Kenza eBookz

Ƙayar ruwa book 2 and 3 complete - Chapter 25

Ƙayar ruwa book 2 and 3 complete - Chapter 25

Ƙayar ruwa book 2 and 3 complete Chapter 25: Ƙayar ruwa book 2 and 3 complete Chapter 25. Furucin ya ban dariya na ɗan dara kafin kuma na haɗe rai. Kuma…

4,471 words

Furucin ya ban dariya na ɗan dara kafin kuma na haɗe rai. Kuma sai ji nayi yace,"Ki gama haɗe haɗen ranki indai za ki buɗen ƙofa shikenan. Anyway kamar yanda na faɗa miki a baya ne My name is Salim Sadiq Oluwa, ni ɗan ƙabilar igbo ne.....".

[2/2, 07:47] Hlm: *B3ƘR02FT5* Ƙaramin yaro ya shigo gidan yana cewa,"Salamu alaikum a bada zoɓo".

Ummani da ke daga cikin ɗaki tace,"Ana zuwa". Ta fito daidai lokacin tana tambayarsa,"Na nawa?".

"Na ɗari, wai don Allah a bada na roba me kyau".

Tayi murmushi tana cewa,"Ai duk masu kyau ne". Tana saka masa cikin leda wani yaron ya kuma shigowa yace,"Akwai kunun aya?". Tace,"Babu sai gobe idan Allah ya kaimu".

Ta sallami me zoɓo Kaka yace mata,"Me yasa ba ku yi kunun ayar ba bayan kun san anfi son sa".

Tace,"Jiya ne Sa'ida ta dawo a gajiye bata samu damar yi ba".

"To amma ke da ba sai kiyi ba". "Kaka hannun jikar taka sirri ne da shi, akwai zaƙin hannu idan tayi wallahi yafi nawa daɗi".

Kitchen ta shiga ta ɗauko abinci a ƙaramin filas tace da Kaka,"A shigar maka da shi cikin ɗakin ko anan zaka ci?".

Ya gyara zama daga kishingiɗen da yake yace,"Bar min anan cikin ɗakin zafi, nepa sun hana wuta yau".

Ta ajiya masa ta ɗauko ruwa ta aje masa, shi kuma yana ta saka mata albarka don shi kansa kaf matan ƴaƴansa yafi son Ummani, a ko da yaushe yabonta yake yi domin ita ɗin macece ta ƙwarai, yanda take masa tamkar shi ya haifeta. Yashaik ya shigo gidan, a nan tabarmar da Kaka yake ya zauna suna gaisawa, kafin daga bisani ya miƙe ya shiga ciki wurin mahaifiyarsa.

Samunta yay ta fito da kayan sif ɗinta dukka tana linkewa, daga gefe ya zauna yan agaishe da ita ta amsa tana tambayarsa ya iyali. "Me makon ki aika a kira miki Maman Yasmin, yanzu ina ke ina aikin ninkin kaya masu yawa haka".

"Ku dai kun fi so kuyi ta gani na kwance sharaf wuri ɗaya bana aikin komai, haka kawai kuma yarinya na can gidanta tana aikinta sai na aika a tasota, a'a kayan nawa suke gaba ɗaya yanzu zan gama ai. Yau babu in da kaje kenan?".

Ya sauke numfashi yace,"Ban leƙa ko ina ba, gani nayi gwara in ke hutawa lahadin jiki na buƙatar hutu".

"Haka ne, Allah daɗa rufa asiri. Jiya naji ka ce zaku yi magana da Abbaan ku sai ban ga ka dawo ba shiru, ba dai wata matsalar ba ce ko?".

Ya kai hannu yana shiga tayata linkin kayan yace,"Da na ƙyale ne kawai saboda na san ko naje masa da zancen ba karɓa zai yi ba, wataƙila ma raina ya iya ɓaci, sai dai ko ke za ki faɗa masa".

Ummani ta mayar da hankalinta kansa sosai tace,"Menene fa?".

Yace,"Ba fa matsala ba ce". Ya faɗa yanda yaga mahaifiyar tasa ta kafe shi da idanu.

