Ƙayar ruwa book 2 and 3 complete - Chapter 24
Ƙayar ruwa book 2 and 3 complete Chapter 24: Ƙayar ruwa book 2 and 3 complete Chapter 24. Ko takalmi ban iya cirewa ba na zauna ina goge hawayena tare da…
4,475 words
Ko takalmi ban iya cirewa ba na zauna ina goge hawayena tare da danasanin tahowar da nayi. Ko kayan ban cire ba na tashi na fita zuwa ɗakin Abbaa, sai da na tabbatar ya haƙura ya daina fushin kana nayi masa sallamar sai da safe na wuce ɗakin Ummani na ci abinci. Wajen sha ɗaya har na rufe ido naji wayata na ringing, da sauri na tashi na rarumota gudun kar Abbaa ya jiyo ƙararta, nifa mahaifina is very strict, bai ƙi ya zo ya ƙwace wayar ba, ban ɗaga ba sai da naga kiran yay yawa har sau uku sannan na ɗaga ana huɗun.
Nayi sallama aka amsa, shiru for some seconds sai aka ce,"Nurse Sa'ida ce?".
Na ce,"Ehh ita ce". Na faɗa ina jin muryan kaman na santa duk da cewan muryan namiji ne.
Sai aka ƙara cewa,"Sorry don Allah na kira ki da daddare, ɗazu na zo asibiti ne Dr Samuel yake bani number na ki yace duk sanda na zo na dinga nemanki, domin ke ɗin ƙwararriya ce wacca ta san makamar aikinta".
Babu shakka na san muryar sai dai ba zan ce ga inda na santa ba ko kuma ta wacece ba, a hankali yaci gaba da magana yana ce min yana fama da ciwon baya ne da ƙafa ko zan taimaka na recommending masa maganin da zai sha yanzu kafin zuwa da safe yaje asibiti. Na zage na buɗe murya ina ta kora masa bayani da tambayan ya yake ji, kusan minti goma haka sai naji ya katse ni da tambayan,"Babu dai wani damuwa ko?".
Na ce masa,"A'a babu, duk sanda kake neman taimako irin haka zaka iya kira na".
Sai ya sake cewa,"Thank you so much, but still ba ki cikin wani matsala dai ko?".
With confusion na ce,"Babu komai, kawai na dawo daga aiki ne yanzu na gaji ina so zan yi bacci". Na faɗa ina sauke wayan daga kunnena na kashe bayan ya cika ni da godiya.
Daga can ɓangaren Salim ya sauke ajiyan zuciya, sai yanzu ya samu relief jin muryanta ba cikin yanayi na damuwa ba kamar yanda ya tsammata, kenan babu wata matsala saboda sosai ya damu da yanayin da yaga Abbaa a ɗazu, ya san dole zata sha faɗa kam, don faɗan da Abbaa ya dinga mata a lokacin ji yay kaman ya fito ya ba da haƙuri, shi kansa ji yay ba zai iya barinta ta tafi ita ɗaya ba a wannan daren shiyasa ya aje motarsa ya shiga napep ɗin domin ya san idan yace ta zo ya rage mata hanya ba yarda zata yi ba.
Ya sauke a jiyan zuciyayana aje wayarsa, tare da jingina kai a gadon ta gefen ƙwayar idonsa kuma yana kallon Kudrat da ke gefensa tana bacci.
******Bayan kwana biyu yau tun tashina Ummani tace da na gama komai na gyara ɗakin Al'amin akwai baƙin da za'a yi anjima. Ban tsaya tambayarta ba ni dai ina gama wanke wanke na shiga na gyara tass, na sanya turaran wuta me bala'in ƙamshi da nasa ordarsa daga meduguri. Gidan duka ya ɗauka har Ummansu Hindatu sai da ta leƙo tana faɗin kamar gidan haihuwa ko sabuwar amarya.
