
Post
Kida a ruwa Book 3 page 48
..... today we have not seen him in this house even once". Dada just smiled a little and did not say anything. Imran also stood up and took the laptop with his entire body... Dada said, "Are you okay?". "No, it's easy. Don't get up if I call Mammah on the phone." "I am the one who will call Mammah?" Do you mean that I will welcome you to a girl who is a bride on her first night in your house? I will also come today to update my advice, I will not be there." Dada almost laughed at Daddy Imran's last statement. But he did nothing but his face showed a sign of recovery. He didn't bend down and didn't stand up. He knew that Imran would never let him breathe. He just looked at his phone to find the way out. Imran turned off the laptop and he was recovering. He also gathered everything behind him. After the prayer, Imran said he would not go inside. He did not say anything and went to the house. The hall was full of people from Kano and Maiduguri.
48
..........“Yaufa bazaka kwanar mana a gidan nan ba Zak..” Shiru kamar Dada baiji mi Daddy Imran yace ba. Idanunsa akan screen ɗin laptop yana aiki hankali kwance. Sarai Daddy Imran yasan ya jishi. Zancen ne baya son ayi kuma bazai barshi ba, yau zaiga ƙarshen miskilanci. “Haysam!”. Ya kira shi da sunan daya kan jima bai kirasa da shi ba. Dan haka Dadan ya ɗago idanunsa a karo na farko ya kallesa. Imran ya harare shi. “Kana jina kenan?”. Dada yay murmurshi yana kauda idanun nasa daga kallonsa. Cikin sake basarwa ya ce, “Kazo mu ƙarasa aikin nan, kasan fa gobe akwai office bamu da isasshen lokaci. Dan ba lallai ka ganni a gidan nan ba ma”. “Babu wani aiki da zamu cigaba da yi gida zaka wuce. Bamma san miya dawo da kai ba yanzu...” “Miyasa kake da rigima ne wai?”. Cewar Dada yana sake maida idanunsa akan screen ɗin laptop ɗin. Imran ya ce, “Hummm har na kai ka rigima ne. Ni yanzu ma duk ba wannan ba. Canai ka tashi muje na rakaka. Ni ban taɓa ganin ango irinka ba wlhy. Kana ganin Haydar yau ko sau ɗaya bamu ga ƙeyarsa a gidan nan ba”. Dada ya ɗan murmusa kawai baice komai ba. Shima Imran sai ya miƙe yazo ya ɗauke laptop ɗin jikinsa gaba ɗaya... Dada ya ce, “Kana lafiya kuwa?”. “A'a da sauƙi dai. Koka tashi ko na kira Mammah a waya”. “Ni ne zaka kirama Mammah?”. “Da gudu ma kuwa. Kana nufin zan barka ka barmin yarinya ita ɗaya tana amarya a daren ta na farko gidanka? Nima zuwa zan yau na sabunta nawa angwancin dan baza'ayi babu ni ba”. Dariya ta kusa kama Dada akan furucin ƙarshe na Daddy Imran. Amma baiyi ba sai dai fuskarsa ta nuna alamar murmurshi. Bai sake tankawa ba ya miƙe kawai dan yasan nacin Imran bazai taɓa barinsa yasha iska ba. Wayoyinsa kawai ya ɗiba yay hanyar fita. Imran dake kashe laptop ɗin yay murmurshi shima ya tattare komai waje ɗaya yabi bayansa....
