
Post
L U'U L U'U BOOK 3 PAGE HAUSA NOVEL PAGE 49
..... she carefully completed that training and came out, since all the investigations he had on her said they did not find anything on him, this time she will show him the extent of her power. She didn't know what was going on, she just found herself busy checking her phone. After a few minutes, check the screen of her phone, then start going to the call center. She keeps the phone close to her for a while, she turns the phone in her hand for a while, she doesn't know what she is waiting for, she doesn't know what she is looking for. Little by little, these pictures were taken without anyone's knowledge....at different times and in different places, they became familiar to her....they became her things that every day she would not come out and see. In the end, she knew.....she let her heart have a bad news about his affairs......the news that didn't know what the reason was.....the news that didn't know what brought it......she knew she was used to it, she was used to it, she was used to it......but still there is one thing to believe in herself that is LOVE. Admitting that she loves him, she feels it is the last lie she will ever believe and her heart is broken. She knows how to
💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 49*
Suna waya da shehnaz,aisa da morsa lokaci lokaci......amma har yanzu ta gaza samun sultane sai sau daya tak. Shima maganarsu dashi gajeriya ce......ya mata wata magana a qarshe data sanyata fashewa da kuka.
"Gida nakeso na dawo bappi......gida nakeso nazo na ganka" Murmushi ya sake mata.
"Nace miki ko bayan na mutu kike kuka ko biftu?" Ya fada da murmushi
"To ko mutuwa nayi indai haisam bai lamunce kizo ki ganni ba ban yarda kizo ba.....idan kika bishi hakanne zai samawa ruhina salama koda cikin kabarina......duk da ina lafiya cikin qoshin lafiya,muna kan wani aiki ne da yake janyemin lokaci,duk sanda kika nemeni baki sameni ba....karki saka a ranki wani abu ne mara kyau,cikin aminci nake da kiyayewar Allah".
Tayita kiran aisa sa shehnaz ko zataji wani abu,amma ba wata alama data nuna akwai damuwa ko matsala cikin masarautar,haka ahmad data kira shima abinda ta gani kenan,wannan ne ya sanya mata nutsuwa a ranta,ta maida hankali ta kammala wancan training din ta fito,tunda duk binciken da tasa a mata sunce basu gano komai a kansa ba,wannan karon ita zata nuna masa adadin nata ikon.
Batasan me yake faruwa ba,tasan dai kawai ta tsinci kanta tsundum da yawan duba wayarta. Duk bayan shudewar wasu mintuna saita duba screen din wayarta,daga haka saita fara zarcewa zuwa gurin kira.
Takan jima da wayar a kusa da ita,takan jima tana juya wayar a hannunta,batasan me take jira ba,batasan me take nema ba. Sannu a hankali sai wadannan hotunan data fuskanci da yawa an daukesu ba tare daya sani ba......a mabanbantan lokuta a kuma mabanbantan gurare suka zame mata qawaye.....suka zame mata abubuwan da duk rana ranar ba zata fito ta fadi ba bata buda ta kalla ba.
Daga qarshe ta sani.....ta bari zuciyarta tayi mummunan sabo da al'amuransa......sabon da batasan meye dalili ba.....sabon da batasan meye ya kawoshi ba......ta sani ta saba ta saba ta saba......amma duk da haka akwai abu daya dataqi yarda a karan kanta cewa SOYAYYA CE.
Yarda da cewa tana sonshi tana jin shine qarya ta qarshe da zata qara yarda zuciyarta ta qulla mata. Ta sani tadade da kashe duk wani gurbi na taso wani d'a namiji a zuciyarta. Ko meye takeji ta yarda ta sallama da cewa SABO NE SILA.
Tasha kallon number daya kira a wancan ranar......amma kuma ta dade da yiwa zuciyarta bore wadda ke shawartarta ta gwada kiransa. Yasan inda zai ganta......yasan number da zai kira ya sameta,bai nemeta ba......ta yaya dalilin sabo zata bari alfaharinta na diya mace yayi qasa?.
Tana tsoron sabo ya karya wannan alfarmar don haka a wani yammaci ta dannawa number delete,amma batasan me ya sanya wani abu ya tsaye mata a wuya ba bayan ta goge number.
Ranar farko da hawaye suka cika mata idanu ranar da kewarsa ta hanata bacci. Tayita juyi,tayi alwala tayi sallah duka wannan kewar data rasa wacce iri ce ta hanata sakat.
Me yasa duk yadda na dade da sultane da kowa da kowa dake cikin masarauta bana jin girman kewarsu haka a raina?. Me yasa banquntata da yawa ba daga rashinsu a kusa dani?,saishi?.....WAYE SHI?,meye na musamman a tattare dashi da kewarsa ta dara ta kowa nauyi cikin zuciyarta?.
D'isar qwallar kawai taji saman cinyarta,sai wani irin mamaki ya kasheta.
"Qwalla akhnan?,qwalla saboda kewar D'A NAMIJI?" Ta jima jikinta a sanyaye tana jin zafin abun. Me yasa ta sake masa haka da yawa?,me yasa ta bari suka saba da ganin juna da jin motsin juna?,wanne irin sakarci tayi haka?. Hannu tasa ta dauke qwallar tana gayawa kanta,har yanzu itace dai akhnan muhammad hammud.....bai kamata ta bari wani abu ya karyata ba,amma dai daga qarshe sautinsa.....qira'arsa.....karatun qur'aninsa ta kunna da qaramin sauti can qasa,shine abinda ya sama mata nutsuwar data samu yin bacci a wannan daren.
★★Duk zirga zirgar daya yini cikinta tsakanin gidan prime minister da gidan governor na jimma a yinin ranar data zama ta qarshe tun daga safiya zuwa yanzun da sararin samaniyar jimma ke bada wata lallausar iskar hadari hakan bai ture tunaninta ko sau daya daga ransa ba.
Baisan meye me qarfi da girma haka dake maqale da ita a zuciyarsa ba. Kwanaki ne da suka zame masa cikamakin kwanika masu muhimmanci wajen cika alqawari kan aikinsa. Yayi handling muhammad jinjiri ga ahalin ajani a sirrance bisa sharadin ba zasu bayyana dawowarsa cikin ahalin ba har sai ya kammala nasa aikin......ya rufe file na case din mutuwar ajani,ya miqawa gwamnatin qasar Ethiopia tamim babba tamim qarami da dukka qasurgumayen masu laifin da ake ci dasu cikin haramtaccen gidan villa street da ya salwantar dashi. Abu guda daya ya nema su daga masa qafa suyi masa alfarma shine,gurfanar da zaituna cikin asalin qasarta tushenta,wanda ya buqaci su bashi wasu watanni don komai yazo daidai da yadda ya tsara.
A yanzun aikin da ya yiwa qasar ba wata alfarma da tafi qarfin ayi masa ita.......bama wannan lokacin ba.....tun a bayan,yana da wani irin girma kima da martabar da gaba yake da alfarma kowacce iri ce,ballantana a yanzun. Ya sake samun wani girman na musamman,darajarsa ta sake ninkuwa,hakanan ya sake shiga cikin abubuwa masu tsada da darajar da qasar Ethiopia din ta mallaka.
Ya dauka ya kammala aikin a kwana biyun kawai,saidai ahalin ajani sun dora masa nauyin daya hada da moti na zuwa kebantaccen gurin da moti dinne kawai ya sanshi inda sauran kaso me girma na dukiyar ajani take.
Tafiyar tazo masa da wahala sosai,bai sani ba gajiya jikinsa ya fara yi ko kuwa?. Shi kansa ya sani,a wannan karon yayi aikin daya kamata ya daukarwa kansa da kansa hutu,ya bawa gangar jikinsa dama ta huta sosai. Kwanansu uku a gurin suka kammala komai,aka fidda dukiyar data bawa moti lambar yabo daya iya dauke wannan sirri na tsahon shekarun da amininsa ya buqata. Yawan adadin dukiyar daya gigita kowa,saidai moti ya shaida musu,akwai reshe daya daya rage da ajani ya fadawa wani cikin aminansu.
Sun zabi killace muhammad a tare dasu,ya saba dasu zuwa sanda haisam zai bada umarnin sadashi da dangin mahaifan safeena kakanninsa kenan.
A wannan yammacin da motocin alfarmar da suke zama tambarin prince sheikh muhammad haisam suke tafiya cikin wata irin nutsuwa saman kwaltar......idanunsa can qasa qasa cike da tarin gajiya......idanun da suke zube saman kwalta yana ganin yadda yanayin ya fara juyewa irin yanayin da yakeso......irin yanayin da tsirrai ke wani irin kyau,yanayin da tsirran ke fidda sabbin ganye masu daukan hankali,su kwantar da duk wata qura da ka iya damun dan adam da walwalarsa.
Lafiyayyen agogon fatar da yayi luf saman kyakkyawar fatarsa dake lullube da nu'imtacciyar gargasa ya kalla. Yamma tayi sosai.....amma zuciyarsa yaji tana karkata wani guri na daban a maimakon gida.
Wani guri ya dan danna daga seat din gabansa
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Mu wuce palace training home" Ya furta da wani nutsuwa da jan aji,jan aji da ginshirar data dadu saboda gajiya da kasalar da yakeji. Daga ta cikin abinda ya danna din aka dawo masa da amsa cikin girmamawa,da alama ya tura saqo ne zuwa ga driver din motar.
Maida idanunsa yayi kan kwaltar yana kallonta,kafin a hankali murmushi ya subuce masa,wani tattausan murmushi daya qarawa fuskarsa ajiyayyen kyau.
Ya sani.....kuma jikinsa yana bashi,zaije ya tarar da wani yanayi tabbas saman fuskarta. Abinda ita kanta bata sani ba.....abinda ya jima shi kuma da kara tarsa da kuma lura dashi shine. Ita din wata iri macace me son kulawa.....macace meson a damu da ita,wanda hakan qila ya samo asali ne daga fake love da fake caring na mammina. Wadda ta kadaita a dukkan komai,ta tattara kulawarta da damuwarta a kanta a zahiri ba tare data hadata komai da kowa ba. Ta tashi da wannan yanayin,ta saba dashi,shi yasa komai yake zuwa mata a baqo a duk sanda aka dauke kai daga lamarinta.
Da gaske yayi busy din da dukka wayoyinsa ma basa hannunsa,ya ajiyesu a killataccen guri. Amma behind hakan akwai wani TARKO da yakeso ya d'ana,akwai wani ANALYSIS da yakeso yayi.
Daga ranar da hannuwansa suka kai gangar jikinta,daga ranar da hannuwansa sukakai muhalli da guraben da bai taba zaton zasu je ba.....daga ranar ya tabbatar MUTUWA ce kadai zata iya sanyawa ya zare igiyoyin aurenshi daga kanta,koda mutuwar ma baya tunanin ta isa ta sanyashi yayi hakan. Daga ranar daya qetare iyakar da bai taba qetarewa wata mace ba sai a kanta,....daga ranar daya shiga wani yanayi da babu wata diya mace data taba ganinsa a cikin sa,koda kuwa nanay dinsa......daga wannan ranar ya dasawa kansa MALLAKA......ita din mallakinsa ce.....koda da kallo na idanu zaiyi bakin qoqarin hana kowacce halitta isa gareta ta hanyarsa.
Yana da kishi......yana da kishi sosai ya sani,wannan kishin bazai taba bari ya barwa wani ita ba. Koda baiji mafi girman soyayya a ransa ba.....amma ya raba wani sirri nasa da ita,ta ganshi cikin wani yanayi na fitar hayyaci,shi kuma bazai taba bawa wani d'a namiji hannuwansa sukai kan inda nashi hannun suka kai ba.
Idanunsa ya lumshe yana jin tunaninsa kawai na qarshe kaman an dora masa wuta saman zuciyarsa,sai kawai ya miqa hannu yana sassauta necktie din dake daure a wuyansa cikin lafiyayyar luxury suit din jikinsa da kalarta ta fidda anihin ma'anar kalmar KYAU a tattare dashi,ya maida idanunsa ga hanya sanda suka fada titin da zai sadasu kai tsaye da qofar killataccen gidan.
~Da wannan miskilar fuskartata take zaune birra na qarasa daure mata dogon gashinta a tsakiyar kanta. Fuskarta tayi wani fayau,wani irin ajiyayyen kyau na samun ninkin kulawa da wani sirrantattun abubuwa da batasan amfaninsu ba da suka ratsata. Da farko batasha saboda bai mata kama da abun al'adarta ba,amma daga qarshe zenabu ta zauna ta amintar da ita tasha cikin hikima. Kuma koda tasha din ya mata dadi a baki,ya mata kama da wani abunsha da sukanyi na al'adar buzaye,tun daga ranar bata sake musun sha ba.
A girmame aka nemi izinin shigowa sannan aka turo qofar,bata damu ta waiwaya ba,ta zubawa kanta idanu ta ciki madubi tana kallon yadda shigar kayan sukuwar dokin suka mata kyau.
Qoqarin kokawa takeyi da tunaninta da dukkanin iyakacin qarfinta......qoqarin koyawa kanta rayuwa takeyi dashi ko ya nemeta ko bai nemeta ba,shi yasa yau da yammar nan ta buqaci a shirya mata doki zata hau cikin gidan tayi sukuwa a faffadan filin wasannin ball dake cikin gidan.
Alitash ce,daya daga cikin hadimanta na cikin gidan,wanda sosai takejin dadin zama dasu kamar yadda suke dasu birra. Wasu irin bayi ne data rasa wanne irin horo aka musu haka na iya faranta ran ubangidansu da duk abinda yakeso a sanda ya dace?.
Ko a yau da tace tanason hawan dokin,ta dauka a yadda tsare tsarensu yake zasu hana,amma sai gashi tana cikin bathroom tana wanka suka shaida mata an gama shirya komai.
Zenabu ce kawai taso tadan mata gyara kan shigar da tayi. Wando ne skinny daya kama jikinta sosai,ya fidda kowanne lungu da saqo da tudu na jikinta,kamar yadda fingilalliyar rigar itama ta fidda dukiyar fulaninta kamar ka saka hannu ka cirosu,suka kuma fidda plate tummy dinta kamar bata taba sanya masa abinci ba tunda Allah ya halicceshi,saidai kuma daga baya ta sanya aka yiwa gurin tsarin da daga ita sai hadiman data zaba su shiga harta gama hawan nata,basu kuma sake cewa komai ba.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