Ummani tace na shirya zan rakata unguwa, nayi wanka na saka rigar bubu sai ce tayi lallai sai na sauya in ɗauko abayata da na siya kwanaki mana. Na ce an gama ranki ya daɗe, haka na ɗauko na saka na zauna zaman jiranta sai ƙorafi na ke ina Ummani ki zo mu tafi kin san ba wuri ɗaya kike zuwa ba, an ta shige shige kenan yanzu za ki ga yamma tayi.
Tace kar na dameta in ban rakata Yasmin zata rakata. Ban ƙara magana ba na fito da keken ɗinkina tsakar gida na hau ɗinka kayan wasu da za'a kaiwa bauchi. Lokacin yaro ya shigo yana cewa ana sallama da Abbaa, na tashi na leƙa ɗakin na faɗa masa, babu jimawa ya fito ya fita, can ya kuma dawowa yace da ni na ɗauko masa tabarma. Da kaina na kai soro na shimfiɗa kana na dawo ciki.
Abbaa ya leƙa daga waje, tsaye ya hangi Salim jingine da motarsa hannayensa harɗe saman ƙirji, cikin kamilalliyar shigarsa ta cofee ɗin yadi da ɗinkin irin na yare, shigarsa tayi masa bala'in kyau. Abbaa dai murmushi ya suɓuce masa, tun asubahin yau ko kuma yace tun a lokacin da yay sujjada ga ubangiji a cikin dare yana me neman zaɓinsa akan lamarin Salim da Ƴarsa yaji fargaba ya barsa yayin da ƙwarin gwiwan aurama Salim ƴarsa ya shige shi, kuma a yanzu da idanunsa ke kan yaron sai yake jin yana samun salama a cikin ransa dangane da lamarin.
Yaywa Salim izinin shigowa, ya tako cikin tafiyarsa ta namiji me cikar zati da kamala ya shigo soron lokacin Abbaa har ya zauna akan tabarmar, ya cire takalma ya nemi waje ya zauna, zaman nasa ma har sai da Abbaa yace masa tukunna don da tsugunawa yayi cikin jin nauyin zama a inda surukinsa ke zaune. Ya gurfanar da kansa gaban Abbaa kamar me neman gafara, da girmamawa da ladabi ya sake gaida Abbaa a karo na biyu, Abbaa ya amsa ƙwayar idonsa ƙyam akansa tun a ɗazun.
Abbaa yay nisa tare da sauke numfashi ya kira yi sunansa. "Salim ka ke ko?".
"Ehhh Abaa".
"To ya kake ya aiki?". "Alhamdulillahi Abbaa, fatan na same ku lafiya". "Lafiya lau, Salim ko za ki iya faɗa min dalilin zuwanka wurina?". Da wani ƙwarin gwiwa da jarumta irin tasa ta sojan gaske yace,"Abbaa na zo gare ka ne da ƙoƙon baran ka bani amanar rayuwar ƴarka Sa'ida...".
Abbaa ya katse shi,"Amana dai Salim? Ka kuwa san amana?". "Na sani Abbaa, ni musulmi ne cikakke, kuma ina da yaƙinin zan riƙe amanar shiyasa na ce aba ni ita". "Salim amana tana da girma, wutar Allah na cin wanda bai riƙeta ba". "Bana fatan na kasance cikin sahun maciya amana Abbaa, ka yarda da ni zan riƙe amanar da zaka bani tsakani da Allah".
Abbaa ya sake cewa,"Kai ka turo iyayenka kenan ko kuwa sun yi zuwan kan su ne?". "A'a Abbaa ni naje musu da maganar". "Amma me yasa baka fara zuwa da kan ka ba? Ko kuma kana ganin kawai don mahaifanka sun zo sai na ce musu na baka ƴata? Shin ka taɓa neman soyayyarta ne?".
Ya ƙara yin ƙasa da kai kafin a hankali yace,"Bamu da ƙarfin ikon da zamu zo kai tsaye mu ce zamu ne abu a bamu ta yanda muke so, na fi so ne a duk sanda wani babban lamari ya shiga gabana na fara saka manyana a ciki, musamman sha'ani me girman gaske irin wannan. Sa'ida kuma ban taɓa tunkararta ba, kawai dai na san da cewa in har iyaye suka amince min na nemi soyayyarta da sannu...".