★Sun iso anguwar ana shirin sallar isha'i. Dan haka suka shiga massalaci kawai. Bayan an idar da sallar Imran yace shi bazai shiga ciki ba zai wuce gida kawai. Dada baice komai ba ya bashi hannu sukai musabaha. Ya shiga mota shi kuma ya shiga gida. Maimakon sashensa sashen Mammah ya nufa. Falon cike yake da baƙin Kano dana Bauchi da Maiduguri. Duk da kuma kasancewar ba yara ne kawai ba harda manya sai da kwarjininsa yasa sukai tsitt, yaran duk suka sake nutsuwa suna masa sannu da zuwa da gaishe shi. A taƙaice ya amsa a jimlace. Sannan ya gaida suma manyan a jimlacen. Sun amsa masa tare da addu'ar zaman lafiya nahar abadan ga duk ɗinsu ma'auratan. Sun san bamai yawan magana bane, dan haka basu damu da amsawar tasa a taƙaice ba. Daga haka ma ya wuce ɗakin Mammah dan tunda har bai ganta anan ba yasan tana ɗakinta. A can kuwa ya sameta ita da Aunty Mimi tana shafa mata man zafi a ƙafafu. Ya zauna kusa da ita yana amsa sannun da Mimin ke masa idanunsa akan ƙafafun Mammah ɗin. “Suna ciwo ne ƙafan?”. Murmushi Mammah tayi da amsa masa da, “A'a gajiyar kai-kawo ce kawai Muhammad. Yanzu nake tunanin kiranka ashe kana kusa?”. “Mammah ta samu ke nan?”. Mammah tai dariya da faɗin, “A'a, yadai kamata kazo kama su Bilal nasiha duk da nasan kullum cikin yi kake”. Murmurshi ya ɗanyi bai ce komai ba. Dai-dai nan kuma sai ga sallamar su Ja'afar ma.....
....★★★....
Cikin matsananciyar kunya Biebah ta fito a bayin duk da rigar wanka data saka a jikinta ta rufa da towel ɗinsa kuma babba. Faro dake zaune bakin gado yana waya ya ɗago idanunsa yana kallonta. Shi sai ma ta bashi dariya. Amma dai ya danne baiyi ba. Ya cigaba da wayarsa duk hankalinsa na kanta. Sai dai ganin bata da niyyar baro inda take tsaye ta sashi miƙewar shi yana bama abokin wayar tashi amsar zancen daya gama yi masa. A gabanta ya tsaya, kai tsaye kuma ya kai hannu ya yaye towel ɗin gaba ɗaya. Sai kawai ta runtse idanunta dan bazata iya hanashi ba ko yin musu. Bai ce da ita komai ba shima ya jefa towel ɗin kan kujerar mirror sannan ya sake juyowa inda take. Fuskarta da idanun ke rufe ya kalla. Cike da rashin kunya irin ta soja ya kai hannu saman igiyar rigar wankan data ma ɗaurin zarge kawai ya jashi ya warware. A take rigar ta buɗe jikinta ya bayyana. Dai-dai kuma lokacin yake ƙoƙarin yin magana da wanda suke wayar kawai yawu ya sarƙesa ya fara tari. Yayinda ita kuma ta zabura jikinta na rawa ta juya masa baya wata kalar matsananciyar kunya da bata taɓa ji a rayuwarta ba na mata bargo a illahirin jikinta.. Faro ya yanke wayar ƙirjinsa na bugawa da sauri-sauri. Ai baima san ya je gab da ita ya rungumeta ta baya ba dan ji yay shima jikin nashi na rawa tsabar yanda yaji wani al'amari mai matuƙar girma ya tsarga tun daga saman kansa zuwa yatsar ƙafarsa. Har ji yake ƙafafunsa na neman kasa ɗaukar nauyin gangar jikinsa. Kallon nan ɗaya tak da yayma Biebah a ainahin Biebah ɗinta ya kwance masa dukkan lissafin sa, dan bai taɓa tunanin yarinyar takai har haka ba, koma yace ta zarce inda yake zato da tsammanin ta. Tunda yasan Biebah a shekarunta na hankali da hijjab ya santa. A hotunan bikin nan ne kawai ya fara ganinta ba hijjab.. Biebah kam da gaba ɗaya ke jinta kamar ta fashe da kuka dan tsoro da kunya neman zamewa a jikin nasa take. Amma ya hanata dukkan dama sai ma kamata da yay ya sake juyota suna facing juna. Bazata iya tsayawa ya cigaba da kallonta a haka ba, duk da tuni ta kama rigar ta sake haɗewa waje guda ta rufe jikin nata. Sai dai bata ɗaure igiyar ba a yanzu. Bata da mafitar data wuce neman wajen ɓuya, musamman daya sake ɗora hannunsa akan nata hannun dake runtse da rigar zai buɗe. Jikin nata na tsuma kawai ta shige nashi jikin ta ƙanƙamesa... Murmurshi ya saki, sai kuma ya maida fuskarsa kan wuyanta shima yana mata zobe da hannunsa ɗaya kawai ya fara bata sumba a wuyan. Rawar da jikinta take yanzu kam ta wuce ta farko. Dan bata ma san ta saki rigar ta koma ƙoƙarin riƙe hannunsa dake yawo a gadon bayanta ba. Da wannan damar Faro ya samu ya saluɓe rigar gaba ɗayanta ta sauka ƙasa. Zatai magana ya haɗe lips ɗinsu waje guda kawai tare da ɗagata cak daga kan ƙasa ya nufi karagar mulkinsa da ita.......
★∆∆∆∆∆∆∆∆∆★
Anan ɓangaren su Mole kuwa basu san wainar da ake toyawa ba, saboda Dagger dake fama da jiyyar ƙafarsa data sha harbi. Sai yau ne kwatsam kiran Sanda ya samu Mole. Lokaci-lokaci Mole kan kira Sanda ya zungureshi labarin gidan, amma kwana biyu sai bai jisa ba, gashi har ansha biki, shine kawai Sanda yace bari ya taɓa shi yaji ko lafiya. Bayan sun gaisa Sanda ke faɗin, “Malam Buba ka ƙi dawowa dai, ga shi har an sha biki, ko har yanzu jikin matar taka ne dai?”. Da mamaki Mole ya ce, “Biki kuma? Na waye? Kuma a ina?”. Dariya Sanda yay yana gyara zama an samu na fesawa, dan dama yanda akasha bikin nan tuni neman abokin labari yake da bai gani ba. Dan haka ya gyara zama ya fara zayyana zance daki-daki. Tun kan yakai maganar farko ƙarshe zufa ya wanke jikin Mole tas, cikin rawar bakin da yasa Sanda yay shiru na mamaki Mole ya furta, “Sanda kana nufin yanzu ita Uwa ɗin ta tare a sashen?”. “Kaifa Malam Buba shiyyasa ban cika son baka labari ba, wani lokacin sai ka dinga yi kamar baka ganewa. Miye kuma wani Uwa. Hajiya Nimrah fa nake faɗa maka Babban Alhajin gidan nan ya aura, ita kuma usainarta Alhaji Ammar. Dan ALLAH idan ana baka labari ka dinga barin mutum na kaiwa ƙarsh....” Ƙittt Mole ya yanke wayar jin hajijijiya na neman zubar da shi a wajen. Cikin sassarfa ya bar inda yake zaune zuwa cikin gida da Oga Dagger ne kaɗai sai ƴammatansa suke holewa. Ai bai jira izinin shiga ba kamar yanda dokar take, Dagger na falonsa jikinsa ƴammata biyu na masa tausa yana busa wiy-wiy Mole ya faɗo. Cikin takaici Dagger ya dubesa, ya buɗe baki zai danna masa zagi ya riga shi yin magana... “Oga muna cikin tashin hankali. Matsiyacin nan fa ya tare da Uwa”. “Miye Uwa?”. Dagger ya faɗa yana harararsa. “Oga ya kake abu kamar baka gane ba. Nimrah nake magana Zak-Shadu yake ko mi yasa an musu biki...” Tuni Dagger ya wancakalar da ƴammatan biyu gefe yana miƙewa cikin rawar jiki. A gigice ya furta, “Amma dai hauka kake ko Mole?”. “Oga idan ma ban haukace ba da yanzu kam na haukace wlhy. Shi ke nan rayuwata ta gama lalacewa maƙiyina ya zama mijin ƴata”. Ji kake tauuu Dagger ya wanka masa mari. Tare da nuna shi da yatsa. “Idan ka sake cewa mijinta wlhy sai na kashe ka kaima”. Ya hanaɗesa gefe yana ɗaukar bindiga dake saman tebirin gabansa ya nufi hanyar fita.........✍️