi, amma sai Areef ya nuna masu tsab zai yi ball da su idan basu tashi mashi a kan hanyarsa ba. A hanzarce wasu daga ciki suka kira office ɗin ƴan'sanda, sai dai kafin ma ƴan'sandan su zo, sunbar company ma abinsu. Haka suka kamo hanyar Kaduna.

A ɓangaren Lion kuwa, sai da ya ɗauki good 3 hours a asibiti ba tare da ya motsa ba, sai zarya likitoci suke yi a kansa, Aseef kuwa, da shegen saurin kuka kamar daddyn Jelly, sai zuba kukansa yake yi, har idanuwansa sun kumbura suntum, yaki yarda ya matsa kusa da Lion ɗin, yana zaune a saman bed ɗin, gwaggo na zaune a gefensu, ga sojojinsa suna tsaye cirko cirko a kofar shiga ɗakin, Mark ne kawai ya shigo cikin ɗakin, sai Tga dake ta faman magana da likitoci.

Duk wanda ya doso ɗakin da Lion ɗin yake kwance, sai ya juya a dubu ya koma, dan waɗan nan zaratan sojojin da suke tsaye a bakin kofar, ganin su ba ƙaramin razana al'umma yake yi ba, ga su jajir da su, tamkar ka taɓa jini ya zuba, dukkansu babu wanda yake sanye da uniform a jikinsa, duk fararen kaya ne a jikkunansu, fuska kam ba'a magana, kamar na shanu! A ɗaure tamau!.

Har sai da Lion ya kara good 1 awa, sannan ne likitocin suka yi nasarar saita bugawar zuciyarsa, suka kuma yi sa'a ya farfaɗo.

Yana buɗe idanuwansa, da Aseef ya fara cin karo, ido huɗu suka yi da Aseef ɗin. Da sauri ya mayar da idanunsa ya lumshe, yana tariyo abubuwa da dama a cikin ƙwaƙwalwarsa. Tabbas jaririn da mutumin nan ya kawo, mai brown eyes ne, jaririn da Josephine ta miƙa mashi kuma mai blue eyes ne, shi ma ɗayan jaririn da yake kwance, blue eyes ke gare shi, wanda Dr William ya fita da shi kuma ash eyes ke gare shi, abu biyu ne suka sanya Lion zuciyarsa ta kusa bugawa a cikin wannan video da ya gani, kuma kunsan abin da zai sanya shi suma duk da irin taurin zuciyar nan tasa ba ƙaramin abu bane!!.

Abu na farko, jaririn da ya ga mutun ya kawo, tabbas mai brown eyes ne, idan hasashensa gaskiya ce, to Aseef ne kenan, dan wanda yake kwance a saman sofa dai, mai blue eyes ne, hakan na nufin shi ne kenan, babban abin da ya fi ɗaga mashi hankali shi ne, ya fi kaunar Aseef ɗin sama da kansa, ya fi son Aseef fiye da Areef, ya fi son Aseef fiye da kowa, sun fi shakuwa, shakuwar da take a tsakaninsu baki ba zai iya faɗarta ba! Gara ace mashi mutuwa ya yi, da ace mashi Aseef ba jininsa bane! Ba zai iya jurar hakan ba, ko na rana ɗaya ba zai iya rabuwa da shi ba! Yana kaunar shagwaɓatinsa! Yana son ɗan rigimammensa! Yana son pleasurensa! Shi ne bugun zuciyarsu! Ko daddynsu ya fi kaunarsa sama da kowa! Ya ilahi ya lillahi, ina zai saka ransa ya ji sanyi! Josephine ta cuce shi! Ta gama da rayuwarsu, sai da suka saba! Suka taso a tare! Komai tare, shakuwa tasa har suke jin juna a jikinsu, yanzu ya Areef zai ji? Anya zai iya yarda kuwa? Babbar tambayar da Lion ɗin yake yi wa kansa shi ne, to meyasa suka yi hakan? Meyasa aka canza masu ɗayasu? Me suka yi da wancan ɗayan da suka ɗauka? Ina suka kai shi? Yana raye ne ko ya mutu? Shin Aseef mutun ne ko aljani? Cikakken mutun ne kuwa? Ko shi ne yasa yake wasu abubuwa da bana cikakkan mutane ba? Dole dai akwai dalilinsu na yin waɗan nan abubuwa dukkan, haka kawai baza'a canzasu ba! Haka kawai baza'a kawo wani yaro daban a cikinsu ba!!