"Dama akan Sa'ida ne ban san me Abbaa ke hange ba da yaƙi bawa zaurawan nata dama, haka kuma gaba ɗaya bai son zancen auren nata ba, amma ni gani na ke bai kamata a biye mata ba, duk da cewar dole auren ya sire mata, amma ai ba zamu ɗauka cewa lallai abin da ya faru a farko shi zai kuma faruwa ba ko kuma yayta maimaituwa, kawai ta ɗauka hakan matsayin jarabawarta ba wai saboda dalilin hakan kuma tace ita ba zata ƙara yin wani auren ba. ita macece ko ai na take ko me take yi duk matsayin da take da shi da aurenta tafi daraja a idon duniya, kuma ku kan ku idan da aurenta hankalinki zai fi kwanciya, kuma sannan shekaru tafiya suke ta yi gaba ba dawo baya zasu yi ba, nan da wata shekarar magana ake ta zata shekara talatin idan da rai da kuma lafiya, to ta gama karatun ta samu aikin yi me za'a ƙara jira Ummani? Baka biyewa maganar mutane balle ta dameka amma ana gudun baki, wani bakin kaifi ne sune masu kambun baka, ni gaskiya na fi ga sha'awar tayi aurenta, ba duka aka taru aka zama ɗaya ba ta dage da adu'a kawai Allah kar ya maimaita mata irin mijin baya".

Ummani ta numfasa tace,"Ni kaina da ka ganni wlh yanzu hankalina yafi ga tayi auren, Sa'id idan ta fita aikin wannan wallahi sam sam bana samun natsuwa har taje ta dawo hankalina ba'a kwance yake ba, amma lokaci ne duk dai Abbaan naku na daƙile damar hakan, Allah dai ya kawo mata na gari ya musanya mata da mafificin alkhairi".

"To amin ya Allah. Kuma dama Nura ne yay min magana ɗazu da safe yace abokinsa Ya ganta yace idan ba'a tsayar da maganar wani akanta ba ya gani yana so".

Ummani tayi murmushi me faɗi tace,"Allah sarki, ai na yake to?".

"A can garejin ma su yake shima, kin sansa ma sai dai ba za ki gane shi ba, amma da sallah ƙarama tare suka zo da Nuran ai".

Tace,"To madallah, ai ina ga sai kace masa ya tunkari Abbaan na ku da maganar ko, ya gwada tasa sa'ar ko a kansa dacen yake".

"Ehh to dama ni abin da ma yasa ban masa maganar so na ke na fara bugar cikinta naji ko tana da ra'ayin auren me ƴaƴa".

Ummani tayi gajeriyar dariya tace,"To ita wanne zaɓin saurayi ne da ita yanzu, sai dai kuma wani lamarin na Allah, fatan dai Allah bata wanda yafi wancan".

Da haka suka ci gaba da hirarsu akan maganar Al'amin ma da za'a kai kuɗin aure cikin satin nan, har sai da suka ninke kayan dukka. Shi ya share mata ɗaki ya goge ko ina, yay mata sharar tsakar gida da kitchen suma duk sai da yay mopping, dama sun saba hakan shi da Imam duk sanda suka sameta tana aiki, don shi da yake kusa da suma da sassafe yake zuwa yay sharar soro da ƙofar gida. Bayan tafiyarsa yana zuwa gida kuwa ya aiko mata Yasmin wadda ta shigo tana ta ƙunci wai Kawu yace ta zo tayi wanke wanke.

Da yamma yaro ya shigo tsakar gida yana ta doka sallama babu wanda ya amsa, Ummani na daga cikin ɗaki a kwance kamar a mafarki taji sallaman wajen ƙofan ɗakinta, tayi saurin tashi tana cewa,"waye ne?".

Yaron yace,"Ai ko ni aka yi, wai ana sallama da me gidan".

Labule ta ɗaga ta leƙo tana cewa da shi,"To masu gidan ai da yawa, kaje kace wa ake nema?".

Ba jimawa ya dawo yana cewa,"Wai Malam Salman".