Sai yay shiru bai iya ƙarasa faɗin abin da zai ce ba. Abbaa yace,"Da sannu me? Yi min bayani ina jinka".
Ya sarƙe yatsunsa da ƙyar ya iya cewa,"In har ta bani dama na shiga sahun manema aurenta da sannu zan koyar da ita so...". Sai kuma ya canja kalamin da cewa,"Da sannu zata aminta da ni".
Abbaa ya jinjina kai sannan yace,"To amma kai da kake da iyali mene naka na son ƙara aure Salim? Ba ku zaman lafiya ne ko kuwa dai lamarin wasu mazan na son wulaƙanta matayen su ne?".
Abbaa yay maganar wajen bugun cikin Salim ɗin. A hankali kuma cikin natsuwa Salim yace,"Babu ko ɗaya Abbaa, ina dai da sha'awan ƙara aure ne domin ko addini ya bamu damar yin hakan, idan har muna da iko kuma zamu yi adalci zamu iya ƙara aure. Sannan zaman lafiya iyaka gwargwado akwai shi tsakanina da iyalina, bani da nufin na ƙara aure don na ci mutuncin iyalina, ba zan ƙara aure don na cutar da wani ɓangaren ba, lamarin aure abinda Allah ya nufa shi ke kasancewa". [2/2, 07:48] Hlm: *B3ƘR04FT5* "Masha Allah! Abbaa ya faɗa yana jinjina kai.
"Salim da gaske kake kana son ƴata tsakaninka da Allah ba domin wata manufa ba?".
"Ƙwarai Abbaa ina son Sa'ida ba tun yanzu ba, ko a wancan lokacin na haƙura ne saboda ta nuna bata sona, kuma ko a yanzu ma zan iya haƙura idan har ta ce ba zata iya aurena ba, ba zan zamar mata dole ba kamar yanda ba zan so ayi mata dole ba, ni dai burina ne auren nagartacciyar mace kamar Sa'ida, idan kuma hakan bata Faru ba na san da cewa Allah ne ya rubuta cewar ba zan rayu da ita ba a inuwa guda matsayin ma'aurata, kuma zan karɓi hakan a madadin ƙaddara".
Abbaa yay ɗan jim kafin ya sake cewa,"Ka san da cewa ita ba budurwa ba ce bazawara ce ƙaddara ya rabata da mijinta?".
"Na san da hakan Abbaa".
Abbaa ya ƙara mayar masa da cewa,"Fatan kowanne miji ne ya samu zuri'a tare da matar aurensa, Shekaran Sa'ida goma da aure bata taɓa haihuwa ba Salim".
Ya sauke numfashi kana cikin tattausan lafazi irin nasa yace,"Abbaa komai yin Allah ne, Haihuwa da rashinta dukka lamarin ubangiji ne, wataƙila ubangiji ya jinkirta mata lokaci ne wataƙila kuma bata ɗaya daga cikin waɗanda ubangiji ya tsara za su samu rabon hakan, Allah shi ne masani kuma shi yasan daidai na yanda ya tsara rayuwarta, kuma yanda ya tsara mata ɗin shi ne mafi alkhairinta ba don baya sonta cikin bayinsa ba...Abbaa ni Sa'ida na ke so zan kuma zauna da ita a kowanne irin yanayi babu cuta babu tsangwama babu kyara face cikin nuna kalawa da soyayya".
Abbaa ya murmusa, tun farkon fara maganarsu da Salim yaji yaron ya burgesa saboda irin lafuzansa da ke fita daga bakinsa a nutse, kalami na me kaifin tunani da sanin yakamata gami da hankali. Abunda ya sani lokacin da zai aurawa Sa'ida Nazifi bai ji zuciyarsa na ƙarfafa masa gwiwar hakan ba, haka bai ji aminci da salamar da yake ji a yanzu ba.
