Ƙayar ruwa book 2 and 3 complete - Chapter 38
Ƙayar ruwa book 2 and 3 complete Chapter 38: Ƙayar ruwa book 2 and 3 complete Chapter 38. Ina zaune nan wajensu anata hira, Umman Batula tace ba don aure…
4,473 words
Ina zaune nan wajensu anata hira, Umman Batula tace ba don aure me kai mutum inda bai tsammani ba ita ina ta taɓa tunanin zata zo wannan garin me uban nisa, sai ga shi ta kawo ƴa har ta kwana ma. Ana ta shaftan hira ni dai duk a ƙage na ke na tashi na tafi wurin mijina, hankalina na kansa ban son barinsa ahi kaɗai. Can sai ga Kudrat ta dawo da ƙaton tray na abinci ta aje, suka shiga yi mata sannu da aiki da ɗawainiya da su.
Hajjo na cewa,"Ya kamata ki huta haka tun safe kike kai komo da mu, kinga mu abincin safe da muka ci har yanzu a ƙoshe muke wallahi, ya kamata ki huta haka kuma, an gode Allah ya shi albarka, munji daɗin yanda kika karrama mu wallahi kin mana kamar na ki".
Tana murmushi tace,"To ai dukka ɗaya ne Mama, ku ɗin nawa ne nima ku ɗauke ni taku tunda har zama ya haɗani da ƴarku". Dariya ta suɓuce min saboda hausartata, ban da ɗazu da aka haɗamu ana mana nasihar nan ni ban taɓa jin tayi hausa ba, to ɗazun don ina cikin zafin kishi ne shiyasa ban ji gwarancin da kyau ba, ashe haka ta iya kwaɓa hausa, kuma ba wai kwaɓar ba ne, hausar akwaita a bakinta yanayin fitar maganar ne abin dariya. Ita ta dube ni tace,"Me kina wa dariya?". Ta faɗa da turanci sai na ce,"Ai da hausa za ki faɗa Madam". Ta kawo min duka tana cewa,"Ƴar wulaƙanci, zan zo in fiki iya hausan ne ai".
Gwaggo tace,"Rabu da wannan ƙanwar taki, mu dai don Allah ki huta haka kin ji ƴata, hidiman yay yawa".
Tace,"Mama waye zai gajiya da yiwa manyansa hidima, idan kana son ganin daidai ai sai ka kyautatawa iyaye, na ɗauke ku iyayena ina kwaɗayin adu'anku da albarkanku, ba zan gajiya da biya muku buƙatunku ba har ku tafi, ko wannan yarinyar ba zan bari ta ƙwacen lada na one second ba, komai ni zan ke yi muku".
Naji daɗi sosai da yanda ta mutunta min ƴan uwa. Sai da zata fita ne take ce min,"Sisi na haɗe mana namu gaba ɗaya a dining ko ɗaki za ki tafi muku da shi?".
Na ce,"ki yi mana yanda kika ga ya dace". "Ah ah ni dai ki faɗa don Allah". A hankali cikin wani yanayi nace,"To ki haɗa mana, gani nan fitowa".
Tana fita baki ya ɗauka da nayi dacen kishiya. Na so naci abincin a wurinsu sai ga Foridat ta shigo tace,"Momi Maama tace ki fito mu ci abinci".
Na tashi muka fita tare da ita ina riƙe da hannunta, ina tambayanta ba su je school ba tace min ai suna holiday. Dukkanmu kuwa muka zauna a dining har da Safiyya da yaran, Kudrat na mitan ni da Salim sai mun haɗa har na safe da bamu ci ba, ba zamu bar mata abinci ba, ita tayi girki ba Kuku ba, idan ba haka ba kuwa ɗumamensa zata mana da daddare. Ina dariya na ce,"Ni dai miƙo min plate ɗina, ke dai tunda kin dafa Allah yay miki albarka".
A wanda ta zuba min Safiyya ta jaye gabanta, sai wani ta zubo ta miƙo min, haka muka ci abincinmu cikin raha, muna ta hirarrakinmu shi yana faman danna wayarsa, Kudrat na tsokanar Safiyya akan ta zauna mana sai wani lokaci ta tafi Safiyya ta hau bala'in mun rainata, saboda mun mayar da ita bata da miji shine amu mata wannan zancen, haka tayi ta bambami ni da Kudrat dai na ta mata dariya. Na ke cewa Kudrat,"Kema ashe wannan ƴar bata barki ba". Tace,"Idan Sofiyya na masifa to ina yi mata shiru ne, idan ta ise ni sai in kunna wayana in ware kiɗa n abarta da halinta".