Ummani tace,"Tooo wallahi ba ya nan, amma kace musu yana kan hanyarsa ta dawowa ko zasu jira shi, suna da yawa ne?".

Yaron yace,"Ehh mota biyu ce har da sojoji".

Gaban Ummani ya yanke ya faɗi ya bada rasss, tayi saurin dafe ƙirji tana faɗin,"Sojoji kuma ɗan nan? An ya ba makuwa ka yi ba kuwa, ko can ɗaya gidan aka aika ka kusa da me kayan miya".

Yace,"A'a ni dai nan suka ce min". "To shikenan je ka kace musu bai dawo daga kasuwa ba sai dare".

Yaron ya juya ya fita ita kuma ta dawo cikin ɗaki, ta kasa zaune tayi tsaye tana tunanin lafiya? Me zai kawo sojoji neman Abbaan su? Sai tayi maza ta ɗauki wayarta ta yiwa Sa'ida flashing, Sa'ida ta biyo bayan kiran, ta ɗaga tana ce mata,"Ke sako min kati zan kira Abban ku".

Yanayin fitar muryan nata yasa Sa'ida cewa"Lafiya Ummani?". "Lafiya lau sauri sako min zan ba shi sallahu ne a kasuwa kar ya riga ya taho".

Within one minutes sai ga shigowan katin ɗari biyar a wayar, ta lalubo sunan Abbaan Sa'id ta kira. Abbaa a lokacin na bakin titi ya ɗaga kiran wanda hayaniyar ƙarar ababen hawa bai barin sa yaji me take cewa itama ɗin kuma bata jinsa sosai, haka tayi ta faman kira ƙarshe sai haƙura tayi, ta fito tsakar gida ta zauna tayi jugum, har sai da ta leƙa ƙofar gidan taga tabbacin maganar yaron, soja ɗaya na tsaye bakin mota da bindiga a hannu, wannan fa yasa ta daɗa tsurewa ta kama safa da marwa a tsakar gida tana ta faɗin Allah sa lafiya.

Bayan kusan rabin awa sai ga Abbaa ya shigo gidan a gaggauce yana ƙwala kiran,"Sa'a! Sa'a! miƙo min babbar tabarma maza maza".

Irin yanda yake ƙwala kiran bana lafiya ba, Ummani ta fito daga ɗaki fuskar hijabi a juye jiki duk sai ɓari yake yi, ganin yanda Abbaan yake shima da ruɗani ta tsaya tambayan,"Abbaa lafiya? Kaga baƙin ƙofar gidan ne kaima?".

Bai amsa mata ba yaci gaba da ɗauraye ƙafarsa da duk tayi ƙura tare da wanke fuskarsa ma. "Ni dai sauri miƙo min tabarmar tukunna, ni kaina ba na ce miki lafiya ko ba lafiya ba Sa'a, amma hankalina duk ya tashi".

"Abbaa to kaje wurin su kuwa? Ko na aika a kira Yashaik yau yana gida bai fita ba".

"A'a ƙyale su Sa'a, bara na fara jin me ke tafe da su sun ce sun jima waje, maza miƙo min tabarmar dai, kin san irin mutanen ba'a barin su da jira".

Ganin ta tsaya kawai ya wuceta yay ɗakinsa ya buɗe ya yayibo tabarma ya fito yay waje da hanzari, duk ya rikice tafiyar tamkar zai kifa ƙasa. A soro ya baza ƙatuwar tabarmar, takalamansa ma a baibai ya saka ya leƙa yana ce musu,"Bismillah ku shigo daga ciki".

Zatonsa iyaka waɗannan sojoji biyun na waje ne sai yaga an buɗe mota manyan mutane dattawan arziƙi suna fitowa, da kallo ɗaya ba sai ka ƙara na biyu zaka shaida duniya ta san su ta san da zaman su, matsayi kuma an same shi sai wanda ake kan rabawa, kuma masu faɗa ne aji a ƙasar da suke ciki. Sojojin na basu kariya har suka shigo soron wanda duk Abbaa ya daɗa hargitsewa yana duban tabarmar da duk ta ɗan sha jiki, da shi kansa soron gidan wanda yake ganin sun girmi su ko rakuɓe a cikinsa balle zama.