"Salim na amince maka ka nemi soyayyar ƴata, ka shiga layin zauwaran da suke neman auranta, idan har tayi amanna da kai ni kuma zan aura maka ita, zan baka amanarta, ina son ƴata ya kamata kan da wannan, ka rubuta hakan a tafin hannunka saboda gaba...sai dai akwai sharaɗi game da auren, idan ka amince faƙat idan baka amince ba to sai dai kayi haƙuri".
Salim da kansa ke ƙasa tun ɗazu yana murmushi me kyau saboda samun nasararsa ta amincewar da Abbaa yay masa, furucin Abbaan yasa shi ɗago kai ba tare da alamu na sarewa ko kuma karaya ba, domin kuwa yana da tabbacin zai iya bin kowanne sharaɗi ne muddin zai samu Sa'ida, sai dai sam ya kasa ko da kallon gefen da Abbaa ya ke kamar yanda yay niyya saboda girman kwarjinin da Abbaan yay masa.
Abbaa yace,"Ka shirya jin sharaɗin nawa?". "Ehh Abbaa".
"Yauwa! Sharaɗin shi ne ƴata tana aikin asibiti, da aikinta ka ganta saboda haka babu batun cewar idan ka aureta zaka dakatar da ita ma'ana zaka hanata zuwa aikinta, sannan tana burin ƙaro karatu anan gaba shima ba zaka hanata ba, bayan haka tana ƴan sana'ointa na hannu, ka yarda da wannan yarjejeniyar ko kuwa ya?".
Yay murmushin da sautinsa ya fita a ƙasan ransa, leɓensa kuma ya tale, to taya Abbaa yake tunanin cewa zai dakusarwa da Sa'ida karatunta ko kuma ya dakatar da ita aikinta? Idan da haka why zai shiga ya fita wajen ganin ta kawo wannan matsayin? Abinda yay mata don Allah yayi, kuma alƙawarinsa ne ba zata taɓa sanin hakan daga gare shi ba sai in Safiyya ce tayi katoɓarar faɗa mata duk da itama tayi masa alƙawari har abada ba zata sanar da Sa'ida ba shi ya ɗauki ɗawainiyar karatunta har matakin aikinta ba. Kuma ba ya so kowa ya sani ɗin domin za'a ga kamar yayi ne domin ya mallaketa, kuma itama with that reason zata iya zama with no other option ta tilastawa kanta saboda rama halacci da halacci.
"Abbaa na amince na karɓi sharuɗanka, ba zan zama me sauka daga kai ba, illa iyaka ma ni zan zama wanda zai ƙara tallafawa lamuran nata".
Abbaa yace,"Shikenan duk san da ka shirya kana iya zuwa ku gana da ita, amma bana so a ɗauki tsawon lokaci ana abu guda".
Wannan karan sai da Abbaa ya jiyo sautin sanyayyan murmushinsa na samun nasarar da yay. Yana kallon yacca ya gyara tankwashe ƙafarsa kafin ya shiga cewa,"Na gode sosai Abbaa, na gode da bani dama, kuma da yardar Allah ba zaka yi nadamar aura mini ƴarka ba, nayi maka alƙawarin riƙe amanar da ka bani da dukkan ƙarfin ikona, zan kula da ita bisa gaskiya da aldalci".
Abba ya murmusa kafin yace"Ina fatan hakan ta kasance, Allah ya baka ikon tsayawa a tafarkin da yake daidai, Allah yay maka albarka".
"Amin ya Allah Abbaa, Allah ya ƙara muku lafiya da tsawon cin kwana".
Shiru ya gimla tunanin Abbaa sun gama da shi ko zai tafi ne, amma sai yaga ya gyara zama yana aikin jujjuya yatsunsa, Abbaa dai kallonsa yake tayi da murmushi tare da fatan Sa'ida ta amince. "Za ka wuce ne?".
Salim na ƙara yin ƙasa da kai da ƙyar ya iya buɗe baki cikin jin nauyi yace,"Abbaa idan ba damuwa ko zan iya ganinta kafin na wuce?".
