Kenza eBookz
Cover art for KIDA A RUWA BOOK 2 PAGE 50

Post

KIDA A RUWA BOOK 2 PAGE 50

..... they got the seat of the federal parliament member, one tenure showed them again their desire to be the president of the country, they again insisted that he get a big plan that they will use to bring back the things they stopped doing in the past. And then the hair will be turned upside down by the owl. In the week that President Yusuf Shu'aibu Tafida is trying to complete one hundred days after gaining power, he released their biggest threat from prison. The general did not seek peace. I am not happy with the whole meeting today. So the son did not do much good and they dispersed to everyone and he will think of a way out from here for a week. They had to find out where Zak-Shadow was and they got confirmation that he was taken to the hospital and not to his home. They only have to search the hospital and kill him from there, but his body is revealed to the world. The president was so shocked that he would rather kill him too. You and even Zak-Shadow's family will not survive this time. They have to prepare a real game with the name of game in this part...... >>>>>>>>>>%<<<<<<<<< ★3-DAY LATER★ It is three days before the presidential pardon for Dada.....

Standalone post1,795 words

50

........A lokacin da zuriar alkairi ke farin ciki anan a ƙungiyar duhu dama wasu munafukan bayan fage cikin soji irinsu Garba a hargitse suke da tashin hankali. Dan shugaban ƙasa kam ya musu mamaya irin wadda ko'a mafarki basu taɓa kawoma zuciyarsu za'ayi ba. Tuni oga Jush yay kiranyen meeting na gaggawa, duk da shi bama ya ƙasar ya koma inda ya fito tunda dama lokaci-lokaci yake shigowa. Amma sai ya kira ta video call da akai connecting da ƙaton tvn meeting room ɗin nasu. Yau kam a zafafe yake, dan kai tsaye ya ƙalubalanci Mr Scythe dake matsayin ogan Janar, dan shine ya kawo sunansa matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa. Ya kuma nuna musu jawo Janar ɗin a jiki zai taimaka musu wajen sanin sirrin gidan soja fiye da sanin da suke da shi a yanzu. Sannan zasu sake karya zuciyar Zak-Shadow dan Janar ogansa ne. Su kuma ganin yanda Janar ke faman kwantar da kai da biyayya ga Scythe dama duk wani ɗan siyasa sai suka yarda da shi, batare da barinsa yasha wata wahala ba suka shiga suka fita ya samu kujerar ɗan majalisar tarayya, tenure ɗaya ya sake nuna musu sha'awar zama shugaban ƙasa, nan ma suka sake dagewa ya samu da babban shirin zasuyi amfani da shi wajen dawo da abubuwan da suka daina yi a baya dan ace da gaske da hannun Zak-Shadow a ciki tunda Janar ogansa ne. Sai kuma gashi tun kan aje ko ina reshe zai juye da mujiya. A satin da shugaban ƙasa Yusuf Shu'aibu Tafida ke ƙoƙarin cika kwanaki ɗari da samun mulki ya fitar da babban barazanarsu daga kurkuku. Lallai Janar bai nema zaman lafiya ba. Yau gaba ɗaya meeting ɗin bana daɗin rai bane ba. Dan haka baiyi wani armashi sosai ba suka watse akan kowa zaije yayi tunanin mafita daga nan zuwa sati ɗaya. Dan dole su bincika inda Zak-Shadow yake dan sun sami tabbacin asibiti aka wuce da shi ba gida ba. Dole ne su bincika asibitin kawai su kashe shi tun daga can sai dai gawarsa ta bayyana ma duniya. Shugaban ƙasa kuwa sai sun shayar da shi mamaki na gaske da sai ya gwammace shima kashe shi sukai. Kai hatta da ahalin Zak-Shadow a wannan karon bazasu tsira ba. Dole ne su shirya wasa na gaske mai sunan wasa a wannan gaɓar......

>>>>>>>>>>%<<<<<<<<< ★3-DAY LATER★

Kwanaki uku kenan al'amarin fitar afuwar shugaban ƙasa ga Dada na cigaba da trending a cikin ƙasar. Mutane ko gajiya ma basayi, sai ma wasu ƙungiyoyin matasa dake zanga-zangar lumana akan sufa ko sau ɗaya ne suna buƙatar ganin Zak-Shadow dan su samu kwanciyar hankalin yarda yana cikin ƙoshin lafiya kuma afuwar da akai masan ta gaske ce ba yaudarar ƴan siyasa ba. Dan ɓoyesa na saka musu jin kamar baya cikin ƙoshin lafiya ne ko wani abu ake son shiryawa da batun. A yanzu ma gwamnati batace uffan ba, sai ma batun dawowar shugaban ƙasa akeyi a yau ɗin daga taron kwanaki biyar da yaje. Dan washe gari yake cika kwanaki ɗari da samun mulki. Ga batun naɗe-naɗen mukamai da har yanzu yaƙi yi sai tsiraru da aka bamawa. Dan haka ita kanta jam'iyyar a wuya take da shugaban ƙasa, suna ganin raina musu hankali yake shirin yi da nuna mulkin mallaka irin na gidan soja daya saba a baya...

✨✨✨✨✨✨✨ .★JAMUS★.

A wannan lokacin daga ƙasar Jamus ma su Daddy Imran sun kammala shiri tsaff na isowa ƙasarsu ta haihuwa. Sai dai su akwai saɓani sai gobe idan ALLAH ya kaimu ne. Dan haka a karo na biyu Imran yay waya da Mammah. Dan randa aka sanar da takardar afuwar Dada sunyi waya suna taya juna murna, sai dai bai gaya mata yana tare da Dada ba ko'a lokacin. Ya dai tabbatar mata da yana nan dawowa gida a satin nan. Dan haka yanzu ma daya kira sunyi gaisuwa yanda suka saba irin ta mahaifiya da ɗa. Daga nan yake sanar mata a gyara ɗakin da babu kowa anan ɓangarenta. Yayi magana da wani kamfanin funichars za'azo a saka. Ɗan jimmm Mammah tayi na alamar tambaya, sai dai fahimtar kamar Imran bai son buɗe zancen yasa bata tambayi mi za'ai da ɗakin ba tace to kawai. Daga ƙarshe take sanar masa ya kira su Ma'aruff yay musu magana dan Uncle Tasi'u na son zuwa da yaransa yau da daddare amma tasan halinsu da shegen taurin kai. Bata son a samu matsala kuma, fatanta suyi haƙuri su barsa da halinsa su yafe masa komai ya wuce a cigaba da zumunci. A cewarta duka ma rayuwar nawa take. Murmurshi Imran yayi yana sake jinjina ƙyawawan hali irin na Mammah. Cikin lallashi yace mata karta damu, in sha ALLAHU zai musu magana. Daga haka sukai sallama. Duk wannan wayar da Daddy Imran keyi Dada na zaune a wajen. Sai dai hankalinsa na'a kan laptop zaka rantse baima san mi Imran ɗin keyi ba. Sai dai sarai yana fahimtar komai, dan ji yayi kamar ya kwaci wayar yayi magana da Mammah ɗin. Amma ya danne baiyi magana ba koda Imran ɗin ya kammala wayar ma. Sai ma wani zancen ya ɗakko masa akan aikin da yake yi a laptop ɗin. Kusa da shi Imran ya dawo ya zauna shima yana maida hankalinsa ga screen ɗin laptop ɗin......

<<<<<<<★>>>>>>>

Washe gari a gidan Mammah bisa umarnin Daddy Imran abubuwa biyu suka faru. Na farko isowar Companyn da zasu shirya ɗakin daya buƙata. Ba kuma wani ɗaki bane daban, ɗakin da Nimrah ta shiga ne tai kallon video kwanaki. Dama tun safe su Ammar suka fidda komai na cikinsa su Kulu suka sharo suka wanke bayin da ba'a taɓa amfani da shi ba. Lokacin da masu zuba kayan suka zo aikinsu kawai suka fara cike da ƙwarewa. Abu na biyu isowar Uncle Tasi'u gidan a karo na biyu, sai dai a wannan gaɓar harda yaransa uku. Biyu maza, ɗaya mace. Kamar kowa sai da sojojin nan suka musu bincike ciki da bai aka kuma tabbatar da sanin masu gidan suka zo kafin a barsu su shigo. A lokacin su Nimrah basa nan, suna makaranta iyayen gidan ne kawai sai su Aunty Ummi da kullum yanzu suna gidan sai dare suke komawa nasu gidajen. Shariffa ce kawai babu a falon dan yau ta tashi bata jin daɗi sosai kasancewar cikinta yafi na Lailah tsufa. Babban ɗansa yana kamanni da shi sosai da Mammah. Sai dai ko Ammar zai iya girmarsa da kusan shekara biyu. Sai mace itama budurwa, daka ganta kaga wayayya, gata fingai-fingai kamar kazar mayu. Itama dai Biebah zata iya girme mata kaɗan, dan bazai fi irin shekara ɗayan nan ba ta bata. Sai Auta namiji, shi kam zasu iya dai-dai da Mu'azz. Kai da ka gansu kasan rainon ƴan gayu ne, sai dai kuma da ganin inda suka zo ɗin yama fi gidansu komai suka kama kansu. Ga Mammah ta musu tarba ta mutuntawa da soyayya kamar zata haɗiyesu. Su Aunty Mimi ne ma dai sama-sama suka amshesu dan ma gargaɗin Yaya Imran ne. A haka su Nimrah suka dawo gidan suka samu baƙi, duk da dama a kwanakin nan kullum gidan bai rabo da baƙin. A gidan nan babu wanda yakai Nimrah da Ruky wulaƙanci idan mutum bai musu ba. Sun gaida Uncle Tasi'u da girmamawa matsayinsa na uba. Amma ƴaƴansa kallo ɗaya sukai musu suka watsar da su kamar sun ga kashi. Sun kuma yi musu haka ne saboda ganin yanda suketa wani jijji da kansu su a dole ga rainon turai. Kota kansu kuwa basu sake bi ba suka shige ɗakinsu, bakuma su sake fitowa ba ko abinci sakawa sukai masu aiki suka kai musu dan yau alhamis ne babu Islamiyya. Sai da Mu'azz ne ma ya dawo gidan yazo ya jajibesu suka haura sama ganin ɗakin da aka zubama kaya. Anan suka lalace sunata santi da hotuna da wayar Mu'azz ɗin. Dan ɗakin yayi ƙyau matuƙa. Haka suka fito suna damun Mammah da tambayar wazai zauna a ɗakin. Tace bata sani ba itama Daddynsu ne kawai yace a gyara....

★RANA BATA ƘARYA......★

Tabbas wannan batu haka yake. Dan kuwa washe garin juma'a kamar jiya yau ma Daddy Imran ya kira Mammah a waya yace su shirya za'azo a ɗaukesu bayan sallar juma'a zuwa wani waje. Kan Mammah ya fara ɗaurewa, amma sai nan ma bata tambaya ba saboda halin girma da dattako irin nata tace kawai to. Su Bilal ne ma data sanar mawa suka fara shan jinin jikinsu. Jiya an gyara ɗaki, yau ance su shirya anya kuwa?.. Kasancewar baƙin ido a gidan yasa basu ja maganar da nisa ba. Bayan sunyi shirin massalaci sun fita harda ƴaƴan Uncle Tasi'u Dayyan da Afeef, suma su Mammah dake gida suka hau shiri. Sai ga su Aunty Ummi sun fara isowa da tasu tawagar suma. Dan yaran basu sami sukunin zuwa gidan ba sai yau saboda makaranta. Shiyyasa yau juma'a kowa da ɗansa yazo. Nan fa aka sake kacamewa har wani baya jin zancen wani. Banda yara za'ai fitar, dan haka su Nimrah a gida akai shirin barinsu da yara amma suka shiga magiya da roƙon Mammah dole tace su shirya. Kasancewar harda Aunty Biebah da su Aunty Lailah su Nimrah sune ƙanana. Su yaran ma murna sukai da tafiyar tasu, dan a sanin da sukai musu basa ɗaukar raini, idan aka barsu da su dole su daku. Dan kaɗan daga aikin Damisa da Zakanya yaro yaci duka kafin uwarsa ta dawo.... Ba ƙaramin ƙyau sukai ba kuwa da kwalliyar tasu. Nimrah skirt da riga ne na atamfa da tai mugun zama mata a jiki, sanin ba barinta ake fita da ƙaramin gyale ba idan ta saka irin waɗan nan kayan yasa ta ɗora after dress a sama, ba ƙaramin ƙyau tayi ba ga fuska tsaff da kwalliya mai nutsuwa. Hakama aminiyar tata tana sanye da irin kayan nata sai dai ita kam gyale ta saka. Suka kawo turarrukan SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. suka saka, gashi dama sunyi kabasa da shi a kaya.. Suna fitowa Ya Mu'azz ya fara tsokanarsu wai kamar ranar auren su. Ba raga masa suke ba, dan haka suka shiga ramawa ana dariya. Daga haka suka fito harabar gidan kowa ya shiga mota. Ninah da Ruky na tare da Mammah, Uncle Bilal ke tuƙi sai Mu'azz a gefensa. Ana buɗe gate suka fito motocin sojoji biyu dake jiransu suka take musu baya. Ɗaya a gaba ɗaya a baya. Wannan matakan tsaro na ba kowa mamaki a cikinsu, dan ko yanzu su Nimrah sai da sukai magana. Dan har a makaranta ma yanzu tare suke zuwa da sojojin da a yanzu suka zamewa kowa dogari a gidan batare da sun san dalilin yin hakan ba. Abinda kawai sojojin suka sanar musu tun a ranar farko da aka kawosu shine umarni suma kawai suke bi........✍️