Ni kuma PRINCESS TEEMA abin da yake cikin ra'ina, yake kuma damuna shi ne ya Akila zata yi? Ya zata ji a ranta? Shin zata zauna da wanda ba mutun bane? Ko dai yaya? Anya zata iya rayuwa babu shi kuwa? Tana son heartbeat nata fiye da kanta, wai Meyasa Aseef ya cika mugu mugun shiga ran mutane dayawa har haka ne? Meyasa kowa ya fi son shi? Wannan ma ayar tambaya ce!!.

Abu na biyu da ya sanya Lion ɗin zuciyarsa ta kusa bugawa shi ne, wannan mutumin da ya kawo wannan jariri ba kowa bane face uncle Herry, ba shakka uncle Herry ne, dan da kallo ɗaya Lion ɗin ya yi mashi, ya kalle shi da idanun basira, nan ya fahimci uncle Herry ne, duk da ya ɓoye komai na jikinsa, yana cikin shigar bakaken kaya, hakan bai hana kaifin ƙwaƙwalwa Lion ta gane cewa shi ɗin bane, saboda idanun uncle Herry, John, Jay, GTA, daddynsa, Aseef, Areef, ba za su taɓa canzawa ko su ɓoye mashi ya kasa gane su ba, ba zai taɓa kasa ganesu a ko wani irin yanayi ba, zaka gan shi wani lokaci kamar baya kallo abubuwa, amma yana sane da komai, tabbas uncle Herry ne ya kawo jaririn. Tambayar da Lion ɗin yake yi wa kansa, to ina uncle Herry ya baro daddynsu? Ina ya baro Dr? Bayan kuma a tare suka fita daga gidan a lokacin, ko dai ya yi wa Dr ma wani abin ne? Wai shin menene gaskiya? Me yake faruwa ne?!!!.

Waɗan nan sune abubuwan da suka hargitsa zuciyar Lion, ace kannen babansa dukka maciya amana, kuma su rasa amanar waye za su, sai na yayan nasu, kai duniya ina zaki damu, ɗan uwa ya ci amanar ɗan uwan sa, sun cutar da rayuwarsu, to wai me suka yi da jaririn da suka ɗauka? Kuma a ina suka samo jaririn da suka kawo ɗin? Ga dukkan alamu dai suma aiki suke yi a karkashin wata kungiya, ko kuma wani, dan ga dukkan alamu umarni suke karɓa, duba da yanda suka tsara abin, a lokacin shekarasun ya yi kankantar da za su iya tsara hakan, sun yi kananan wajen shirya wannan abin, dole akwai wanda ya fisu shekaru da yake shirya masu komai, wannan dalilin yasa Lion ɗin bai ji cewa yana bukatar ya zauna da su, dan su gaya mashi gaskiya ba, dan ya san irin wannan case ɗin, ko kashe su zai yi, wlh ba za su taɓa faɗar gaskiya ba, so is better for him ya nemo gaskiya da kansa, babbar magana, ta ina zaka fara kenan? Waye zaka fara tunkara?!!

Murya a dashe saboda kuka Aseef ɗin ya ce "My Lion, please ka tashi ka ji?". Kara datse idanuwansa sosai Lion ɗin ya yi, har cikin ransa yake jin muryar Aseef ɗin, yanzu idan gaskiya ta gama bayyana, shi Aseef me makomansa? Kenan idan ba mutun bane tafiya zai yi ya barsu? Ko yaya ne? Ya ilahi ya lillahi.

Gwaggo ce ta matso tana faɗin "Saif ka tashi dan Allah".

Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da waro idanuwansa a hankali, kai tsaye sai saman face nata kallonsa ya sauka. Shiru ya ɗan yi kafin ya kai hannu ya ɓalle karin ruwan da aka sanya mashi, ya cire, sannan ya yunkura ya mike zaune.

"Saif meyasa ka cire ruwan kuma?". Cewar gwaggo. Girgiza mata kai ya yi alamar baya da bukatar ruwan. Matsowa ta yi tare da dafa kafaɗarsa tana shafa kansa da hannu ɗaya.

Ɗago idanu ya yi yana kallon TGA dake tsaye a gefe guda, tun da yake da Uncle T ɗin nasa, bai taɓa tsura mashi idanu yana kare mashi kallo irin na yau ba, zuciyarsa na gaya mashi cewa har da uncle T ɗin yanzu a tafiyar su Josephine ɗin, amma yaki yarda da hakan, saboda wasu dalilan guda biyu, na farko TGA yana sonsu so na tsakani da Allah, dan an taɓa yin yunkurin harbin Lion ɗin ma da bingida, GTA ya tare, ya shiga tsakaninsu bullet ɗin ta same shi, na biyu kuma, TGA yana ɗan ƙaramin yaro lokacin da abubuwan suka fara faruwa, sai dai abin da ya sanyawa Lion ɗin shakku a kan Tga ɗin shi ne, meyake kai shi wajen Josephine a yanzu? A gaban idanunsu zai nuna baya son Josephine, amma a bayan idanunsu zai saci kafa ya je wajenta, ga uncle Herry ma, a gaban idanunsu yana nunawa baya sonta, amma a bayansu kuma 5 and 6 suke da ita. Wannan abin akwai matukar ɗaure kai over.