Abbaa ya yunƙura ya miƙe yana cewa,"Babu matsala ka ɗan jira".
Abbaa ya wuce cikin gida, kai tsaye ɗakin Ummani ya shiga, tana zaune ita da Walida tana tsefe mata kai ya same su. Ummani ta bisa da kallo tana faɗin,"To ya ake ciki?". Tayi tambayar da zaƙuwa.
"Yana jiranta sai ki mata magana, amma kin san bani son tsayuwan ƙofar gida".
Ummani ta saki kan Walida tana cewa,"Ahh ai dama tun da safe nasa ta kimtsa ɗakin Al'amin, ko kuwa su zauna a soron?".
Yay ɗan jima kafin yace,"Shikenan su zauna can ɗin".
"Ɗakin Al'amin ɗin?". "Ehh". "To bari na faɗa mata ta kimtsa ko".
Ta faɗa tana fita a ɗakin shi kuma Abbaa na tsokanar Walida da ƙwaƙwido, ta miƙe tana taɓara ya kama hannunta suka wuce ɗakinsa. Ummani na fitowa ta ƙwala kiran Yasmin wacca ke can wurin Kaka, sai gata da sauri ta fito tana zuwa Ummani ta bata maƙulli tace,"Je ki soro za ki ga baƙo ku gaisa ki buɗe masa ɗakin Al'amin kice an ce ya shiga, idan ba ya nan ki duba shi a ƙofar gida".
Yasmin ta karɓa maƙullin ta fita, a soron ta sameshi zaune yana karkaɗa maƙullan hannunsa, ta durƙusa tana gaida shi, bayan sun gaisa ne ta buɗe ɗakin kana ta dawo ta kuma durƙusawa gabansa tace,"Ummani tace ka shiga daga ciki". Yanayin ladabin yarinyar sai ya burge shi, yana mata murmushi yace,"Mene sunanki?".
"Sa'adatu amma Yasmin ake ce min".
Yace,"Umm nice name, kice ina gaida Ummani idan kin shiga".
Ta amsa da to daga bisani shi kuma ya miƙe ya shiga daga cikin ɗakin. Zamansa ba daɗewa Yasmin ta kuma dawowa ɗauke da farantin tangaran da jug da ƙananun kofuna akai sai purewater guda uku.
Ina zaune a ɗaki ina saka stones ɗin rigar dana gama ɗinkawa ɗazu, ban san me ya same ni ba tun a ɗazun dai na ke jina a cikin wani irin yanayi da na kasa gane masa. Abunda ban taɓa yi ba tun mutuwar aurena wai na zauna ina tunanin aure ko sha'awarsa, amma tunda na hau kan keke wani banzan tunani ke neman dagula min lissafi. Kuma rabon da inji a raina na tuna da tsohon mijina da irin rayuwar da nayi a gidansa wallahi tallahi har na manta, amma yau ni ce tunanin Nazifi ke zuwar min da jin cewa ina ma na haɗu da shi ya ganni yaga yanda na koma da kuma irin matakin da Allah ya kai ni, kuma har na ke sha'awar ina ma na samu mijin da zai goge min tabon da Nazifi ya bar min shi da ƴan uwansa.
Ummani ta shigo ɗakin da sassarfa tana cewa da ni,"Ke tashi yi da sauri ki gyara jikin ki".
To na san fita zamu yi dama, saboda haka na miƙe ina gyara fuskata, ina ta kallon Ummani da farin ciki a tare da ita nace,"Wai me ya faru Ummani naga sai murna kike".
"Aa to ba ki so kiga ina farin ciki ne?". "Ina ni, ai burina ku kasance cikin farin ciki a ko da yaushe".
Na faɗa ina sanya pin a jikin veil ɗin da na yafa na ke kallon Ummani da annurin fuskarta ke ƙaruwa na ce,"To Ummani ai ke ba ki shirya ba".
Tana murmushi me faɗi tace"Ai mun fasa waccan fitar, wannan shirin na ki ne ke ɗaya, kin gama?".
Nace,"Ehh to amma me yasa kika fasa? Allah yasa ba Abbaa ne ya hana ki ba kinga dai kar a kuma abin kunyar da aka yi aƙi zuwar Hajiya Tabawa gaisuwa".
Tasa hannu cikin jakata tana ɗauko turare ta buɗe tana ƙara feshe ni da shi kamar wadda akewa kamun aure tace,"Bar batun can ko gobe ma je insha Allahu, kije ɗakin Al'amin akwai baƙo ku gaisa da shi".
Da mamaki ƙarara na ke kallonta na ce,"Gaida baƙo kuma Ummani sai naje a haka, ina lefin hijabi ma".
Ta ɓata fuska tana kama hannuna,"To matar liman, yau dai ɗaya mene laifi a ciki, ba ki ga kyan da kika yi a hakan ba ne, duk wanda ya kalle ki sai ya ƙara kallonki yanda kika san balarabiya".
Murmushi nayi da har haƙorana dukka suka bayyana. "Allah kin yi kyau da gaske na ke faɗa miki, tsab sai kin daɗa sace zuciya".
Sai naji kunya ta kama ni, tare da sabon mamaki wanda na kasa samun haske a inda Ummani ta dosa. Tare muka fito a ɗakin ina aikin ɓata fuska don tunda tace baƙo naji sam ban son zuwa gaisuwar balle kuma a cikin shigar da na ke. Zungurar kai nayi ina faman jan ƙafafu takalmi na sharaf sharaf Ummani ta figo ni,"Wai ke ƙaramar yarinya ce, ya za ki tafi a haka".
Na rufe ido na buɗe ina karyar da kai na ce,"Ummani shin baƙon wajen wa ya zo ne?".
"Wurin ki ya zo, don haka ki natsu ki yi tafiya a yangance irin ta mace me tsada kamar ki".
Na ƙanƙance ido da cewa,"Baƙo ya zo wurina? Kuma Ummani kike ta murna? Ni ai na muka yi da wani zai zo wurina? Gaskiya ba inda zani idan ya gaji ya tafi". Na faɗi hakan da haƙiƙanin bɓacin rai a tare da ni ina nufin juyawa na koma ɗaki.
Harara ta wurga min tana cewa,"Idan ke baku yi da shi zai zo ba ai yayi da Abbaanku, na faɗa masa kin ce ba za ki ba ko ƙaƙa?".
Jin haka na turo baki gaba ina haɗe gira sama da ƙasa na nufi soro ba don son raina ba, sai dai me! da zuwana soron naji gabana yayi mugu mugun faɗuwar da sai da na kai hannu na dafa bango, haka kawai na tsinci ƙafafuna da yin karkarwa. Da ƙyar na dawo hayyacina daga fitar da nayi daga cikinsa na ɗan lokaci, domin kuwa ƙamshin turaren da ya gauraye dukka soron da kuma tsadaddan takalmin da idona ya sauka akai sai ya nemi ya burkita ni.
Na haɗiyi yawu ina cire takalmana a kusa da wanda na ke gani, ƙafafuna suka ɗaga da kansu suka shigar da ni ciki, da yanayina na sanyi nayi sallama da ƴar ƙaramar muryar da zata ɗauki hankali ko ai'na ne, kamar wata sokuwa haka na maƙale a bakin ƙofa kaina a ƙasa na kasa sarrafa kaina saboda yacca na ke jin ido ya manne akaina da kallo.
A karo na biyu na ƙara cewa,"Salamu alaikum". Ban sani ba ko an amsa a wannan lokacin domin kuwa kunnena a toshe yake dumm haka na ke ji a cikinsa tun ɗazu. Wucewar bugun zuciyata sau ɗaya, biyu, uku, huɗu naji kamar babu motsin halitta a ɗakin saboda haka na ɗago ido a tsorace, karaf ƙwayar idona ta sauka akansa da yay saurin sadda nasa kan ƙasa kamar ba daga kaina ya sauke kallonsa ba.