Cikin nishaɗin da kowannemu yake Sofiyya tace da Salim,"Brother ni ba zan ƙara yini a gidanka ba ka sallameni kafin matanka su saka min ciwon kai".
Yana murmushi ya tashi ya barmu anan. Komawata ɗaki ne yake faɗa min su Umman Batula a jirgi za su tafi, na ce masa kuɗi ai zai yi yawa, sai yace Sir ne yace ba zai yiwu su zo a mota su koma a mota ba, zaman motar babu daɗi, tunda akwai hali zasu tafi a jirgin kawai, nayi ta masa godiya kuwa da nuna masa jin daɗina. Gabanin la'asar muka raka su airpot suka tafi, kamar kar a rabu ni dai har da ƙwallata, Safiyya nata min tsiyarta, shi ɗin ma bata barshi ba sai da ya ranƙwasheta a ka, haƙiƙa nayi kewan su tun ba'ai nisa ba, Gwaggo ce take haihuwa me rana yau ga shi silar arziƙin ƴa za su hau jirgi.
Bayan mun dawo daga rakiyar tasu ne a mota yake min zancen dinner ɗin da abokan aikinsa suka shirya mana, yace anan cikin barrack ɗin namu za'ai ba a wani waje da nisa ba. Ko da muka koma gidan aje ni yay yace zai je wani waje. Ni da Kudrat muka zauna ita tayi ta min hira tun ban saki jiki ba har na ware, yaran na gefenmu suna na su wasan, da kanta ta kira min Mamanta ta haɗamu a wayan muka gaisa, itama Mamanta mace me halin mutunci, tana ta ce min daughter ne, muka sa wayan a handsfree ita kuwa dai faɗa ta dinƙa mana har da cewanta idan bamu haɗe kanmu ba sai ta zo har gida tayi mana duka, cikinmu duk babu wanda yafi ƙarfin duka a wurinta.
Sai bayan isha'i ne Salim ya kira Kudrat, yake ce mata mu shirya da ya zo tafiya zamu yi can wajen dinner ɗin, shirinsa ba mai wuya ba ne. Kudrat ce tayi min kwalliya ashe makeup artist ce, nayi shigan white material na gown, nayi kyau sosai a ciki, su kansu yaran cewa suke Momi kin yi kyau. Ita kuwa haka ta dage tana tayi min hoto a iphone15 ɗinta. Sai da muka gama shirinmu muna ta zaman jiransa a falo tukunna ya dawo, ba ƙaramin daɗi yaji ba da yanda ya same mu, don sai da ya kasa ɓoye farin cikinsa, har da ce mana,"Yawwa kunga yanda na sameku ɗin nan tare kuna hira kuna dariya, haka na ke so na sameku ko da yaushe har sanda zan daina numfashi a doron ƙasa".
Ni ce me saurin cewa,"Please ka bar mana zancen mutuwa". Ya murmusa kunci yace,"Mutuwa dole ne". Kudrat tace,"Mun sani ai, yanzu dai jeka shirya".
Shima shigar white suite yayi yay kyau sosai, sai dai muna zuwa can wajen taron suka sa shi sai dai ya cire ya saka uniform ɗin su. Ni dai ƴar kallo na zama a wajen don duk wadanda suka zo mana murna magana suke da yare. Ba wani taron mutane aka yi ba na azo aji a gani, iya ƴan barrack ɗin ne suma kuma manyan cikinsu duk da iyalinsu, ai kuwa naga yanda ake shan barasa kamar lemu haka aka dinga fasa kwalabenta. Na kasa daurewa sai da na taɓo Kudrat na yi mata gulman. tana dariya sosai tace ai kusan duk cikin barrack ɗin mu ne kawai Allah ya zaɓa da gidan wani soja Moses nan ne kawai ba'a shan barasa. Amma ko gidan mutum kaje aka tashi kawo ma ruwa sai an haɗo maka da ita.
Kiɗin da aka saki shi yaja mana lokaci, ban san Salim haka yake ba ai, ya shiga sai rawa suke tiƙa ba ya ko jin kunyar yaransa. bamu baro wajen dinner ɗin ba sai after eleven, kyautukan da suka ba ni har da na kuɗi, har da ƙaton frame da aka mana na hoton mu gaba ɗayan family ɗin, nawa ne aka yi merging akai nasu kuma already dama akwai shi, lokacin Rofi'at na jaririya. Kafin mu ƙaraso gida yaran duk sun yi bacci a mota, Foridat ce kawai idonta biyu itama don suna buga ludo game ne da Kudrat, Allah sarki babu ruwanta tana kujeran baya ina gaba, ko irin nunawan nan fa sam, dalilin hakan har sai da na tuna ranar da zamu fita da Zahra'u nayi ƙorafin ta shiga gaba Nazifi ya nemi yaci mutuncina, gaskiya samun irin mata kamar Kudrat a wannan zamanin sai an tona.
Haka muka dawo a gajiye, duk kuwa gajiyan da muka yi hakan bai hana Salim ƙara ɗora min wata gajiyan ba, don haka yace shi kam bai iya missing zaƙin madaran da ya sha jiyan, hakan kuwa na biye masa muka sha bidirinmu. To Alhamdulillahi a sati uku da nayi cikin sabuwar rayuwar auren da na samu babu abinda zan ce da mahallicina sai godiya, ko a iya haka aka barni. Haka kuma ina yiwa duk wani wanda ya fuskanci ƙalubale irin nawa fatan samun kyakykyawan farin cikin da ta fi tawa, ina ganin soyayya da kulawar da ban sami irinta a baya ba, ban wani san tarairaya daga wurin miji ba irin yanda na ke samu a yanzu, ban san tattalin mace kamar ƙwai ba a wajen namiji, na dai san bautar miji da bautar ƴan uwansa. Kuma a rayuwan baya na san na shaƙu da Nazifi fiye da dukkan tunanin me tunani, haka na so shi wani irin so da na ke jin ba zan iya rayuwa a duniyar da babu shi a tare da ni ba, sai dai mamakin kaina na ke yi a yanzu, to shin anya son da na yiwa Nazifi so ne da ake kira asalin so muraran? Saboda ji na ke yi kamar akan Salim na fara son wani ɗa namiji, son da har na ke jijjiga idan na sami gimlawar tabbatacciyar da zata iya raba tsakaninmu, a yanda na ke ji yanzu ji na ke kamar zuciyata dama can an halicceta ne da jinin soyayyar Salim. [2/2, 07:48] Hlm: *B3ƘR16FT5* Tsakanina da Salim zaman rayuwa mu ke yi me cike da jin daɗi, tsumammiyar soyayya, kwanciyar hankali, farin ciki da fahimtar juna. shi kam irin mazan da kowacce mace ke kwaɗayin samu ne, wai ance soja bai sakewa iyalinsa to shi dai ba haka yake ba, a waje yake soja amma a cikin gida abokin iyalinsa ne.
Namiji ne me kyautatawa iyalinsa, me bawa iyali lokacinsa, me wasa da dariya da su, idan har yana gida to yana cikin matansa da yaransa ayi ta raha, yay ta mana barkwancin da cikinmu sai ya ƙulle don dariya, kuma ko da yaushe cikin tambaya ya ke ba ku da wata matsala? Me kuke so? Zan yi kaza ya kamata nayi mene shawaranku akai?. Duk abinda yaci a waje kuwa in Allah ya yarda muma sai munci sai in ba a garin yake ba amma sai ya rago ya taho mana da shi, babu nuna wani banbanci tsakanin mu, nuna mana yake dukka matsayinmu guda a wajensa babu wadda tafi wata, kyauta idan zai mana iri guda haka zai siyo mana, kuma shi ba irin mazan da sai sallah sallah suke wa mace suttura ba ne, in dai yay tafiya musamman in lagos yaje to zai kwaso mana ƙanan kaya kuma haka zai kwaso su kamar kayan tagwaye kala ɗaya sak, to suna ma ya koma ce mana Hassana da Hussaina.
Ni dai yaransa kuwa ba ƙaramin daɗi naji musu ba, samun uba irinsa rahma ne wallahi, bai da kyaran yaransa ko hantaransu, ko kaji yaro yaji muryan ubansa ko gyaran murya ya natsu har yana neman maɓoya, inaa ai shi da sun ji yo shi za su falla a guje tafiya taro shi, haka zai shigo da su a ɗaɗɗafe a jikinsa. zai zauna cikinsu yay ta wasa da su, shi ne yi musu makawuya, doki, ƴar guje guje, ball a compound haka zai tayi da su a cikin gidan, idan kuma karatu ne ya kama nan ma zai zauna ya koyar da su, ga ibada ko tafiya zai yi ya dinƙa roƙonmu akan mu sa ido akan ibadarsu, yaran har sun saba ma ana kira sallah kowacce zata wuce tayi alwala hatta da Rofi'at me shekaru huɗu, in bacci kuwa za su yi wallahi kaf ɗinsu da karatun ƙur'ani a baki haka bacci zai ɗauke su, na lura kuma koyarwar hakan ba daga gare shi ba ne kawai har da mahaifiyarsu don itama ba baya ba.
Na ƙara fahimtarsa sosai, shi me son a kiyaye ka'idojinsa ne, shiyasa ko da yaushe na ke iyakar ƙoƙarina wajen yin abinda yake so, na kuma guji duk abinda na san ba ya so, kullum godiya na ke ga Allah da ya sauya min abokin rayuwa, wanda sai a tarayyata da shi ne na san haƙiƙanin jin daɗin da ake kira a zaman aure, za ki yi bautar aure zaku ma ki huta a gidanki, ba irin gidan da na baro ba da ba ki da lokacin kanki. Salim har girki yake tayamu, ko gyara kike haka zai miƙe yace me zan tayaki da shi, idan kika hanasa sai dai ki jisa a toilet yana wankewa, babu girman kai sam a al'amarinsa, wani jin kai na shi me gida ne sam sam bai da shi. Kuma bai hana mu business don yana da kuɗi ba, ko kuma saboda matsayinsa, sam ina business ɗina na kunun aya da na ke yi tun a gida, cikin barrack ɗinmu siyansa suke kamar ruwa, har wani restaurant na ke yiwa suna zuwa su karɓa, to fa duk sanda zan yi indai yana gari muna zubawa a jarka shi kuma yana saka mana murfi da inji. Itama Kudrat ɗin tana yiwa wani restaurant baked meat pie, nan ma shi ke sakawa a oven ya barmu da zuba nama da dannewa, in ya so ma kwaɓin sometyms shi yake yi, kuma sam bai san ya sawa kuɗinmu ido ba, ya san muna samu amma in har mun tambaya kai tsaye zai ɗauka ya bamu, babu zancen tuhumar ina kuɗin da kike samu ko complain ɗin kin fiya a baki a baki, yace kuɗin mu namu ne mu yiwa kanmu hidima, sai in mun yi niyyan taimaka masa ne, shiyasa ga shi nan Allah na ta ƙara buɗa masa.
Lokaci lokaci haka zai kwashemu mu tafi yawon shaƙatawa, yanda yara za su hau lilo haka muma zamu hau kai, ni dai wannan rayuwar na min daɗi, to ta ina ma zaka yi baƙin ciki balle ɓacin rai? Ina kake da lokacin tuna baya? Rayuwar gidan Salim rayuwa ce ta jin daɗi da farin ciki, abinci wataran ma ce yake mu huta da girki sai ya ɗebe mu a tafi restauran aci, idan za'a dawo ayo takeaway ɗin wanda za'a ci da daddare, haka ya ɗebemu muje shopping kowa ya jido abinda yake so, wataran ya saki kuɗi kamar bai san ciwonsu ba, wani sa'in kuma sai yace ai siyayya saffa saffa bai da kuɗi sosai, wani sa'in ma sai ana zaune sai yace da da kuɗi da anje shopping, amma tunda babu ya zamu yi sai muyi haƙuri, kuma ba wai babun ba ne, a'a kawai yana koya mana rayuwa ne ta yanda in mun samu lafiya idan babu ma lafiya, musamman ma yaransa.
Tuni na koma bakin aikina, ashe already ya sama min aikin tun kafin auren anan wani asibiti Westend Hospital, sai da na cika sati biyu ya ke cewa na shirya muje ayi min interview, asibitin babba ne kuma private, cikin sati sau huɗu kawai zan dinƙa zuwa, monday and wednesday aikin safe, sai friday and saturday aikin yamma, kuma albashina ma har yafi wancan ɗari biyu zan ke ɗauka. Ina ta zuwa wajen aikina, idan morning duty ne da ni tare muke tafiya da Kudrat da ike ita tana da mota, yace nima kafin ya siya min tawa, idan na yi evening kuma zan hau cab a tagiya, Kudrat ɗin ita zata je ta ɗakko ni babu yanda ban yi da ita ba akan ta barni na ke dawowa da kaina taƙi, Salim yace shi bai yarda ya bar matansa da driver ba, gwara ya siya miki mota ki yi ta sakarftunki, Yaran dama kuwa school bus ke kai su ya dawo da su, bokonsu me haɗe da islamiya ce tun bakwai idan suka tafi sai shida da rabi suke dawowa.
Duk ranar da na ke evening da ke ina kaiwa tara na dare, kafin nayi closing sai dai naga yara sun zo sun kewaye ni suna Mommy mun zo ɗaukan ki, asibitin har an sanmu an san yaran, da yawansu ma ce suke ni da Kudrat sisters ne, kuma a haka na barsu ba wanda na nunawa abokiyar zamana ce, to in ma na faɗa sai a iya ƙaryata ni dan ba'a san kishiya da kishiya da irin rayuwan da muke yi ba, kanmu haɗe yake, abinda mijin mu ya ɗora mu akai shine mu riƙi juna, shi ma kuma bai fifita wata cikinmu, to ta ina wata zata tsiri buga iskanci?
Ni da kishiyata zama muke na mutunta juna da girmamawa, don tuni na tsayar da hankalina waje ɗaya na kama hanyar da ta dace, ki sakawa kanki banzan kishi ne fa ki sakawa kanki damuwa da zubar da aji, gwarama idan ace kisjiyar ce bata da kirki sai kema ki nuna mata kin fita. yanda muke zaune kamar ba kishiyoyi ba, akwai baƙuwar da aka yi sai zuwanta na uku ne ma take cewa wai dama kishiyoyi ne mu, ita wallahi idan ta zo yanda take samunmu ta zaci ya da ƙanwa ne. Kudrat macece wadda ta iya mu'amalantar wanda ke tare da ita, zama na gaskiya da amana babu munafurci ko ƙullaci, macece me sauƙin hali da bata da damuwar komai, zuciyarta a buɗe take, bata da ruƙo sam sam idan abu ya haɗaku kai tsaye zata fito ta faɗa maka ko da zaka ji haushinta, haka ko laifi ka mata wallahi a ƙarshe ita zata baka haƙuri tace maka mece rayuwar? Nawa take? Wataran duk wayan gari zamu yi babu mu? So muke muje mu gamu da Allah lafiya, to don me zamu aikata abinda ba ya so? Gaba bata da wani amfani, idan an sami saɓani a fahimci juna kawai a wuce wajen a ci gaba da rayuwa. Kuma ƙarya ne kayi rayuwa da ita ba ka ɗauki ilimi ba, ina nufin ilimin iya zaman rayuwa da koma waye, nurƙufanci, ɓacin rai, jin kai Kudrat duk bata da wannan.
Yaranta ta sakar min su kamar nawa, ko daga baya sai da ta tambaye ni wanne suna na fi so suke kirana da shi na ce mata Mommy ɗin ma yayi ina so, ga yaranta a nutse ba rashin ji, wai irin ma idan ɗa yay ba daidai ba kishiya ta tsawatar masa kiga uwarsa na cin magani ko a hau rigima, inaa ai ita kawai kece uwarsa idan ma zama za ki akan yaro indai laifi yayi ba zata ji haushi ba. Abinci kuwa bata yarda wai muci abinci daban daban ba, a plate ɗaya zata zuba mana musa hannu muci mu ƙoshi, a wurin ta ma na koyi hakan, don farko idan nayi girkina kawai ina zubawa ne na ci, to ita kuma da ta sauke ko da safe ne zata zo tace min na taho muci abinci, tun banci yau da gobe dai da bata gajiyawa da min bismillah ba har na zo ma nima bana iya girki ba da ita ba, idan bata gida na dafa zan aje mata tunda ita aikinta kullum ne, week end ne kawai bata fita. idan damuwarta ta ɗakko ni zata zo ta zayyanawa tana cewa Momin Rofi'a bani shawara, ko Momin Rofi'a abu kaza nace yayi in yi?. Saboda yanda Rofi'a ɗin ke maƙale min kawai ta koma ce min Momin Rofi'a amma da Sisi Nah take cewa, Rofi'a ɗin ma yanzu a wurina take don tuni ta tattaro min kayanta tace mu ƙarata can. Idan baƙon sani ne ma kai zaka ce ko ni ce uwar yarinyar.
Haɗin kan kuwa da muka samu ba ƙaramin daɗi yaywa Mijinmu ba, dalilin hakan har kyauta yake yi mana, yace kyautan kun haɗe min kanku ne kuna zaune lafiya, yay tayi mana godiya. To mu kanmu mun fi jin daɗin yacca muke zaunen, ba fa mu san mu ƙule a ɗaki ba, a'a uzuri ne kawai ke kai ki ɗaki sai in bacci, amma falo muke yada zango, in kallo ne ayi in hira ce ayi, ayi wasa ayi dariya ba cin muutuncin juna ko ɓatawa juna. To ni da banda ƴan uwa ma a garin, ita da take da su sun koma kamar ƴan uwana idan suka zo gidan, sai su zo kai tsaye su taho wurina su ce wurinki muka zo Momin Rofi'a.
Gaskiya da farko na so na bawa zaman namu matsala, ina iyakar yina wajen ganin na danne kishina amma sai na kasa, har ta kai ga wata rana lokacin watana guda, Salim yay tafiya ya dawo ni kuma naje kai Isioma asibiti taji ciwo a makaranta garin lilo, to dawowan da zai yi a wurina zai sauka, ai kuwa ina zuwa na tarar da shi can ɓangarenta ya baje yana cin abinci suna hirarsu, wannan abin ya ƙona min rai, zuciyata ta sosu, don me a ranata? Duk da dawowan bagatatan yay ai sai ya jira na dawo tukunna na samar masa da abincin da zai ci, mayunwaci ne shi da ba zai iya riƙe yunwar har na dawo ba, ko kuma idan ya zauna a ɓangaren nawa kashe shi za'ai? Haka na cilla musu ledan maganin Kudrat na min magana naja tsaki na fita.
Ai kuwa ranar na dinƙa masa banbami na tayar masa da hankali akan kar ya ƙara cin abincin kishiya a ranar shigata, ko kuma ya tafi zuwa wajenta, fuskarsa ta nuna ɓacin rai sai dai sam bai biye min ba, hasalima haƙuri ya shiga bani yana lallashina, amma na fututtuke masa na ɗaura gaba da shi, har ina cewa ni sai ya raba mana gida, haka muka zauna da shi har ya koma ba na masa magana, girki ma sai in yi inci kayana ni ɗaya. Kuma tun wannan lokacin na ɗaukewa Kudrat kai itama na daina sauraronta har yaje ya kuma dawowa, acewata ai ita ta haɗa ni da mijina. Sai bayan dawowar tasa ne yaga bama mu'amala da juna, ya saka ido yaga idan tayi min magana sai dai na gaggaya mata magana ina faɗin makira munafuka macuciya, ranar kuwa ashe ya jini muka gauraya da shi a ɗaki, ranar naga ainihin Salim na san kuma wanene soja, na kuma san asalin kalmar tsayayyan namiji a gidansa, don nuna min yay akan matarsa bai ƙi ya sallame ni ba, kai ni ban ma taɓa tsammanin zan sake kwana a gidansa ba wallahi, har ya fita a ɗakin jira kawai na ke ya dawo yace na kwashe kayana na bar masa gida, ashe fitan kiranta yay itama ya haɗamu a falo yaci mutuncinmu gaba ɗaya tun balle ni, ita kuwa duk ta ruɗe hankalinta ya tashi akan yanda ya hayayyaƙo min, tayi ta basa haƙuri tana ba laifina ba ne nata ne, haka ta dinga kare ni a wajensa har sai dai da gaske faɗan ya koma kanta, kuma ta amshe sai haƙuri kawai take basa.
Yay fushi da ni fushin gaske, zan yi abinci yaƙi ci, in magana ya shareni, a zo bacci kamar ba mata da miji ba. Na shiga damuwa matuƙa, sai a lokacin na ke jin rashin kyautawar abinda nayi, to Allah na tuba mutumin da ke hidimta min, yake nuna tsananin so da kulawa, ya wanzar da ni a daddaɗar duniyar da na rasa a baya, ko bai ce kar na tada fitina a gidansa ba ai bai kamata ba ni a karan kaina. Ai kuwa naji jiki da ɗauke min kan da yay, wancan karan ai ni kaɗai na ke gabata shi bai tsaya biye min ba. Naga ba zan iya da shariyarsa ba sam, ranar yana bacci na rungumo abina ta baya ina saukar da hawayena masu zafi a gadon bayansa, muryana ya fito da sautin tausayi da nadama ina faɗin,"Mahbub kayi haƙuri don Allah ba zan ƙara ba, ka yafe min laifin da na aikata, zan zama me kiyayewa insha Allah".
Yi yayi kamar bai san ina yi ba, yay kamar bai farka a baccin ba, sai da yaji ina kuka haiƙan sannan a hankali yace min,"Ba sau ɗaya na faɗa miki ba, ba biyu ba, amma kika take maganata. Ba na so So'ida, ba na son haifar da rigima wannan shine last da zan maimaita miki".
Rungumesa na ƙarayi ina cewa,"Kayi haƙuri anyi farko an kuma yi ƙarshe".
Juyowa yay yana ce min,"Kinga ko a musulunce zargi bai da kyau, idan kika biyewa zugar shaiɗan kuma yana raya miki abubuwa kina ɗauka shikenan ya buɗa miki hanyar rashin samun natsuwa da kwanciyar hankali, ga shi ki kwasarwa kan ki zunubin zargi".
"Kayi haƙuri Mahbub ba zan ƙara ba i promise you". Na faɗa ina daɗa lafewa a jikinsa.
Washegari da kaina naje na sami Kudrat ɗin da niyyan bata haƙuri, amma matar nan ta inda na ƙara yarda da pure heart ɗin da take da shi rufe min baki tayi, alamu na bama ta so taji maganar, ta janyo ni na zauna kan kujera, ƙoƙarinta kawai sai ta kawar da batun sai take ta ɗakko min zancen bikin sister ɗinta, zamu je can zamu kwan biyu tunda Paapa(Salim) bai gari lokacin. Wallahi ba ƙaramin kunya naji ba, sai abun ya ƙara min ciwo, duk da haka sai da na bata haƙuri, amma hakan take ce min ita bata san ma anyi ba, idan ma anyi ta manta, nima in yi haƙuri don Allah. Tun daga lokacin ne kuma na sauka daga kan keken ƙayar da shaiɗan ya nemi ya ɗora ni akai, muka koma zaman mu lafiya.
Ɓangaren Family ɗin Salim tsakanina da su sai adu'ar samun aljannah, sun ɗauke ni tamkar ƙabilarsu haka kuma sun mayar da ni kamar ɗiyar su, dama Kudrat ta taɓa faɗa min haka Familyn Salim su ke wajen mayar da inlaw kamar su suka haifeta. Ku san ko da yaushe sai an kira anji ya muke, idan yau ni aka kira bayan mun gama gaisawa za'a ce na kaiwa Kudrat ɗin, haka itama idan ita aka kira za'a ce ta kawo min duk dai dan aji ya zaman namu yake. Idan ba ya gari kuwa an dinƙa mana aiken abubuwa ba wai don babu a gidan ba, tsaban kulawa ne kawai, da zarar yau ya ɗauke ƙafa Sir zai kira mu da kansa kowacce yace mata ga kuɗi nan ya tura mata. Ɓangaren ƙannensa kuwa ni ban san wani rashin kunyan ƙannen miji ko rashin ladabi ba irin na hausawa, yanda suke girmama Yayansu haka muma suke girmama mu, ba su kaɗai ba hatta Yayyunsa cikin girmama juna muke da su, Babban Yayansa Chibuzo kuwa mutumin nan ya mayar da mu tamkar iyalinsa, da yake bamu da nisa da su shima duk wani aike da zai wa iyalinsa zai sa a kawo mana, musamman Yaran duk abinda ya siyawa Ƴaƴansa to sai ya siyawa ƴaƴan Salim.