
Post
Kida a ruwa Book 3 page 34
....."We grabbed these cars from the shore. And that's how they were brought to my house. They were armed with bombs inside. We only took them to where we were ordered". "Who is your Ogan?". "We just call him Oga Jo. I don't know his real name". "How long have you been working for him?". "It's been three years." "Where does he live?". "We don't know what to do with his presence. Only when he wants to put us to work, he tells us where to find him." "How many of you did the work?". "We are ten". Silent Dada did not ask him anything again. He also drew some water from the needle and handed it to them. The person next to him was also pressed against him. Just like the first one, his body is already confused. Even Dada asked him. "Where is the other one you worked with?". Baima did not let him close his mouth and started to explain. "There is work they will do for Oga. They went to meet him. But I am sure they will return home and spend the night today". "Do you want to stop coming?". "Everyone has his job." "Son of GOD, Oga, do not kill me, because I feel pain in my body as if I am being cooked". Dada did not touch him. He also gave the other one the injection. He was also starting to
34
.......Isowar sa gaban su ya saka cikin jami'an nan biyu saurin jawo kujera ya ajiyema Dada. Koda ya kai zaune wani kalar zaman ƙasaita yayi tare da harɗe hannayensa a ƙirji ya zuba musu idanu. Ɗakin yay tsitt, sai nishinsu na wahala kawai kake ji. Mintuna goma cif Dada ya cika yana nazartarsu a haka kafin ya warware hannayensa ya ciro abu a aljihunsa. Wata ƴar mitsilar kwalba ce sai syringe guda uku a ledar su. Baiyi magana ba ya shiga buɗe ɗaya a ciki tare ta ɓalle kan kwalbar dake tabbatar da ruwan allura ne a ciki ya zuƙa a syringe ɗin ya miƙama ɗaya a cikin jami'an. Amsa yay da sauri, batare da ya tambaya ba kawai ya dannama ɗaya allurar. Aiko sai da ya saki wani ihun azaba. Saboda ruwan allurar wani mugun raɗaɗi ne da shi, kuma yana fara shiga jikinka kake jin hakan. Mintina biyar basu cika ba jikinsa ya fara rawa. Ga zufa ta bala'i ta jiƙesa sharkaf. Sai ga shi ya fara rattafo zance sala-sala. Cikin razananniyar murya Dada ya jefa masa tambaya, “Kayan miye kuka wuce da shi?”. “Mun ɗakko waɗan nan motocin daga gaɓar ruwa. Kuma a haka aka shigo dasu ta kwantaina. Makamai ne a ciki da bama-bamai. Mun kaisu inda aka umarcemu ne kawai”. “Waye Ogan ku?”. “Oga Jo kawai muke kiransa. Ban san ainahin sunansa na gaskiya ba”. “Tun yaushe kuke masa aiki?”. “Shekara uku ke nan” “A ina yake zaune?”. “Bamu san taka maimai wajen zamansa ba. Kawai idan zai sakamu aiki ne yake gaya mana inda zamu sameshi.” “Ku nawa kukai aikin?”. “Mu goma ne”.
Shiru Dada bai sake tambayarsa komai ba. Sai ma wani ruwan allurar ya sake ɗiba ya miƙa musu. Na kusa da shi shima aka danna masa. Kamar dai na farko shima tuni jikinsa ya rikice. Koda Dada ya tambayesa. “Ina sauran wanda kukai aikin?”. Baima bari ya rufe baki ba ya fara bayani. “Akwai aikin da zasuyi ma Oga. Shine suka je ganawa da shi. Amma na tabbatar zasu dawo gida sun kwana a yau ɗin”. “Ku miya hanaku zuwa?”. “Kowa da aikinsa.” “Dan ALLAH Oga karku kasheni, wlhy azaba nake ji a jikina kamar ana dafa ni”. Dada bai tanka masa ba. Ya bada shima ɗayan akai masa allurar. Shima yana fara nashi vibration ɗin ya jeho masa tambaya. “Ina kuka kai kayan?”. Tsaff ya bada address ɗin wajen. “Mi za'ayi da su?”. “Bamu sani ba muma. Amma mun ji Oga Jo kamar na magana da wani a waya cewar za'a fara kai su jihohi daban-daban, amma bamu san akan aikin minene ba. Dan yanzu haka yan uwan mu akan haka sukaje ganawa da shi”. Ba ƙaramin zafi zuciyar Dada keyi ba. Komai bai sake cewa ba ya miƙe ya fice. Bayansa su Faro suka bi suma zukatansu na zafin. Tsumin sojojin na ƙoƙarin tashi. Dan wlhy badan suna da target ba yaran nan bazasu kwana da rai ba yau......