Sai dai ga mamakinsa babu wani yanayi na ƙyama ko jin kai a tare da su, duk sai yake jin wani iri, bai taɓa yin baƙo yana jin ya ƙasƙantar da shi duba da irin muhallinsa ba sai waɗannan mutanen.

"To ko kujera za a samo muku?".

Ɗaya daga cikin su yace,"A'a babu komai Malam, ai nan ɗin ma Alhamdulillahi ya isa, ga shi duk mun zauna, muna godiya da karramawa".

Sai da duk suka gama zama sannan ya zauna yana mai fuskantarsu, ya ranƙwafa kamar bafaden sarki, da firgicin da ke tare da shi ya shiga miƙa musu hannu wanda a farko sai da yaji shakkar hakan, sai kuma yaga saɓanin fa yanda yake tunaninsu ne domin da kansu suka miƙo masa nasu suna gaisawa da girmama junansu da kuma mutuntawa. Cikin wani yanayi Abbaa da bai taɓa shigansa ba yake kallon tsohon mutumin da ke cewa da shi,"Da ka natsu naga duk ka dabarbarce da ganin namu".

Abbaa yace,"To ai ranka ya daɗe ganin mutane irinku dole mutum ya shiga irin wannan yanayin na ruɗani, ni dai fatana Allah yasa lafiya, Allah yasa lafiya don cikin gida ma kanta iyalina a tsaye take".

Alhaji Sama'ila ya murmusa yana duban Abbaa da kyau yace,"Kar ka samu damuwa lafiya lau, Alkhairi ne ya kawo mu gare ka, saboda haka ka bar tunanin ko ba lafiya ba ne".

Sai sannan Abbaan ya samu ya ɗan sauke ajiyar zuciya ta salama yace,"To masha Allahu, bara a miƙo muku ruwa".

Ya yunƙura zai miƙe sai ga wani baƙon ya shigo, Abbaa ya kalle shi cikin faɗaɗa fara'ar fuskarsa yay saurin miƙewa yana miƙawa Baba hannu yace,"A'a Alhaji Babangida kai ne da kanka a gidan nawa, barka da zuwa".

Baban su Safiyya shima cikin fara'ar da ke wadatuwa saman fuskarsa yake cewa da Abbaa,"Malam Salman ka ganni kwatsam ko, to ya za'ai zuwa ya zamar mana dole".

"Wallahi fa, kar dai kace min tare ku ke da waɗannan bayin Allah'n?".

Baban su Safiyya yace,"Tare muke da su, da yake ni uzuri ya ɗan riƙe ni a hanya ne shiyasa suka riga ni isowa, tafiyar ai tawa ce ma gaba ɗaya, na ke ce musu ai gida muka nufa su isa kafin na ƙaraso".

Baban su Safiyya ya nemi waje ya zauna yana magana da jama'arsa, yayin da Abbaa ya shiga daga cikin gidan yana kiran sunan Ummani a hankali saboda ana iyo jiyo maganar tsakar gida daga soron. Ummani kuwa na kitchen a lokacin ta rafka tagumi tana jinsa ta taso da sauri tana buɗa masa hannu alamun ya ake ciki.

"To bana ce ba amma dai sun ce lafiya lau alkhairi ya kawo su, don tafiyar ma har da Alhaji Babangida".

"Alhaji Babangida dai?". "Baban yarinyar nan ƙawar Sa'ida, bani sunanta nan, yauwa Safiyya".

Ummani ta sauke nauyayyan numfashi da cewar,"Ohhh har na samu Sa'ida amma da hankalina duk ya tashi ina ta tunanin me zai kawo mana sojoji wajenka, don wallahi har na fara zargin ko matsalar rumfar nan ce".

Yanayin fuskan Abbaan dai gata nan yace,"Samu faranti ki zubo lemu da ruwa".

Ummani ta koma kicin ta ɗauko farantai guda biyu, shi kuma Abbaa ya shiga ɗakin Sa'ida inda firiji ke ajiye ya kwaso kunun aya da ruwa. Yasmin ta shigo Abbaan ya bata faranti ɗaya yace ta kaiwa baƙin waje, Ummani kuma na cewa da shi,"To ai kai musu waɗancan kofunan robar kuwa? Da dai an bar musu a jarkunan? Ko na aika Yusra ta bada kofunan tangaran ɗinta".

"Bar shi akai musu hakan ai sun san inda suka zo". "To shikenan Allah sa khairan ɗin da gaske".

Ta faɗa tana bin bayan Abbaa da kallo har ya fice. Kafin ta shiga daga ɗaki tana cewa bari ta kira Sa'ida ta faɗa mata ko zata siyo kofunan ƴan gayu a hanya saboda zuwan manyan baƙi irin haka, ranar nan ma haka ta zo da ma'aikatan asibitinsu duk sai taji kunya saboda irin farantin da aka zuba musu abinci, to da yake dai baka kunya da matsayin da Allah ya aje ka.

Abbaa ya zauna suna ƙara gaisawa da juna, bayan an taɓa ƴar hira tsakanin Abbaa da Baban su Safiyya sai Alhaji Surajo ke cewa,"Tom Babangida kayi masa bayanin me ke tafe da mu ko".

Baban su Safiyya na jijjiga kai yace,"Ƙwarai haka ne, bama biyewa hirarmu da ba zata ƙare ba, zumunci yay ƙaranci wai don ma Allah ya haɗa kan ƴaƴan namu sunata na su zumuncin".

Abbaa yace,"Wallahi fa Alhajin Allah, da sai a wuce shekaru masu yawan gaske ma ba'a gaisa ba ko ta wayar, zumuncin zamanin sai adu'a sai mutum yayi da gaske zai samu ladansa".

Baban su Safiyya ya numfasa kana ya dubi Abbaa yana yi masa nuni da babban mutumin da ke tsakiya me cikar kamala da dattako, wanda Abbaa zai iya cewa dama tun zuwansu yaji mutumin ya cika wurin da haibarsa, kuma yana da tabbacin ƙamshinsa ne ya gauraye dukka wajen tun daga ƙofar gida har cikin gida.

A hankali Baban su Safiyya yace,"Malam Salman wannan shi ne Major Sadiq Oluwa Ibrahim, Yayar Matata ne uwa ɗaya uba ɗaya domin a wurinsa ma na karɓi auren ƙanwarsa, na kusa da shi kuma kusan mahaifi ne a wurinmu sunansa Captain Adebisi Oluwa...waɗannan kuma duk da kake gani abokai ne sai wancan". Ya faɗa yana nuni ma Abbaa da na kusa da shi yace,"Shi ƙane ne a wajen Major, sunansa Alhaji Mukhtar Oluwa".

Abbaa yana ƙara rissinar da kai yace,"To masha Allahu, madallah dukkanku ina ƙara yi muku maraba, ayi haƙuri dai da irin wajen da aka samu".

Captain Adebisi yace,"A haba dai haba dai muma duk irin namu muhallin kenan".

Baban su Safiyya ya ƙara cewa,"To Malam Salman abin da yake tafe da mu muhimmin abu ne, magana ce babba, kuma alkhairi ne ya kawo mu gareka, sai dai bamu san a yanda zaka karɓi al'amarin ba, duba da cewa mun sake dawowa ne a karo na biyu da buƙata iri ɗaya, amma a wannan karan muna fatan samun karɓuwar tayin mu saɓanin baya da bamu samu karɓuwa ba".

Abbaa yace,"To Alhajin Allah a ɗan warware ni ko, an saka ni a duhu". Ya faɗu haƙoransa a waje fuskarsa washe da fara'a.

Major Sadiq wato Sir kamar yanda ƴaƴansa ke kiransa yay nisa tare da numfasawa, yana daɗa kallon fuskar Abbaa da ke kama da ta Sa'ida sak wadda ya gani a cikin jirgi ranar da zasu kaita makaranta, kafin ya fara magana a cikin birkitacciyar hausarsa ta yarabawa yace,"Ammm Malam Salman mun zo wurinka ne a dalilin Yarona, wato dai mun zo nema masa auren ƴarka da ya gani yake so, idan ba'a rigada an tsayar mata da mijin aure ba shi yana da buƙatar aurenta, aure nan kusa ba tare da anja lokaci ba".

Abbaa ya ɗaga kai a karo na biyu yaywa Major kallo na ƙurulla, sai kawai yaji kwarjinin mutumin ya dake shi, haka kuma nauyinsa ya kama shi, yay saurin ɗauke ƙwayar idonsa akansa yana me ƙara sunkuyar da kai ƙasa yace,"Ina sauraronka Ranka shi daɗe".

Major yaci gaba da cewa,"My son Salim na ɗaya daga cikin manema auren ƴarka a shekarun baya masu yawa da suka wuce, to kuma sai ubangiji ya ƙadarta cewa ba zata zama matarsa ba a wancan lokacin, shi ne a wannan karon ya turo mu gare ku da ƙoƙon bararsa yace a taimaka masa idan har wani bai riga shi ba".

Kan Abbaa ya ɗaure, kafin ya kalli Baban su Safiyya yace,"Alhajin Allah ni ai har yanzu na kasa shaida ɗan namu da kuke magana akai".

Baban su Safiyya yace,"Ehh to da yake a wancan karan ba mune muka zo ba gaskiya, amma ai ba zaka mance yaron da ya kawo kuɗin aure daga baya kuma aka karɓa da cewar ba zai iya jiran yarinya ta kammala karatun da aka ce masa ba, wanda kuma hakan ta faru ne duk ba da son ran zuƙatan kowa ba musamman shi yaron".

Abbaan yayi ƙayattacen murmushi da cewa,"Na tuna, na tuna hakan, to amma shi da yay wancan magana a lokacin baya ai ce na ke an wuce babin...".

Sai yay shiru kamar yanda duk suma suka yi shiru suna kallonsa. Zuciyar Major cike da fargaba da zullumin kar su ƙi amsar tayin su, don shi kansa ya kwaɗaitu wa ɗansa auren Sa'ida. A lokacin ne kuma aka yi kiran sallar magriba, don haka duk suka miƙe Abbaa ya shiga gida Ummani ta zuba ruwa a buta guda biyu ta ba shi ya fita da ita, ta aika Yasmin wurin Umman su Hindatu ta ƙaro buta aka ƙara musu kafin Abbaan ya dawo ya karɓa masu sallaya, ita dai Ummani ganin yanayinsa na yanda yay sanyi kamar jikinsa ya mutu sai duk ta shiga damuwa da fargaba, tana tayi masa magana ma bai tsaya ya saurareta ba.

Don haka da sauri ta ɗauka waya ta kira Yashaik tace idan yana gida yay sauri ya leƙo gidan. Ko a wajen sallah ma babu yanda Abbaa bai yi ba akan wani cikin su ya ja su sallar suka dage masa akan lallai shi ne zai ja su, haka yaja su sallar bayan sun idar kuma suka komo soron suka zauna, Abba ya amso fitila a cikin gida ya saka musu saboda soron yayi duhu a lokacin.

Bayan zaman nasu Alhaji Mukhtar yace,"Malam Salman na san kana tunani ne akan abun da ya faru a baya ko, to idan wannn ne kar ka damu, wallahi tallahi ko a baya Salim ba ya janye maganar aurensa da ƴarku ba ne saboda dalilin da aka faɗa, hasalima danne zuciyarsa yay ya haƙura a babu yanda zai yi saboda nuna masa da tayi na bata sonsa, shi kuma bai zai iya auran macen da bata sonsa ba, yana ganin idan ya nace aka yi auren zaman ba zai yi musu daɗi ba, saboda wannan dalilin a lokacin ya zo ya same ni muka yi magana ya faɗa min duk yanda suka yi da yarinya har ma ya fahimci akwai wanda ita take so, amma bai karɓi kuɗinsa don yay wulaƙanci ko tozarci ba, kum ahatta maganar da akayi a lokacin na cewa ya samu wata matar wallahi a lokacin babu wannan zancen anyi hakan ne duk don samun mafita".

Abbaa ya sake jinjina kai kafin yace,"To da wannan da wannan, don bayanin da ka min yanzu shi ne nake so na tambaya. Sai dai duk da haka akwai wani hanzari ba gudu ba, ƴata ba budurwa ba ce yanzu bazawara ce ita, wataƙila kuma bai san da hakan ba ne".

Baban su Safiyya yace,"Ya sani Malam Salman, ya san komai, sannan shima ɗin ba wai saurayi ba ne da aurensa, bayan aure ma har da arziƙin yara uku...". [2/2, 07:47] Hlm: *B3ƘR03FT5* Abbaa yay shiru yana nazarin kalaman na su, ba zai ƙi tayinsu ba, domin shi kansa ko a wancan lokacin Salim ya kwanta masa a rai, yafi gamsuwa da shi fiye da duk waɗanda suka zo neman auren Sa'ida, shiyasa ko a lokacin ya yarda ya amince aka karɓi kuɗinsa bisa sharaɗin da ya gindaya na cewar sai ta kammala makaranta, kuma ko a sanda suka zo karɓar kuɗin su bai ji daɗi ba fiye da adadin kalmomin baki, ba wai rashin jin daɗi na sun wulaƙanta su ba kan karɓar kuɗin ba, a'a rashin jin daɗin Ƴarsa ta rasa yaron kirki, yaro me nagarta kamar Salim, yaga haƙiƙanin soyayyar ƴarsa a ƙwayar idon yaron, haka ya tsinci raunin rasata a muryarsa, kuma gamsu ɗari bisa ɗari da irin shaidun da mutane suka yi akansa, ba tare da sanin iyalinsa da kowa ba ya ɗauki ƙafa yaje har garin Anambra state domin yayi kyakykyawan bincike akan yaron da iyayensa kuma duk suka samu shaida mai kyau, dama tsoronsa ɗaya bawa ƙabila auren ɗiyarsa.

To a lokacin da ace shi irin mahaifin da ke tilastawa ɗiyansa abin da yake so ne ko da basa so, to da lashakka Sa'ida bata isa ta auri wani miji bayan Salim ba, to sai dai babu yanda zai yi shi uba ne me son farin cikin ƴaƴansa kuma me son dukkan abin da suke so ko da shi ba ya so in har wannan abu bai kaucewa shari'ar musulunci ba.

A yanzu tarin tambayoyi ne a ransa to amma zai bar su bincikensa ya ba shi amsa, akwai dai damuwa da fargaba a tare da shi. Major ya katse tunaninsa cikin magana me taushi irin ta dattijon arziƙi, yace,"Malam Salman Safiyya ita ta tabbatar mana da babu maganan wani akan ƴarka, bisa wannan dalili muma muka ga ya kamata muyi gaggawan zuwa kar mu makara. Kuma ni da kaina ina baka tabbacin insha Allahu my Son zai kula da ƴarka ba zai ci mutuncinta ba, yaƙini na ke baka akan hakan saboda na san waye yarona".

Da irin waɗannan maganganun Major ya ƙarfafawa Abba gwiwa. Wanda har Abbaa ya dinga jin zuciyarsa na buɗewa da yarda gami da farinciki, sai dai ba zai zama me fatan lamarin ya kasance ba har sai yayi istikara ya kuma sa Sa'ida tayi istikara itama.

Abba yay nisa sannu a hankali ya fara magana da cewa,"Tom ni babu abin da zance sai Allah ya zaɓa mafi alkhairi wa yaran namu. Sannan kamar yanda na faɗa muku ne Ƴata ba budurwa ba ce bazawara ce, saboda haka ni ban da hurumin da zan mata zaɓi kai tsaye domin kuwa shari'a ta bata damar yiwa kanta zaɓi".

Alhaji Mukhtar ya jijjiga kai da cewan,"Wannan haka yake Malam Salman, magana ce me kyau kayi".

Abbaa ya sake cewa,"To madallah, saboda haka ku faɗa masa cewa ya zo ya fara samuna domin ina da buƙatar na gana da shi kafin na basa damar ganawa da ita ƴar tawa su sasanta kansu".

Major shi ya fara cewa,"Tom shikenan zai zo ɗin in Allah ya yarda, muna godiya".

Gaba ɗayansu kuma sai suka shiga yima juna godiya kafin suyi sallama su miƙe zasu tafi, Abba ya shiga ciki ya karɓo leda wurin Ummani yazo ya kwashe kunun ayar da ruwan ya zuba musu a ciki ya raka su da shi har mota. Kamar yanda suka ji daɗi suke ta godiya da irin karramawar da Abbaa yayi musu haka shima ɗin yake ta godiya a gare su. Bayan tafiyar su ya wuce masallaci bai dawo cikin gida ba sai da yayi sallar isha'i.

Ya shigo a lokacin Ummani na daga ciki tana lazimi, yay ɗakin nata ya zauna daga bakin gado, kuma zuwan nasa yasa Ummani idda lazimin nata tare da juyowa ta fuskance tana nazarin yanayin fuskarsa kafin tace,"Abbaa lafiya dai ko?".

Abbaa na duban labulen ɗakin kamar me son karanta wani abu a jikinsa yace da ita,"Ehh to lafiyar zamu ce".

Furucinsa nasa yasa gabanta faɗuwa, ta ɗaga hijabinta ta cire tana aje carbi ta tashi daga kan dardumar ta dawo kusa da shi ta zauna. "Wani abu ne ya faru? Shi Alhaji Babangidan me ya kawo shi kuma mene haɗinsa da su mutanen?".

Ganin duk ta ruɗe Abbaa yay murmushi yana me ɗora ƙafarsa ɗaya akan gado ya fuskanceta, fuskarta ya shafo tare da cewa,"Kwantar da hankalinki matata ta kaina, Sa'adatun Salmanu ba komai ya kawo su ba face alkhairi".

Ummani ta sauke doguwar ajiyar zuciya tana karayar da kai kafin tace,"Yanzu naji batu, amma da hankalina gaba ɗaya a tashe yake, wallahi ka ganni tun da na zauna Allah na ke ta faɗawa, to ai Alhamdulillahi tunda ba wata matsala ba ce, amma me ya kawo su?".

Abbaa yace"Zuwan na su akan Sa'ida ne".

Cikin mamaki Ummani tace,"Sa'ida kuma? Na shiga duhu me ya faru da Sa'idan?".

"Kinga samu nutsuwa don Allah, zuwa suka yi da batun aurenta...".

Bai ƙarasa ba ta katse shi,"Kamar ya ban gane ba, shi Alhaji Babangidan ya zo maka da wannan zancen kuma ka tsaya sauraronsa? Ya manta mahaifin ƙawarta ne shi ko kuwa ya manta akwai aminta tsakanin matarsa da ni? To ban da ma mutuwar zuciya ina shi ina zuwa neman auren Sa'ida fisabilillahi, kuma kai bai ji kunyarka ba ma".

Tayi maganar cikin Firgicin da ya bayyana a muryarta zuwa ƙwayar idonta da ta fito waje. Wannan yanayin nata da kuma maganar da tayi sai ya bawa Abbaa dariya. Aifa ran Ummani ɓace ta miƙe tana faɗin,"Dariya na baka kenan, to ba zai yiwu ba wallahi, yanda ya zo ya tafi ya tafi kenan babu wani aure tsakaninsa da Sa'ida, hauka ake yi?".

Abbaa yace,"To idan Allah ya ƙadarta faruwan hakan fa? Kuma ina ga ai ba haramun ba ne don ya aureta".

"Allah ma ba zai ƙadarta hakan ba ubangiji ai ya san daidai, kuma nima ai ban ce haramun ba ne sai dai ai akwai duba a lamarin, kuma ya ce ko ka faɗa masa babu wurin shigarsa?".

Abbaa na yin wata dariyar ganin duk tayi kicin kicin yace,"A'a na dai ce masa ya dawo gobe ya ganta, tunda yace yana so a ba shi dama ya shiga jerin zaurawanta ya fara kafa gwamnatinsa da wuri".

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull