Kenza eBookz
Cover art for KIDA A RUWA BOOK 2 PAGE 6

Post

KIDA A RUWA BOOK 2 PAGE 6

..... but Dada replied with a little closed eyes and opened them again on Imran. "I trust you to work with him, Imran..." Imran said, "Are you going to meet people whom everyone is afraid to raise?". A small, warm, bitter smile appeared on the corner of Dada's lips. "I am not someone I am afraid of, Imran. But the truth... is what they have prevented me from seeing for three years. I myself agree with the general's prediction, in the way they are leading, we will just follow and find them and fight them" he was silent for a second. Then he continued to say, "Today I am giving you this text. Take it away. Don't let anyone see it now, even the General. I only want you to do these investigations." In other words, if Zak.. is concerned about something, sometimes he looks like a demon or a seer, even children fight. Even a fortune teller can call it, but he knows that it is not like that, it is just a coin of intelligence and the ability to know about the world and the people in it that GOD has given him. When he or Dada saw the look that Imran was giving him, he just leaned on the chair slowly and closed his eyes. So he said, "I don't know the sauce.....

Standalone post2,069 words

___________________

..........“Ku fara da gaskiyar Ojo. Akwai wani abu da bai dace ba. Kuma akwai hannaye da yawa da suka fi mu ƙarfi har a cikin gida. Sai dai fuska biyun su tasa sun zame mana masu lulluɓin biri”. Shiru ya cika ɗakin. Wani irin sanyi ya ratsa zuciyar Imran. Cikin kasa haƙuri ya furta, “Idan kuwa har akwai masu fuska biyu zan kasance mai tsoro da shakkar mu'amulantar kowa?”. “Wannan shine gaskiyar magana, amma a ciki akwai ɗaya tamkar da dubu. General Yusuf Shu'aibu Tafida. Col. Haydar Galadima (Faro), Brigadier General Abraham Yohana, yaranmu Dabo, Yusuf. Amma saura duk ka ajiye kowa. Akwai saƙo a ɗakina na ajiye maka, idan ka haɗa da wannan zai baka abinda nake buƙatar ka fahimta. Dan na tabbatar daga yau bazasu sake barinka ka ganni ba.” Da ƙyar Imran ya iya furta, “Janar ya shiga SIYASA...” Cak numfashin Zak-Shadow ya tsaya, hakama bugun zuciyarsa kafin su dawo a tare. “SIYASA?!”. Ya furta yana tsatstsare Imran da idanu. Kai tsaye Imran ya jinjina masa kai. Sai kawai Dada yayi murmurshi tare da wani ɗan lumshe idanu sannan ya sake buɗesu luuu akan Imran. “Na amince kayi aiki da shi Imran....” Cikin tsatstsareshi da idanun shima Imran ya ce, “Zak… kana nufin kaci karo da mutanen da kowa yaji tsoron ɗaga su?”. Wani ƙaramin murmushi mai zafi, mai ɗaci ya bayyana a gefen labban Dada. “Ni ba wanda nake tsoro, Imran. Amma gaskiya… ita ce abin da suka hana ni gani tsawon shekaru uku. Ni kaina kuma na yarda da hasashen General, ta irin hanyar da suke kai, kawai zamu bi mu gano su, mu kuma yaƙe su” ya ɗanyi shiru na sakan biyu. Sai kuma ya cigaba da faɗin, “Yau na baka wannan rubutun. Ka tafi da shi. Kada ka bari kowa ya gani a yanzu har Janar. Dan kai kaɗai nake son kayi waɗan nan binciken” Idanu kawai Imran ya kafeshi da su ya ma kasa magana. Wato idan Zak.. ɗinsa na wani abu a wasu lokutan yakan ga tamkar mai aljanu ko mai gani har hanji da yara kan faɗa. Kai har ɗan duba ma zai iya kiransa, amma yasan duk ba haka bane, tsabar kaifin basira ne kawai da iya sanin kan duniya da mutanen cikinta da ALLAH ya bashi. Shi ko Dada ganin kallon da Imran ɗin ke masa, sai kawai ya jingina da kujera a hankali ya lumshe idanunsa. A haka ya ce, “Ban san miya baka mamaki ba ka tsaya kana kallona bayan lokacin ka ƙayyadadde ne. Idan rana ta yi zaka gane me yasa naga mutuwa ta fi wannan shari’ar sauƙi.” Imran ya kasa magana yanzun ma, a haka har lokaci ya ƙare, masu tsaronsa suka buga ƙofa. Miƙewa kawai Dada yayi zai bar gurin, sai kuma ya tsaya ya kalle shi for the last time yasan kafin a sake ganin juna sai bayan shekaru. Dada ya lumshe ido tare da furta masa a hankali kamar sirrin da baya buƙatar iska ta ɗauka zuwa gaba a tsakanin su. “Ka zama hasken da nake bukata a waje. Ka cigaba da zama UBA kuma nagartaccen MIJI a cikin GIDA”. Daga haka yay gaba batare da ko waiwayen Imran ba. Shi ko Imran ya kasa motsi sai kai-kawo furucin ƙarshe na Zak-Shadow ɗin ke masa amsa kuwwa a cikin kai, dan magana ce a dunƙule ya bashi kuma mai ƙarfi.....

(((★)))(((★)))(((★))) ★ 2021..... ★

Duk wanda yasan gidan a shekarun baya takwas da suka shuɗe yanzu idan ya zo ba lallai ya gane ba. Domin kuwa gidan nan da Mammah da yaranta tara mai sassa biyu kacal a yanzu ya zama mai sassa da yawa sakamakon iyalanta da suka ƙara yawa. Kamar yanda Dada ya barma Imran wasiyyar dawo da ginin su Ma'aruff a cikin gida a wacan lokacin hakan ta tabbata, duk da kuwa shima Imran ɗin dole ya bar ragamar a hannun Uncle Nasiru sakamakon prison ɗin daya shiga na shekara uku. Duk da suna cikin ɗacin yanayi Uncle Nasiru yayi abinda ya dace harda kuɗin aljihunsa. Anyi bikin Ma'aruff da Ja'afar da amarensu Shariffa da Lailah, sai dai bikin baiyi armashi ba sakamon jarabawar da wannan ahali suke ciki a wancan lokaci na rasa jigon gidan da suke ma kallon Uba bawai yaya kawai ba. Amare sun tare a gidan Mammah kowace da ɓangarenta, kuma Alhamdullah dukansu masu tarbiyya ne da suka fito daga gidan tarbiyya. Dan kuwa akwai abubuwa da yawan gaske da suka bambanta su da surukar gidan ta farko Nabeeha. Mammah mace ce mai sauƙin kai da sanin haƙƙin ɗan adam, tana da zafi idan kace zaka kawo mata wargi, dan in har kaji muryarta a sama lallai an kaita maƙura ne. Duk wanda yazo jikinta ya zama ɗa na halak da zata haɗe da nata ƴaƴan ya riƙe babu bambanci a ciki, wannan yasa biyayya da nutsuwar Aunty Shariffa da Aunty Lailah ya basu fiye da abinda suke zato da farin ciki a gidan aurensu. Dan kuwa suna matuƙar kiyaye al'amarin Mammah a matsayinta na uwa, hakama ƙannen su Ma'aruff sun maida su ƴan uwansu na jini ba dangin miji ba, sai hakan ya bada masalaha da shaƙuwa mai ƙayatarwa da birgewa a wannan gidan, idan ka cire rashin Dada dake zagaye da zukatansu dan suna jin hakan a ransu a kowacce rana tamkar sabo. Babu ranar banza da zata zo ya wuce ba'ai hirar Dada ba, za kuma ka samu hatta su Ma'aruff dake magidanta kuma manya yanzu a gidan sai sunyi kuka suma. Mammah ce kawai jaruma mai danne komai a gabansu sai dai idan tana ita kaɗai ta share hawaye. Shekarar su Lailah ɗaya a gidan duk suka haihu, kuma Alhamdullah haihuwar tasu babu wani nisa tsakani. Dukan su yara maza suka samu, kuma yaran sunan Dada da Imran aka saka musu wato Haysam da Imran. Sai dai ana musu alkunya da Abees da Aheel. A shekarar da Imran ya fito bayan ya gana da Dada sau biyu sannan suna cika shekara uku-uku da aure suka sake haihuwa, sai dai wannan karon Shariffa mace ta samu, ita kuma Lailah Namiji. Bayan haihuwar tasu ne kuma Imran ya sake tada saban aikin gyaran gidan na su Mammah. Dan kuwa gaba ɗaya aka rushe sashen Mammah dana su Zak-Shadow tunda Nabeeha ba zama take ba sai jefi-jefi take zuwa gidan, shima ɗaukar wani abu ne ke kawota, wani lokacin ma sai tazo ta fita su Mammah basu sani ba. A wannan karon ne akama gidan gyara fiye dana baya, dan komai da fasalinsa an canja, hatta Ammar da Bilal an musu nasu ɓangaren. Sai ya zama anyi sashe huɗu ta can baya, an fitar da gate ta wancan Street ɗin, ta cikin gida akwai katanga tsakanin ɓangaren su Ja'afar ɗin dana su Mammah da Dada da suma suke su biyu. Tsarin ya bada kamar gida biyu. Dada da Mammah a sashe ɗaya, su Ma'aruff su huɗu a sashe ɗaya sai dai kowa da part ɗinsa, akwai katanga tsakaninsu amma akwai ƙofar da zaka iya shigowa sashen su Mammah basai ka zagaya ta wajen gate ba. Wannan gyara shine ya sake sauya gidan Mammah daga mai sashe biyu na talaka mai ƙaramin ƙarfi zuwa na masu rufin asiri da wadatar zuci a yanzu, ga irinmu ma talakawa kai tsaye zamu kirashi ana masu kuɗi.....

))))(((()))))((((

A ɓangaren Imran yanzu haka dai shekarunsa biyar kenan da ganawa da Dada dake cika shekaru 8 a prison, kamar yanda Dada ɗin yay hasashe ya faɗa kuwa ba'a sake bashi damar ganinsa ba. Babu irin shiga da fitar da baiyi ba amma sun hana masa damar sake ganinsa. Dan haka Janar ya zauna ya lallashesa akan yayi haƙuri komai yana da lokacin sa. Badan hankalin Imran ya samu kwanciya ba ya haƙura. Sai dai ya maida hankali akan binciken dukkan abubuwan da Dada ɗin ya bashi. Sannan yaje ya ɗauki saƙon daya ce ya ajiye masa. Inda saƙon ya fahimtar da shi abinda Dada ya shirya. Dole ya ajiye batun damuwarsa da kewarsa a gefe ya maida hankali akan aiki yanda ya kamata....

Burin Janar ya cika na shigewa cikin siyasa tsundum da sha'anin ƴan siyasa. Cikin nasara ya lashe kujerar da aka tsaida shi a takarar ɗan majalisan tarayya. A yanzu haka yayi ɗan majalisa shekara huɗu kenan. A kuma yanzu haka ana shirin sake buga tambarin sabon zaɓe, babban shirinsa kuma shine fitowa takarar shugaban ƙasa. A gefe kuwa Imran ya sake samun girma zuwa Colonel saboda kwantar da kai da yayi shima bisa shawarwarin General ɗin dana Dada.....

✷✷>><<✷✷>><<✷✷ ★SCHOOL★

“Yau sai naga waye ubanku a cikin ƙasar nan, ƴan iskan yara kawai kamar wasu ƴan daba ku kama min yarinya da duka, koni dana haifeta da ubanta bamu taɓa dukanta haka ba. To wlhy idan kuna taɓa wasu ku zauna lafiya yanzu kun taɓoma kanku kuwa, dan har prison sai na saka ubanku yayi bama ku ba.......” “Ranki ya daɗe dan ALLAH kiyi haƙuri, mahaifinsu bashi da laifin komai sune sukai miki ba daidai ba. Wlhy mu kammu yaran nan sun kai mana wuya a makarantar nan, kawai dai babu yanda muka iya ne.....” “Oh babu ma yanda kuka iya? Wato tsoronsu ma kuke ji saboda uban su ne shugaban ƙasa, yara na irin wannan ta'addacin amma kuke iya barinsu a cikin makarantar ku harda faɗin babu yanda kuka iya.....” Kasa cewa komai principal yayi, sai ma haƙuri daya cigaba da bama hamshaƙiyar matar da kallo ɗaya zakai mata kasan matar babban mutum ce a ƙasar. Dai-dai nan akai knocking ƙofar ofishin, principal ya bada izinin shigowa. Wani matashin saurayi ne da alamu suka nuna shima ma'aikaci ne a makarantar, yay sallama ya shigo sannan ɗalibai biyu dake bayansa riƙe da wata matsakaiciyar budurwa da bata wuce 15years ba suma suka shigo. Zaram matar ta miƙe tai kansu, jikinta har rawa yake ta kamo hannun yarinyar da suka riƙo kanta naɗe da ƙaton bandeji, fuskata kuwa da ganin yanda tai suɓu-suɓu kasan tasha maruka da kuka ta kuma ci bugu, dan idanun jazur suke suma luhu-luhu. Jikinta yarinyar ta faɗa, yayinda ita kuma ta ɗauki dogon salati ta dire tana mai ɗago yarinyar a jikinta.........✍️

Wannan aiki nasan sai Zakanya da vice ɗinta Damisa🤣.

_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._

*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_*

*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_*

*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*

*9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_*

*_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull

*_WHATSAPP (500)_*

*1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_*

*_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_*

*_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*

*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*

*_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899*

*_ASSALAMU ALAIKUM MUTANE NA MASU ALBARKA_*

*_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._*

*_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_*

*_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._*

*_Akwai VVIP AREWAPEN kenan 💃_*

*_Akwai VIP Telegram 💃_*

*_(Ƴan WhatsApp ku haƙura kawai ƴan ta'addar bati sunfi yawa a cikinku gaskiya tsoron rashin m ɗinku nake 😂🤣)_*

*_Telegram Audio 2k ne kacal ba tsada 💃. Sai kusaka ta wannan account ɗin👇_*

_(2k)_

*9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (2k)_* *_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_*

*_Ƴan NIGER🇳🇪 kuma bazamu barku a baya ba in sha ALLAHU zaku biya (Telegram vip 1,500 CFA) domin littafin KIƊA A RUWA..... na ji Audio-vocal. Sai ki biya tanan👇_*.

_(1,500 CFA)_ *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_*

*Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 1,500 CFA vip telegram

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_*

*_AREWAPEN (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull

*_Ƴan WhatsApp kuzo muyi shawara idan zaku iya amana ayi harkar nan daku 😂, dan bana son a barku a baya duk da dai bakwa ji, ba raga min zakuyi ba na sani duk da ƙaunar da nake muku 🤣😂._*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

7