Kenza eBookz
Cover art for KIDA A RUWA BOOK 2 PAGE 24

Post

KIDA A RUWA BOOK 2 PAGE 24

.....through that. Nabeeha's biggest worry is how everything happened and why she won't keep it a secret from us. Dan Tsaff will say that he is worried that he is united one by one. He has the money and the power to remove himself, we are in the water.." "Of course your conversation is on the right path, Aunty, but we can ask him to lie and inform her, and when he comes, we will do everything we can so that she doesn't know. I am sure that Nabeeha will get everything we want in this world, we will get it from him, but I am just worried about knowing what his intentions are for her." "How do we know that Mamawo? Since it's not his heart, we will tear it apart and look at it." "Aunty, this is the secret of the heart, you are preparing to go to India to work, but what is his plan, he will let us know." Silent Hajiya Hasiba could not speak. She does not follow witches, but most of the spying is done by the first lady. and they went together... "Aunty, are you quiet?" We are not sure today.....

Standalone post1,774 words

24

..........Shiru sukai kowa ya gagara iya cewa komai. Sai zuwa can Mamawo ta ja numfashi mai ƙarfi ta furzar. Sai kuma ta ajiye spoon ɗin hannunta ta rabga tagumi da hannu biyu. “Anya Aunty mutumin nan bada wata manufa yake son Nabeeha ba?. Wlhy nikam al'amarin nan fa ya fara bani tsoro gaskiya. Duk matan ƙasar nan ko a cikin nan Dubai irin sa, da masu shigowa baƙi kullum, dana ƙasashen da yake yawo ace ya rasa matar aure sai Nabeeha da aka jima da sanar masa tana da miji. Abin mamaki duk cin kashin da take masa bai taɓa nuna koda damuwa a fuska ba balle zuciyarsa. Kai wannan batu yana buƙatar dubawa fa. Kalla gidan nan daya mallaka miki halak mallak, ga motar hawa, mu dukanmu yasa akai mana katin zama ƴan ƙasa. Yanda suke da ƴanci a ƙasar nan haka fa muma muke da ƴancin shiga duk inda muke so a lokacin da muke so..”

“Ni kaina a wannan gaɓar na fara tsorata Mamawo. Balle ma maganar kashe Haysam da yayi, bawai bana son ya kashe san ba. Nasan wannan kuma abu ne mai sauƙi a wajensa aikata hakan. Babbar damuwar wataran Nabeeha tasan yanda komai ya faru wlhy bazata rufa mana asiri ba. Dan tsaff zata ce damu aka haɗa kai akayi. Shi yana da kuɗi da mulkin da zai cire kansa, muko mune a ruwa..” “Tabbas zancenki na kan hanya Aunty, sai dai ai zamu iya roƙonsa karya sanar mata, sannan zuwan da zai yi ma duk yanda zamuyi kawai muyi kada ta sani. Dan na tabbatar ya samu Nabeeha duk abinda muke so a duniyar nan zamu sameshi a wajensa, ni dai kawai babbar damuwa ta mu fara sanin wai minene ma manufarsa akan son nata”. “To ta yaya zamu sani kuwa Mamawo? Tunda ba zuciyar tasa zamu tsaga mu duba ba”. “Ai bata wannan ake gane sirrin zuciya ba Aunty, shiryawa zakiyi wuff muje India wajen mai mun aiki, koma minene shirinsa sai ya sanar mana shi”. Shiru Hajiya Hasiba ta kasa magana. Bawai bata bin bokaye bane, sai dai mafi yawa irin wannan leƙe-leƙen bata yinsu a karan kanta first lady ce ke aikenta, kuma tunda suka sauka a mulki ta ɗan rage yi sai na kan kasuwanci da takan je mata, wani lokacin kuma suje tare..... “Aunty kinyi shiru?”. “Ba shiru nayi ba Mamawo, ina auna yanda tafiyar tamu zata kasance ne, balle kinji shi yace zai tafi da wata a cikinmu. Kinga bamu da tabbacin yaushe ne ko?”. “Haba aunty mu sai kace ba mata ba. Zaki iya bagarar da shi akan tafiyar gaggawa ta taso miki wani business ɗinki haka. Kinga sai muyi mu gama da wuri mu dawo. Dan haka ya kamata ma ace cikin watan nan mu tafi”. “To bari muga zanyi tunani”. Daga haka ta miƙe tabar haɗaɗɗen dinning room ɗin da aka cika kayan abincin alatu duk saboda Adeel. Sai gashi ko cikakken lauma uku baiyi ba ya tashi ya barsu da kayansu.....

<%><<<%>>><%>

Mintuna talatin da isowar Mammah da Ammar su Aunty Ummi suka shigo gidan ita da Aunty Mommy. Cikin matuƙar farin ciki suka rungume Mammah dan yanayin ta kaɗai ya tabbatar musu da lafiya ta ƙara samuwa Alhamdullah. Suma dai hankalinsu bai kai ga Uncle Tasi'un ba sai da suka gama gaishe-gaishen su. Turus sukayi suna kallonsa. Ba kallon sani ko tuna waye shi ba. Kallon mamakin kamaninsa da Mammansu kawai. Dan suma sanda wancan abin ya faru basu da wayon tuna komai gara ma Ma'aruff da Ja'afar ɗin. To balle ma Mimi ƴar ƙarshe ita da Ammar da lokacin basu wuce shekaru shuda ba. Biebah kuwa na jaririyar wata baifi biyu ba. Maida kallonsu sukai ga Mammah, kafin ma suce wani abu ta basu amsa da, “Kawunku ne”. “Kawunmu Mammah? Na ina to? Mudai a sananinmu ƙannenki duk sun rasu, gashi kuma yana kama da ke”. Sai da ta ɗan girgiza kanta da murmurshi kawai sannan ta ce, “A'a Bashir ne dama ALLAH yay ma rasuwa, Tasi'u kam ƙaddara ce ta nisanta mu”. A take murmushin fuskokinsu ya ƙarasa ɓacewa. Dan duk da bata taɓa basu labarin abinda Uncle Tasi'un ya aikata mata ba duniya ta jima da sanar musu. Koma suce cikin danginta. A taƙaice sukace, “ALLAH sarki”. Tare da gaisheshi sama-sama suka bar wajen. Cikin sake raunanuwar zuciya Uncle Tasi'u ya bisu da kallo. Mammah da duk take jin babu daɗi da yanayin tarbar da ɗan uwan nata ke samu wajen ƴaƴanta cikin sanyin murya ta ce, “Sai kayi haƙuri da abinda zaka gani a wajensu. ALLAH ne shaida ban taɓa sanar musu koda kuskuren dangin mahaifinsu ba balle naka a gareni, sai dai yau da gobe ta wuce wasa duniya da dangin sun gama sanar musu batare dana sani ba. Amma ka bani lokaci ƙanƙani, in sha ALLAHU zan zauna da su ni da Yaya Nasiru zasu fahimta”. Murmurshin ƙarfin hali yayi cikin girgiza kai. “Ba komai Adda, kuma ki sani ni banga laifinsu ba sam. Kawai ina jin tsoron isowar yaran nan da kullum zancen su danginsu danginsu kuma su fuskanci abinda bashi nake fata ba daga dangin. Nine nai laifi basu ba, dan haka dan ALLAH ko sunzo suyi haƙuru su su amshesu koda ni bazasu ashe ni ba”. “Kaima zasu amshe kan in sha ALLAHU. Kadai bani lokacin. Bismilah muci abinci sai ka samu kaje ka watsa ruwa lokacin Azhar na gabatowa. Yanzu kuma gidan zai sake rikicewa dan masu shi na gab da dawowa daga makaranta”. Murmurshi kawai yayi. Ya gyara zama ya fara cin abincin da aka shirya musu a tsakkiyar falon....

★★★

“Tab ɗi, wai yaya mi hakan ke nufi? Miya kawo wannan mutumin rayuwarmu a wannan gaɓar? A ina ma su Mammah suka samo shi wai shin?”. Ya ƙare maganar tana kallon Ammar. Ammar cikin sake ɓata fuska ya ce, “Aunty acan muka haɗu da shi cikin asibiti fa. Ni kaina nayi mamaki da Mammah ta bashi damar wai ya biyomu, nazata kawai zata barshi ya koma inda ya fito ne”. Hawaye Aunty Momy ta share, muryarta na rawa ta ce, “Sun manta damu a lokacin da muke buƙatar tainakonsu da ƙarfinsu. A yanzu zasu fara dawowa rayuwarmu kenan a lokacin da ƙarfinsu ya ƙare mu mukai ƙarfin. Ni tsorona ma kada ya sake zuwa yaye dukiyar tamu ne ya gudu”. “Shi ɗin banza”. Cewar Ja'afar a hasale. Ya cigaba da faɗin, “Ai ko a wancan karon dan Dada baya nan ne ya samu nasara, kuma yana da hakki a wancan amma a wannan fa. Ko a yanzu da babu Dada akwai halifofinsa a kusa. Idan da rabon yazo yayi ta ransa ne bismilah”. Cikin furzar da iska Ma'aruff ya ce, “Wlhy ni nama rasa tacewa sam. Amma al'amarin ɗan adam bai taɓa bani ƙarshen mamaki ba irin yau. Wai dama Uncle Tasi'u har yana da ƙarfin zuciyar iya sake tunkarar Mammah?”. “Ai baida kunya Yaya Ma'aruff gashi kuwa yayi ka gani. Wlhy ina matuƙar jin kewar Dada. Ya ALLAH ka saka mana ka tarwatsa farin cikin duk wani azzalumi dake da hannu a kama mana shi. Wlhy wani cin kashin ma da yana nan da bazasu kwatanta mana shi ba. Dan na tabbatar duk tsawon shekarun can saboda shakkarsa yasa ko ƴan Bauchi kasa sake tunkarar inda muke. An kama shi dan kar su zo mu nema taimakon sun suka sake ja baya damu. Yanzu kuwa tunda sunga ALLAH ya rufa mana asiri zasu fara kawo kansu...” “Ai ko zasu fuskanci wulaƙanci da tozarci a garemu. Dan mu mun jima da sallama dangi a duniyar mu. Mune dangin kammu mahaifiyarmu da Dada sun ishemu uwa uba a duniya. Azzalumai kawai masu matacciyar zuciyar watsar da marayu”. Ammar ne ke maganar yana kuka. Rungumeshi Ja'afar yayi yana shafa bayansa. Haka ma Aunty Momy hawaye take ta sharcewa ita da aunty Ummi. Kasancewar a sashen Yaya Ja'afar suke zaune sai suka ƙi komawa sashen Mammah har sai da yara suka dawo school. Basa son su fahimci komai dan haka suka dawo sashen Mammah ɗin. Inda suka sameta zagaye da yaran cike da farin ciki kowa ji yake kamar ya koma cikinta. Ita ko bakinta ya kasa rufuwa. Abinci ma ita ta dinga basu abaki tun daga kan Nimrah, Ruƙayya, Abees, Aheel, Afrah da Ayyan ƙarami. A haka shima Mu'azz da Imam suka shigo gidan suka samesu. Suma daɗi ya kamasu da ganin Mammah ta dawo. Ai tuni suma sunyi zaman dirshan suna amsar abincin. Wannan farin cikin ya saka su Aunty Ummi mantawa da damuwarsu. Dan Mammah na kammala bama yaran abinci suka dawo wajen Uncle Ammar shima kowa na tambayar tsarabarsa. Musamman Nimrah da Ruky da suka bada sakwanni na musamman......

<•><•><•><•><•> Kusan lokaci ɗaya Uncle Nasiru da Daddy Imran suka shigo gidan. Dan dukansu daga wajen aiki suke. Sabon Driver dake zaune tare da maigadi ya bisu da kallo su duka. Dan yau kwanakinsa shida a gidan bai taɓa ganin Uncle Nasirun na, sai Imran sau 1 shima. To Daddy Imran ɗin kuma yayi ƴar tafiya bayan wucewar Mammah da yazo sau ɗayan daya gansa, kwanansa huɗu ya dawo. A randa ya dawo yazo gidan lokacin shi kuma yaje ɗakko yara daga Islamiyya. Motarsa na fita shi kuma ya dawo da su. Tun ranar kuma bai sake zuwan ba sai yau. Uncle Nasiru kuwa dama tunda Mammah tai tafiya bai leƙo gidan ba saboda ayyuka sun masa yawa, ya kuma san yaran duk ba zama suke ba sai matan su Ja'afar kawai. Suna tsaka da gaisawa Maigadi ya gama rufe gate ya nufesu, dole shima driver ya bishi suka iso inda suke. Rissinawa sukai suna gaishesu duk da kusan sa'an Imran yake shi sabon driver, koma ya iya girmarsa kaɗan duk da shi Imran akwai jin daɗin rayuwa da kulawa da lafiyar jiki irin ta soja a tattare da shi. Uncle Nasiru yana tsokanar su. Shi ko Imran sai ya ɗan zuba ma sabon driver idanu. Har sai da Uncle Nasiru ya ce, “Imrana yaya dai? Ko ka san shi ne?”. Cikin ɗan murmushi Imran ya girgiza kai da faɗin, “A'a Uncle. Kawai na tafi wani tunanin ne daban”. Bai jira amsawar Uncle Nasiru ba ya juya ga drivern ya amsa masa gaisuwarsa. Daga haka suka bar wajen driver na binsu da ido. A zuciyarsa kam dake bugawa ayyanawa yake (lallai akwai matsala. Shegen nan ko bai gane ni ba ya tsargu da ni. Lallai dole na canja takuna kenan. Dan banzo nan dan na tafi batare da na kammala abinda ya kawoni ba) a zahiri kam miƙewa yay ya koma gate ya zauna a kujera. Sai kuma ya zaro wayarsa ƙaramar nokia ya shiga danne-danne kafin ya kai kunnensa.....KIƊA A RUWA 2