Ganin ya mike zaune ne yasa uncle T ɗin ya kariso wajen nasa da sauri, shi ma Mark karisowa wajen ya yi yana yi mashi sannu.

Zuro kyawawan fararen kafafunsa kasan gadon ya yi ba tare da ya ce masu komai ba. A hanzarce Mark ya bashi takalmar dake kafansa, dan ya sanya, saboda ya san halin Ogan nasa da bala'in kyankyani.

"Momma let's go". Shi ne kawai abin da ya iya furtawa, sannan ya mike tsaye. Daga Mark har TGA kallon gwaggo da ya kira da momman suka yi, mamaki Mark yake yi, tambayar kansa yake yi wacece gwaggo kuma? Shi dai ya shiga duhu.

Wani irin jiri yake gani da ya mike, har wani layi yake yi. Ganin hakan yasa da sauri Mark da Tga suka yi ƙoƙarin tallafa mashi. Hannu ya ɗaga masu alamar baya bukata, sannan ya juyo da kallonsa a kan Aseef dake ta binshi da kallo. Alama da hannu ya yi mashi a kan ya zo ya tallafa mashi su fita, Allah sarki sam baya son Aseef ɗin ya fahimci komai, ya zai ji a rayuwarsa? Ya zai yi da ransa idan ya san gaskiya?.

Mikewa ya yi, duk jikinsa a mace, ya nufo Lion ɗin. Ɗan rungumo shi Lion ɗin ya yi yana shafa kansa gwanin ban tausayi, haka suka nufi waje. Da sauri gwaggon ta mike ta rufa masu baya, su Tga suka rufa mata baya. Shi dai Mark kansa ta shiga duhu....... NI KO NA CE MARK BA KAI KAƊAI BA, KOWA MA KANSA TA SHIGA DUHU, WAI KAI DAN MA BAKA SAN ABIN DA MUKA SANI BA, AI DA DUHUN DA ZAKA SHIGA MA BA ZAI FAƊU BA!!.

Suna fita sojojinsa suka rufa masu baya izuwa wajen motocinsu. Lion haka kawai yake jin babu daɗi zuciyarsa, tunanin Rimsha dake ta faman sheka barci a gida ne ya faɗo mashi a cikin ƙwaƙwalwarsa, nan take ya ji kirjinsa ta buga, tasbihi ya fara yi a cikin zuciyar nasa, dan ya samu salama, abubuwan sun yi mashi yawa, tunani yake yi bai kamata ya yi nisa da duk waɗan da suke da kusanci da shi ba, dan a wannan point da suke a yanzu, kamata ya yi ya haɗe familyn gwaggon gabaɗaya waje guda, domin kuwa, a yanzu koma suwaye suke bibiyar rayuwarsu, sun san ya san komai, ba shakka za'a cutar da su, kuma tabbas familyn gwaggon za'a cutar, dan familyn daddynsu kam suna da hannu dumu dumu a kan komai, so yana da kyau ya haɗa gabaɗaya ƴaƴa da jikokin Dr Salman waje guda, sannan a saka masu matakan tsaro, idan ba haka ba, za'ayi masu ɗauki ɗai'ɗai!!. Babbar magana.

Wayar Aseef ne ta fara kara dai'dai lokacin da suka shiga cikin motar. A hanzarce ya cirota daga aljihunsa, ya sha ruwan mamakin ganin uban miss call na Areef, dan lokacin da Areef ɗin ya yi ta kiransa, sam bai ji ba, baya a cikin hayyacinsa.

My uncle, shi ne sunan da ya bayyana a saman screen ɗin wayar. A hanzarce ya ɗauki kiran, a lokacin kuma har motocin nasu sun fara tafiya, sun fito daga asibitin, yana zaune kusa da Lion, shi da gwaggo sun saka Lion ɗin a tsakiya a gidan baya na motar.

A hand-free ya sanya wayar, daga ɗayan ɓangaren daddyn Rimsha ya ce "Aseef kuna tare da Akila ne? Ta zo asibitin ne?". Jin tambayar daddyn Rimshar yasa Lion ya juyo da kallonsa a kan wayar.

"A'a uncle, ni tun da kuka tafi da ita jiya, ban sake ganinta ba, na kira numberta da safe ma a kashe". "E ba shakka wayarta a kashe, muma mun kira bata shiga, amma ina zuwa".

A hanzarce Aseef ɗin ya ce "Uncle lafiya dai ko? Meyasameta? Bata gidan ne? Ina ta ce dama zata je?". Ya yi maganar a rikice.

"A'a babu abin da ya sameta Aseef, ka kwantar da hankali, ina zuwa zan sake kiranka". Bai jira masar da zai bashi ba, kawai ya katse kiran.

TOH FAH INA AKILA KUMA TA SHIGA⁉️

Karɓar wayar Lion ɗin ya yi, cikin sauri ya fara kiran number Rimsha, dan dama ya kawo wa ransa za'ayi wa matan familynsu gwaggo ɗauki ɗai'ɗai, kuma idan basu yi saurin ɗaukar mataki ba, duk za'a kashe matan ne, dan da alama babu wasa a lamarin masu aikata hakan, bare ma da suka san yanzu asirinsu na gab da tonuwa, ai sai dai wanda Allah ya ƙaddara kwanansa na gaba, amma za'a zubar da jini kam ba kaɗan ba!, Kuma dole hankalinsa zai tashi, saboda a halin yanzu Rimsha ta fi kusa da shi sama da kowa, kuma ga shi shi ne yake shirin bankaɗo gaskiya, shi ne babban makiyin mutanan, ko dan a sanya shi ya rusina, za'a iya yi mata wani mummunar abin, so dole ta kasance a tare da shi a ko da yaushe, rayuwarta yana cikin hadari sosai, da alama ya yi shigar sauri wa mutane, bai shirya ba ya shiga yakin, hakan kuma zai wahalar da shi da na kusa da shi ba kaɗan ba!!.

Sai kiran wayar yake yi, amma ina bata ɗauka ba, number Areef ya kira, su kuma a lokacin sun kamo hanyar Kaduna, babu network sam, number bata shiga, tsaki ya ja tare da dakawa Mark tsawa a kan ya taka motar nan da sauri su kai gida da wuri, dan ya duba ya tabbatar Rimsha tana gida or not. Babbar magana.

Mikawa gwaggon wayar Aseef ɗin ya yi, cikin sanyin murya ya ce "Momma ki gayawa dukka uncles namu yanzu ba sai anjuma ba mu haɗu a gida, dukkansu da ƴaƴansu gabaɗaya".

"Saif meyake faruwa ne? Ɗazun Abban Imran ya kirani ya ce Ayla matar uncle naku Maik ta ɓata, daga baya ya sake gaya mani mijin Aafia ya rasu, ita kuma Aafiar bama su san a wani point zasu ajiye ta ba, yanzu kuma na ji Nawazuddeen yana tambayar Aseef ina Akila, me dukka wannan ne?".

Nisawa ya yi kafin ya ce "Momma babu komai, just tell them what i said kawai, and ki yi sauri ki bani wayar ina son in gayawa Areef a duk in da yake, ya yi sauri ya zo gida ina son yin magana da shi......." Bai kai ga rufe baki ba Mark ya ja wata mahaukaciyar burki, waddata sanya su suka tafi luuuu suka buga kansu da jikin sofar motar, shi ma Mark ɗin sai da ya buga kansa da jikin steering motar.

Kusan a tare suka ɗago kawunansu tare da kai kallonsu a gaban motar, dan suga menene ya sanya Mark ɗin taka irin wannan burki haka...................

❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥

*KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*.

*KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*.

❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥

https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S

❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥

TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️

❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋)

*Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581*

E9

Kusan a tare suka ɗago kawunansu tare da kai kallonsu a gaban motar, dan suga menene ya sanya Mark ɗin taka irin wannan uban burki haka.

Ko da suka ɗago kansu, babu komai a wajen, kan hanyar wayam, da mamaki Aseef yake kallon Mark ɗin, bawan Allah shi kuma wata halitta ya gani tsaye a tsakiyar hanyar, shiyasa ya yi kokarin kauce mata, ashe gizo kawai aka yi mashi, da alama an shirya masu hakan ne domin su yi accident, sai kuma Allah ya karesu da kariyarsa.

Aseef ɗin zai yi magana, Lion ya dakatar da shi, sannan ya ce da Mark ɗin su tafi kawai.

Kunna motar ya yi suka cigaba da tafiya, ita kuma gwaggon ta kira su Abba kamar yanda Lion ya ce mata, daga haka babu wanda ya sake yin magana a cikin motar.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull