Kenza eBookz
Cover art for L U'U L U'U BOOK 3 PAGE HAUSA NOVEL PAGE 41

Post

L U'U L U'U BOOK 3 PAGE HAUSA NOVEL PAGE 41

.....I'm losing my control" She moved her lips and said slowly, but she left her heart and the skin of her mouth the secret of what she wanted to say. She felt as if she was going to say it, but something was suppressing her words. She closed her eyes and felt something was making her face. If he lost his mind by holding her for a few minutes, he could understand the slowness of her breathing, the sweat on her forehead, and the moisture that he felt from the bed where his hands were lying on the side He was going out with some kind of calmness. He didn't know that he was asleep, because he was sweating so much.

Standalone post1,907 words

💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 41*

Cikin qasa da second biyar taji gaba daya an zare mata sha'awar yunqurin qwatar kanta da takeyi.....cikin qasa da second biyar ta soma jin wani irin mani'imcin dumi yana ratsata.....cikin qasa da second biyar ta soma jin wata irin nutsuwa me aminci tana mamaye gangar jikinta da ruhinta gaba daya.

Numfashi taja me nauyin gaske,wanda ya zuqo mata anihin qamshinsa na gasken gaske dake tashi da laushi a gargasar dake qirjinsa wadda tafi kowanne luxury pillow data taba using saboda bacci santsi laushi da wani irin calmness.

"Oud Wood,Baccarat Rouge,Amouage Interlude,Midnight Oud,Royal Ember,His Scent" dukka cikin turarukan ta gaza gano wanne ne ainihin turarensa?,wanne irin qamshi ne wannan me azabtar da zuciya?.

Qamshinnan nasa… mai ɗumi da laushi… yana manne da shi a dukka wani yanayi na rayuwarsa,dare ko rana,kamar wani bangare na jikinsa,wani abu ne da ba a iya mantawa da shi ko bayan ya tafi.

"Zan zauce......please,kaman ina loosing control dina" Ta motsa labbanta tana fada a hankali,saidai ta barwa zuciyarta da fatar bakinta sirrin abinda takeson fada din. Tana jin kamar ta furta,amma wani abu yana danne mata kalmominta. Ta lumshe idanunta tana jin wani yanayi yana fusgarta.

"Me nakeji?,ya Allah" Ta fada tana lumshe idanunta,wani irin feeling da bata taba jinsa ba yana taso mata,saidai bata kalleshi da idanun ma'anarsa ba,sai wani abu na daban.

Idan yace ya rasa hayyacinsa da ita riqon daya mata kawai na wasu mintuna bazai qaryata ba. Abu daya ya iya ganewa,saukar numfashinta a hankali,da gumin da yake goshinta wanda ya fara ratsa fatar qirjinsa,sai damshin da yaji daga gadon bayanta inda tafukan hannayensa ke kwance a gurin saboda tsaro....gudun qetare iyaka,tabbacin zazzabin da yayi mata mummunan kamu ya sauka kenan.

Yayi shuru yana jin yadda jikinta ya sake gaba daya.....yana jin yadda iskar numfashinta ke fita da wani irin nutsuwa. Koda ba'a gaya masa ba ya sani bacci ne ya dauketa,irin baccin nan dake cike da nutsuwa me yawan gaske.

Tunda ta fara gumi dole ya rage duvet din da suke ciki,ya yayeshi gefe yana kallon window da yake ganin fatsi fatsin ruwa,daya saurara sosai sai ya fahimci ruwan sama ne yake sauka,wannan ya sanya wani sabon zafin tasowa. Yabi siririn hasken dake shigowa dakin ta tsakanin labulen dakin,wanda ya sauka direct a kafadunta.

Ya sauke idanunsa a hankali,mamaki kadan yana kamashi,duk da cikin duhu ne amma hakan bai hanashi ganin glowing skin nata ba.

"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel" Ya furta yana jin wannan abun daya danne yana taso masa yana kuma nema yafi qarfinsa fiye da dazu.

Cikin ransa yakejin inde bai tashi ba.....inde bai canza makwanci ba komai yana iya faruwa. Ya fara rasa control dinsa......ya fara jinsa sama sama......ya fara jin kamar numfashinsa yana neman qwace masa.

Ya yunqura sosai zai miqe,daidai sanda akayi wata tsawa data sakata farkawa daga baccin daya mata wani irin dadi. Ba tare data shirya ba ta damqeshi da kyau tana sake qanqame hannuwansa a muhallin da yakejin hadarinsu a tattare dashi yafi hadarin bindiga me bullet.

Tun ba yau ba....tun a wancan ranar ya gama karantar tana tsoron tsawa,amma a yanzun kalan riqon data masa bazai harfar musu da d'a me ido ba. So yake ta sakeshi,ta gyara kwanciyarta,ya kunna Ac,ya dawo ya kwanta koda daman sofa bed ne ko saman Normal sofa,don tunda aka fara ruwa yasan shima bazai barta ba,ba zata iya kwana ita daya ba

"Sakeni" Ya samu ya furta da qyar,don bayajin zai iya mata dogon jawabin ba tafiya zaiyi ba.

"Tsoro nakeji don Allah" Ta fada muryarta na rawa,hankalinta yana kan window din,saboda walqiyar da ake sakeyi ta tabbatar wata tsawar a gaba na nan zuwa,ba kuma tare data lura da muhallin da taketa riqe masa hannu ba.

"Ki sakeni mana" Ya sake fadi wannan karon yana dan kausasa muryarsa kadan saboda ya fara loosing control dinsa.

"Kark......" Ragowar kalaman dukka basu gama fita ba tsawa ta biyu ta biyo baya,wadda shi kansa ya jita,bai gama fahimtar komai ba kuma ya jita cikin jikinsa da wata irin kalar runguma me tsaurin gaske.

Kuka yake qasa qasa,kukan da yake iya jin qananun sautikansa a qirjinsa. Bappi take kira,kamar wata qaramar yarinya,yadda kuma take kukan zai fada maka daga can cikin zuciyarta ne.

A gurinta ne sautin yake kuka,amma a gurinsa tamkar sautin gayyata ne take aike masa zuwa wata duniyar ta daban. Yayi duk dabarar da zai qwace amma yadda ta riqeshin ma sake zare masa duk wani karsashi take sakeyi.

Tsaiwa yayi cak yana jin yadda kunnuwansa suke nisa da duniyar da yake ciki.....hankalinsa yake dada nisa dashi.....tunaninsa yake sake dauko masa wani yanayi na musamman........kaman yadda duk wani sake shige masa jiki da takeyi yakejin kamar tana tura masa komai da komai ne wanda direct yake isa ga fatarsa. Wani sabon salon skin to skin yakeji tana masa.....wani yanayi me firgita hankalin me hankali,da jirkita nutsuwar me nutsuwa duk kuwa kalan nutsuwar da yake tutiyar ya mallaka.

Bashi da wani zabi face bin abinda zuciyarsa take ayyana masa,a hankali ya dora hannuwansa guda daya akan bayanta,daya hannun nasa kuma ya riqe bayan kayanta da kyau,hannuwansa suna nutsewa cikin sassalkar sumarta.

Fuskokinsu ya hade guri daya,tsinin hancinsa ya sauka akan nata,sai ya soma gogawa a hankali yana fadin.

"Aakhnaaan" Da wani irin rarraunan sauti daya sanya tsigar jikinta tashi.

"Na'am" Ta amsa tana qoqarin dauko tunaninta ta dawo dashi gabanta. Sake kiranta yayi,ta sake amsawa,a karo na uku kuma daya sake kiran nata sai kiran ya fito a wani irin zafafe,ya hada kuma da saukar hannunsa saman wancan gurin da ta kawo masa da kanta ba tare data sani ba.

A nan duk wani lantarki na jikinta ta tsinke,a nan ne tunaninta da yayi nisa a dazu ya dawo,ya karanta mata cewa suna saman gado daya,bata da riga baida riga.....tunaninta ya sake karanta mata wani irin saqo me wahalar fassara data soma jin yana aike mata,tunaninta ya sake finciko mata saukar hannuwansa a gurare da dama na jikinta,bata kuma sake tuna komai ba sai taji ya game bakunansu guri daya yana aike mata da wani zazzafan kiss kai tsaye baki da baki.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Wani irin nauyi yake sauke mata,nauyin dake nuna mutumin daya dade yana riqe kansa. Wani baqon abune da bata taba jin irinsa ba tunda tazo duniya.....wani irin yanayi da bata taba kawoshi zai faru a kanta ba nan kusa. Ya yaye dukkan wani hijabi dake tsakaninsu,ya kai hannunsa dukkan wani sashe da yake cikin alfarmarta da alfaharinta na diya mace,ya ajiye fuskarsa a duk wani guri da takejin yana da tsananin girma da kima da tsaro a gurinta. Ta tureshin ta kirashi da mabanbantan suna amma bataci nasara ba.....daga qarshe kawai abinda ta yanke.....kiran sunan sultane da dukkan muryarta,wani abu daya sanyashi tsaiwa cak.......jikinsa yayi wani irin laushi,ya zame a hankali yana kwantawa a gefe rub da ciki yana runtse idanunsa da kyau,ya cije labbansa na qasa sosai yana jin wannan yanayin yana ratsashi,yana lalube cikin kwanyarsa yadda zai samu relief.

Dukkan qarfinta ta sanya tana tattaro duvet din duk da girman da yake dashi tana lullube jikinta gami da curewa guri daya. Wani irin tsoro ne yake ratsata,ta tabbatar banda Allah ya mata ludufi zazzabin ya sauka ba abinda zai hana tsoro ya sanya ta shide gaba daya.

Ya damqe bedsheet din sosai cikin hannunsa kaman zai tsagashi,ya sauke wani numfashi a hankali jikinsa yana qarasa saki gaba daya. Sai a sannan sautin kukanta ya soma dawo masa cikin kunne.

"Me nayi mata ma?" Ya tambayi kansa yana tuna a daidai gurin data sanya masa iyaka. A gurin daya tabbatar inda ya isa can din da yanxun wani sunan daban zai amsa haka ita dinma.

A hankali nutsuwarsa ta dawo jikinsa,yana kuma jin sautinta a hankali,saidai haka kawai yakejin baida energy din da zai iya cewa da ita komai.

Ya kusa mintuna talatin sannan ya iya miqewa,har wani jiri yakeji bayan nauyin da jikinsa yayi masa. Ta dauka zai fita ne zuwa dakinsa,amma ga mamakinta sai taga ya wuce zuwa bathroom dinta kai tsaye.

Tana jin saukar ruwa daga bathroom din wanda ya tabbatar mata wanka yake. Jin komai take kamar a mafarki,har yanzu a gigice take jinta,ta kasa gasgata abinda ya faru tsakaninsu koda na minti daya.

"Inda ya samu nasara fa?" Zuciyarta ta jefa mata tambayar data sake sakata fashewa da kuka. Da tuni shikenan,asirinta zai tonu kenan kamar yadda na falaak ya tonu a idanunta? Tun wancan ranar bata sake bari sun hada ido da falaak ba,haushi haushin falaak din takeji,ita kuma kunyar akhnan takeji.

Da sauri ta maida kanta gaba daya ta lullube a duvet din. Haisam ne......daure da towel a qugunsa,yanayin da yayi matuqar gigitata.....yanayin da bata taba zaton zai iya aikatawa ba. Fitowarsa a haka ba riga,duk wani siffar qarfi nashi ya bayyana ta qaramin hasken bedside lamp daya kunna. Wannan lallausar gargasar da takeji kamar tana ajiyar qamshi na musamman......wannan faffadan qirjin,santala santalan hannayensa duka a fili muraran.

"Kina buqatar wanka?....akwai ruwa a bathtub fresh" Ya fada da wani yanayi na kulawa a muryarsa.

Ba shakka inda akwai daman dan adam ya bace ba abinda zai hanata bacewa. Yana mata magana kanshi tsaye,dab da kanta yadda take iya jin damshin jikinsa ta hannunta daya da bata lullube ba. Wato tambayarta yake a fakaice shin takai inda yakai?,koshi kadai ta raka ta dawo?.

Wani kukan kunya ya qwace mata. Ta tabbatar a yanzu jikinta ba inda hannunsa bai kai ba,ba inda hannunsa bai taba ba,shikenan bata da wani sauran martaba da daraja?. Ya akayi ma ta barshi har saman gadonta?,ba'a kansa kadai ba,tasha ganin kallon sha'awa a kanta daga idanun maza masu tarin yawa,wannan dalilin ya sanya ta tsani kallo daga idanun kowanne d'a namiji.

Bata taba ganin ya mata wannan kallon ba,shi yasa ta sakankance,bata taba kuma kawo hakan a ranta game dashi ba,ashe zai bata mamaki.

Mamakin kuwa yaso bata sanda yake bata zabin taje tayi wanka ko ya dauketa da kansa ya kaita. Hakanan ta tattare duvet din tayi toilet dashi,tanata satar kallonsa,saidai shi idanunsa ma baya kanta,yayi tsaye ne a saitin qofar glass dinnan dake nuna masa Haram na madeena kai tsaye.

Sau ba adadi yana lumshe idonsa yana budewa cikin haram din,wata irin tarin nutsuwa yakeji tana saukar masa. Ambaton sunan Allah kawai yake cikin ransa yana motsa labbansa kuma a hankali,yana tsarkake ubangiji,yana sake miqawa Allah godiya.

Duk da bai isa inda ya dace ya isa ba,amma ko a iya nan ya fahimci abinda zai sanya duk namiji ko.macen da suka kuskura suka fara zina a rayuwarsu zai wahala su daina.

(Duk runtsi.....duk runtsi,duk yadda za'a je a dawo ka/ki yiwa kanki katanga da zina,karki kuskura karka kuskura ka yarda ka dandanata,ka jira halal time......in halal way kuma,Allah haula da zuri'armu duka ka nesantamu da ita).

"Alhamdulillah......alhamdulillah" Yake furtawa a hankali. Wani girma da tsoron Allah yana sake ratsa zuciyarsa......imani na gaske da yaqini,irin karamcin Allah daya yiwa bayinsa.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