Zaune yake a gefen katifa, ya miƙe ƙafafunsa da na gansu dogaye, hularsa da ya cire ta yare a gefensa, yana wasa da yatsun hannunsa, kallonsa na ke da son na fahimto wani abu sai ji nayi na mugun tsorata dalilin jin ance,"Ga wani abu nan wajen ƙafarki". Ƙara na ƙwalla, kuma maimakon in yi waje sai na faɗo cikin ɗakin ba tare da sanin yanda aka yi na dira a tsakiyar ɗakin ba, idona rumtse jikina sai kyarma yake, cikin bakina ina faɗin kalmar la'ila ha'illa anta a hankali, saboda tsananin tsoro da furgicin da na shiga har hawaye na sakko min.
Na jima a haka na kasa buɗe idanuna, sai naji kamar an rufa min abu akaina wanda hakan yasa ni buɗe idanuna a hankali, sai naga mutum tsaye a gabana, faffaɗan ƙirjinsa yay min rumfar na zama kamar wata ɓeranya a gaban nasa ƴar firit, a hankali kunnuwana ke jiyo min sautin bugun zuciya wanda na tabbatar da haƙikanin ba nawa ba ne nasa ne, sai naji wani dunƙulallan abu ya wuce ta maƙoshina gabana na tsananta faɗuwa sosai, so na ke tayi na ɗaga ƙafata na matsa daga baya amma ina kamar akan tarko na maƙale sam na kasa motsa ƙafata ko guda ɗaya.
Cikin wani irin yanayi da na ke jina a cikinsa kasantuwar kusancinmu, na yi saurin ɗauke idona daga kan ƙirjinsa da na ke mamakin faɗinsa ina kai wa saman kamilallar fuskar da ta ƙawatu da kewayayyen saje me haɗe da gemu. Kuma karaf ƙwayar idon mu ta sarƙe ata juna, lokaci guda naji jiri na neman ɗibana ya watsar, nayi saurin dunƙule hannu ina riƙe kaina a tsayen, irin murmushin da ake kira da killer smile ya saki wanda sautinsa yay sanadin girgizawar allon ƙirjina nayi saurin ɗauke ƙwayar idona daga cikin tasa, ban saba da irin wannan kusancin ba sam da wanda ba muharramina ba, don haka kaina na ƙasa ina rawan jiki na shiga ja da baya yayin da ya daɗa kiɗima ni da amon muryarsa da ya fito lokaci ɗaya da cewa,"Am sorry ban tsammaci za ki tsorata da yawa haka ba, nayi hakan ne domin ƙafafun da suka maƙale wuri ɗaya su samu takowa zuwa ciki".
Ina micincina idanu na ce,"To baka san ko a addinan ce babu kyau tsorata musulmi ba".
"Tuba na ke yi ba zan ƙara ba daga ranar yau, amma ki sani kina da me ba ki kariya kar wani abu ya ƙara tsorata ki".
Ni dai ja nake da baya har na zube kan ƴar ƙaramar plastic chair ɗin ɗakin ƙirjina sai faman sama da ƙasa yake yi. So na ke na ɗaga ido na kalla fuskar da na yiwa kallo ɗaya saboda na tabbatar da zargina. Sai kuma ringtone ɗin iphone ya cika ɗakin, wanda da sauri naga ya matsa daga inda yake ya isa katifar ya ɗauka, sai jinsa nayi yana magana cikin wani irin yare kamar jagwalgwalo babu daɗin ji, duk sai naji maganar tana hawar min saman kai har ta kai ga na rufe ido ina gwame fuska.
"Ina wuni". Da sauri na buɗe idona ina dawowa cikin duniyar da na bari jin murya a gaf da ni, na kalle shi muka haɗa ido sai na kasa ɗauke kallona a kansa gaba ɗaya kuma na diririce. Zuciyata ta amsa da sunansa,"Salim!". Mutumin da na sani shekaru goma sha da suka wuce, mutumin da watannin baya da suka wuce naga hotonsa a album ɗin bikin Safiyya.
Naja numfashi inda na haɗe da ƙamshinsa da ke tsumani na zuƙe, sannu a hankali ƙamshin turarensa ya ɗebe ni ya kaini tunanin germany, sauka a airport, cikin napep. Ba tare da sani ba kawai na tsinci bakina da furta,"Kai ne?".
Sai naga ya ɗaga gira dukka biyu yana kallona kawai, kafin yace,"Ai na?".
Na tsuke gira ina tuna komai daki daki na ce,"A airpot ranar da na dawo, da kuma ranar ma a adaidaita".
Sai ya lumshe ido yana girgiza min kai alamun a'a. Na ɗan duki ƙafa a ƙasa na ce,"A'a wannan ƙamshin ne".
Ba zan ce ga da irin muryar da nayi magana ba don ba zan iya tantancewa ba, amma sai naji ya kwaikwayi muryan da cewa,"Ba wannan ba ne, irin wannan ɗin ne".
Kawai sai kunya ta kama ni na kai hannu ina rufe fuska, har ga Allah nema na ke na kasa controlling kaina ba don komai ba sai saboda ƙamshinsa da shi kansa da cikar haibarsa tayi gama gama da ɗakin musamman da yake zaune a gabana. Dariya naji yayi ƴar ƙarama yana maimaita gaisuwar da yayi. Sai na ɗan saci kallonsa, ni ya kamata ace na gaida shi ai to amma ta ya zan samu sakewar hakan mutum babba na zaune a gabana kamar yarona?
"Ba za ki amsa ba?".
Sai na samu kaina da cewa,"Ai kana zaune a gabana kuma ni ya kamata na gaishe ka".
"Ni dai a amsa mini domin kuwa cancantar Sarauniya ne da isarta a duƙa a gabanta a gaida ita, musamman ga mutumin da ya zo da ƙoƙon bara".
Tsintar kalamin nasa nayi har ɓargo da jijiyoyin jikina, kuma kafin na ankare sai gani nayi ya haɗe hannayensa alaman roƙo gami da ɗan karayar da kai yana cewa,"Please a amsa min, domin a ƙage na ke da na miƙo ƙoƙon barana bani a karo na biyu".
Baki na buɗe ganin yacca yay da fuska kaman ƙaramin yaron da ke shagwaɓar ayi masa abinda yake so. Sai ya miƙo hannunsa yay kamar zai zura yatsa cikin sakakkun laɓɓana nayi saurin kauda fuska gefe cike da kunyar da ta kama ni, domin kuwa surar fuskarsa ce ta ɗauki a hankali, kallon da ban samu damar yi masa a wancan lokacin ba, dama wannan kyan ne Safiyya take ta faɗa min? Amma kuwa idan haka ne Allah ya saka masa domin me hoto ma ya rage masa kyau sosai da sosai.
Yunƙurawa nayi zan tashi yay saurin dakatar da ni,"Please koma ki zauna". Ya faɗi hakan yana gyara zaman tanƙwashe ƙafafunsa tare da mayar da yanayinsa na masu magana da gasken gaske. Sai na ce,"To don Allah ka tashi a gabana".
Wani kallo yay min yana sosa gira sannan yace,"Ni fa ki ƙyale ni a yanda kika ganni, ki zauna kawai muyi magananmu, ba dafa ki zanyi na cinye ba, in ma zan yi hakan tukunna dai. Muhimmiyar magana ce ta sani na ke zaune haka a gabanki saboda haka koma ki zauna, idan kuma salon zaman ne bai ba sai na gyara".
Ya faɗa yana ƙoƙarin miƙewa ya dire gwiwoyi a ƙasa. Da sauri na shiga girgiza masa kai ina cewa,"A'a du Allah". Komawa nayi na zauna kamar me koyon zaman, shi kuma ya shafo fuska yana girgiza kai kafin yace,"Zan iya sake gabatar da kaina?".
Kai kawai na kaɗa masa alaman ehh. Da yanayin barkwanci yace,"Awwa Allah sa dai kar ki ce wannan ya fiya naci kamar in mammake shi".