★★★
Tubda suka shigo ɗakin sirrin babu wanda yace da ɗan uwansa komai. Sai Dada dake faman kai-kawo. Kusan mintuna ashirin Dada ya kallesu. “Idan lissafina yayi dai-dai Ojo ne Jo”. “Ojo fa Sir!?”. Cewar Dabo a kiɗime. Batare da Dada ya kallesa ba ya ƙarasa gaban computers ɗin ɗakin. Sai da ya zauna kai tsaye ya cigaba da faɗin. “Bazai taɓa bari su san inda yake ba. Saboda su waɗan nan amfani kawai ake da su. Kuma suna cikin yaran da aka ɗiba a ƙauyen can aka horar. Dole yau za'a fita wani operation ɗin kafin su farga da waɗan nan basa nan. Banda harbi. Dan kaf yaran nan ina son su a raye. In sha ALLAHU zamu maida su barazana ga mutanen nan. Yusuf ka nutsu ka tantance a cikin hotunan yaran tun suna ƙananu waɗanne ne a cik?i. Ka kawo doctor ya binciki lafiyarsu dan alamu ya nuna suna shaye-shaye. Ayi treating ɗinsu da ƙyau, a kuma fara basu abinci mai ƙyau. Zan tanadi malamin da zai fara dawo da hankalinsu jikinsu, duk da bamu da tabbacin da wane addini ma suka tashi ba a yanzu.” “Yes sir. In sha ALLAHU.” Dada ya juyo yana kallon Imran. “Imran matsayinka na NSA ya kamata ka bada umarnin tantance kaf jami'an hukumomin tsaro a aikinka na farko. Akwai waɗan da dole sai an sauke su a aiki zamu samu filin namu aikin. Musamman manya-manyan saman nan. Akwai abubuwa da yawa da suka sani. Wasu dasu a ciki, wasu tsoro ke hana su iya yin komai”. “Tabbas nima nayi wannan tunanin. Karka damu aiki zai fara ba wasa”. “Good. Faro lokaci yayi da zaka sakama Garba ƴar tsama a gidan soja. Dan in har muna son kama Ojo da wuri sai munbi ta hanyar kunna ma Garba wuta ta ƙarƙashin sa. Zafin da ɗuwawunsa zai fara shine zai hanashi zama ya fara neman waje mai sanyi. Babban makaminsa kuma Ojo ne. Saboda ta sanadinsa ya shiga cikinsu.” “An gama Boss”. Harararsa Dada yay yana ɗauke kansa. Dabo ya kalla yanzu kam. “Kai tare zamuyi aiki. Akwai tsohon driver da yay aiki a gidanmu, accident daya samu ya sashi kawo Buba madadinsa. Kwana biyu banga Buba ba ba. Sai a jiya nake ji daga Mammah wai matarsa ba lafiya yayi tafiya. Na tabbatar ba haka bane, akwai wani motsi da yaji kuma tabbas daga na kusa dani ya jisa. Amma ina kan binciken waye yay min wannan aikin? (Nimrah 😱). Cikin satin nan zan aiki Bilal inda tsohon Drivern yake. Ka tabbatar ka bishi ka ga address ɗinsa. A daren nake son a sato min shi. Idan kun fahimci akwai matsala a canjama iyalinsa wajen zama suma”. “An gama in sha ALLAHU Sir”. “Zaku iya zuwa ku huta kafin fita operation ɗin anjima.” Dabo da Yusuf sukai salute ɗinsa suka fito. Suma basu jima ba suka dawo falo. Sai da sukai sallar isha'i suka zauna cin abincin Mammah. Dan har Imran da Faro ɗin yunsa suke ji suma. Bayan sun kammala Dada ya kalla Imran. “Imran ka canja min securitys ɗin nan na office”. “Mi yasa?”. “Kai duk basuyi min ba. Sunyi suffar munafukai da yawa. Idan kuma ka bari aka alburusheni kafin ƴarka ta tare, ALLAH fatalwa zan dinga muku”. Mugun bushewa da dariya Faro da Imran sukai. Cikin dariya Faro ke faɗin, “Anya ƴar nan taka Imran bata zo da gama ba. Gaba ɗaya ta buɗe bakin mutumin fa. Sam baida kawaici akan lamarinta”. “Ai ƴata bata wasa bace. Itama a tsaye take kamar shi. Sannan bana barci, kullum cikin tofeshi nake da addu'a a kanta”. “Lallai Boni ya cika Haysam. Wlhy tun kan ka fara surutu a gidan gwamnatin mutane ka fara masa biyayya ya barka haka”. Dada na Murmushi batare da ya kallesu ba ya furta, “Ai Alhmdllh tunda mugun ya furta abinda yake min da bakinsa. Shiyyasa kullum cikin rikita min tunani ake na haɗu da mugun suruki”. Banda dariya ba abinda Faro da Imran ke kwasa. Idan ka gansu saika rantse basu da wata damuwa ma....
>>>>>>%<<<<<<<
An sha sunan Babyn Lailah. Yarinya taci suna Khadijah. Anyi ma Gwaggo Khadijah takwara. Kasancewar abinda ya faru sunan Naseer yasa wannan karon ba'ai wani taro ba. Iya su ƴan jiki-jiki kawai suka rakashe. Nimrah da Ruƙayya suka zuba capacity abinsu. Da yake cikin ranar aiki ne su Dada duk suna office ma su. Washe gari sun tiƙi aikin gyaran gidan da safe sunata wayyo-wayyo kuma Mammah tace suyi shirin islamiyya. Tunda an koma hutu shiririta ta ƙare kuma. Suma da yake sun gaji da zaman shargallen ba boko ba islamiyyar sai basu nuna damuwa ba. Ɗan shagalin da akai ne dama yasa duk suke jinsu a gajiyen. Su Gwaggo Khadijah ma sun tafi. Gidan ya zama daga su sai su. Sai su Hanoon da suka zame musu ƙayar kifi a maƙoshi. Ta wani fannin kuma daɗi suke ji na barinsu da akai, dan ba ƙaramin ƴar tsama suka saka musu ba. A yanzu ma har Dayyan dake babba basu bari ba. Jira suke kawai wani ya shiga gonarsu a cikinsu su karta masa rashin m.
Su Nimrah sun koma Islamiyya. An kuma kawo wata malama na musu lassing a gida game da jarabawar ssce da zasu zana. Wadda basu san da hakan ba sai randa malamar ta fara zuwa. Abin ya basu matuƙar mamaki. Har suka kasa shanyewa suka tambayi Mammah miyasa zasu zana ssce, a wannan shekarar fa zasu shiga ss3 ɗin. Mammah tai murmurshi, tare da zaunar da su cike da hikima ta fara musu nasiha. Musamman akan abinda ke faruwa. Ta ɗora da faɗin. “Ai abin farin ciki ne zaku shiga jami'a da ƙarancin shekarun ku. Yanzu kuna gab da cika sha bakwai, dan inaga ke Nimrah nan da kwana huɗu ne. Ruƙayya kuma baifi goma ba. Idan ALLAH ya saka mana hannu sanda zaku cika ashirin kun gama jami'a ko kuna gab da gamawa. Ƴan gata kawai ke samun haka fa”. Daɗi ne ya kama su, dan sun fahimci Mammah yanzu kam. Musamman ma da suka ji batun shiga jami'a. Dama Yaya Mu'azz nata musu iyayi shi ɗan jami'a, to yanzu zasu haɗu su jame, suma za'a daina kiransu yara. Rungume Mammah sukayi. Itama tai dariya ganin ta samo kansu. Yaranta iyayen rikici ne, amma zukatansu masu sauƙin ne wajen fahimtar abubuwa. Basu da tsawwalama kai damuwa. Yanzu haka akan batun auren nan na Nimrah da Muhammad hankalinta ya tashi ne da tunanin Nimrah zata ɗaga hankalinta. Amma sai taga saɓanin hakan, bata san mi Muhammad ɗin ya faɗa mata na lallashi ba da har ta shanye komai. Dan ita dai tun ranar tama kasa ce mata komai. Amma tanata addu'a da gayama UBANGIJI ya saka soyayyar Muhammad ɗinta a zuciyar Nimrah batun yanzu ba, shima ALLAH ya saka masa soyayyar Nimrah. Kuma Alhamdullah UBANGIJI ya amsa mata, dan tun dawowarsa gida ta fahimci yana son Nimrah, yana dai shanyewa ne kamar yanda halayyarsa take. Sannan itama a yanzu Nimrah ta fahimci tana son Muhammad, ƙuruciya ce kawai ke ɗawainiya da ita bata gane komai...........✍️