
Post
L U'U L U'U BOOK 3 PAGE HAUSA NOVEL PAGE 47
.....he was very swollen all over the stick and showed it to her. "It's just tired" She said softly with a feeling that she doesn't talk to. Even in his bones he heard the sound... he pressed his recording again and recorded a hidden memory. He is not satisfied with the words of the fight.....only the tone of her voice has any effect, what is the difference between the first call he made to her and this one, even though the call did not take much time. "Biftuuu" He called her again with the same tone that made her feel like she was going to faint. She couldn't answer him, because she knew how difficult it was, her voice came out as it should, maybe he felt hurt in her voice more than he felt before... maybe he found out something that she was avoiding and avoiding him. "There's something you don't understand," he said in a quiet voice, feeling his entire body relax. The words came to her unexpectedly, she closed her eyes tightly and her heart was pounding. There is a distance between them.....but why can he camp something?. "What?" She said slowly. "Yes" Shima did not answer with this husky voice of his and she failed to speak. Her heart kept pounding, her fear was filling her. She
💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 47*
Sosai ta narke cikin duvet din tana dora wayar saman kunnenta. Ba zatace ga yanayin data ji ba sanda muryar nan tasa me zurfi take sauka cikin kunnuwanta ba,saidai da qyar ta qwaci kalmomin amsa sallamarsa hotonsa data gama kalla yanzu yana dawo mata cikin kanta.
Ta cikin wayar yakejin kamar yana sauraron bugawar zuciyarta,shurun nata yana wani irin qonashi tare da yunqurin binne dukka jarumtarsa. Yana jin kamar da gayya tayi shurun.....kamar tasan abinda yake muradi....
"Me ya samu muryarki haka?" Yayi maganan da wani irin taushi cikin amonsa yana sake jin kamar ana tunzurashi zuwa wancan yanayin.
Idanunta ta lumshe,kamar dai dazun muryar na sake shigewa wani gurbi me girma a zuciyarta......kamar ba daga waya yayi maganar ba,kamar gashi gata haka takejin tasirin muryar a cikin jikinta.
tana jin yadda yake matsowa kusa da ita sosai,ba da jikinsa ba.......da muryarsa,da wannan yanayin yanayin kulawar tasa da take jin kanta ya kumbura sosai a duk sanda ya nuna mata ita.
"Gajiya ce kawai" Ta fada softly da wani yanayi da batasan tayi magana dashi ba.
Har cikin qasusuwansa yaji sound din......ya sake matsa recording dinsa yana sauke wata boyayyar ajiyar zuciya.
Bai gamsu da maganan data fada ba.....yanayin muryarta kawai akwai wani tasiri me banbancin tsakanin kiran farko da yayi mata da wannan,duk da tsakanin kiran bai dauki lokaci me tsaho ba.
"Biftuuu" Ya sake kiranta da sautin daya sanyata taji kaman zata shide. Bata iya amsa masa ba,saboda ta sani,abune me wahala,muryarta ta fita yadda ya kamata,wataqila yaji rauni a muryarta sama da yadda yaji a dazu......wataqila ya gano wani abu da taketa gujewa take avoiding nasa.
"Akwai wani abu da baki fadamin ba" Ya fadi da kwantacciyar muryarsa yana jin yadda jikinsa gaba daya yake sake saki. Sosai maganan yazo mata a bazata,ta ware lumsassun idanunta sosai zuciyarta tana bugawa. Akwai nisan tazara a tsakaninsu.....amma me yasa yake iya sansano wani abu?.
"Me?" Ta furta a hankali.
"Eh" Shima ya bata amsa da wannan husky voice din nasa da kasala ta cikashi fal. Ci gaba da bugawa zuciyarta ta dinga yi,tsoronsa yana cikata. Bata shirya ba sam.....bata shirya karba da fuskantar komai ba a yanzun. Me yasa yake iya gane komai ne?,wanne irin mutum ne shi?.
"Me kika boyemin?" Ya tambaya yana cize lips dinsa na qasa saboda tsigar jikinsa data sake tashi sakamakon fitar numfashinta da yaji a hankali ta cikin wayar. Kai ta girgiza da sauri da dukkan qoqarin ta nason binne koma meye takeji a kansa.
"Ba komai,me yasa zan boye wani abu?,akwai wani abune a tsakaninmu?" Murmushi me sanyi ya kubce masa wannan karon,murmushin da sautinsa yakai har kunnuwanta ya kuma sake kashe mata jiki gaba daya. Yadda tayi maganan da sauri da salo iri na son kare kai shine abinda ya d'arsa masa wani abu a ranshi,amma a yanzun bayan buqatar jin muryarta so yake hirar tayi tsaho koda kadanne......ya fara samun wani relief yanzu haka.
"Eh akwai......akwai biftuuu" Ya furta sunanta a qarshe da wani yanayi dake illata mata zuciya,saita haqura da qoqarin komai ta maida kanta ta sake kwantarwa tana sauke numfashi a hankali. Fargaba takeyi......meye a tsakaninsu?,me ya gano game da ita?,yanayinta ko muryarta?.
"Akwai akhnaaan........kewata kike" Ya fadi kai tsaye yana sake fadin sunanta a tausashe.
Idanunta ta runtse sosai,kamar wadda taga wani abun tsoro,bugun zuciyarta yana ninkuwa fiye dana dazu.
"Waye kai?,don Allah waye kai?" Ta samu kanta da jefa masa tambayar da asalinta adane take a zuciyarta,bata kuma shirya furta masa ita a yanzu ba.
Shuru na sakanni,sannan ya saki murmushi kadan.
"Wani bawa ne ni......wanda ya sanya bauta a gaba".
"Bawa?"
"Eh" Ya amsa mata kai tsaye yana son karantar komai daga muryarta.
"Bakayi kama da bawa ba" Ta fadi kanta tsaye a wannan karon tana jin takai maqura nason sanin wayeshi.
"Bakiyi kama da wadda bata kewata ba......kaman dai na fara cin nasara ko?" Maganarsa ta yanzun ta maida kwadayin son jin amsar tambayar da tayi masa.
"Kinji kewata da gaske?" Ya fada muryarsa na sake yin qasa sosai.
"Aah" Ta amsa da sauri,saurin da yake sanyashi wani siririn murmushi. A komai tana qoqarin nuna tsayayya ce jajirtacciya ce......saidai a wannan fagen.....a wannan fannin,a wannan bangaren kamar dai bata da wayo.
"Shikenan......inzo zaki sake fadi a gaba na?". Idanunta ta soma warewa sosai tana kallon duhun daya mamaye dakin. Inde da gaske zuwan zaiyi a yadda takeji zuciyarta ta narke da kowanne bugu.......a yadda takejin zuciyarta a yau kamar tana shirin fin qarfinta,zuciyarta kamar tana son d'arsa mata wani abu da takejin bai kamata da zuciyarta da rayuwarta ba.......komai zai iya karanta daga idanuwanta,wanda a yanzun sam bata shiryawa hakan ba.
Maimakon ta amsa sai kawai ta zabi kashe wayar ta cusata qasan pillow,sannan itama tabi wayar qasan pillow din tana qanqameshi sosai tana kuma jin yadda zuciyarta taci gaba da bugawa.
Wayar ya zare daga kunnensa a hankali,wani murmushi da baisan me ya haddasashi saman fuskarsa ba yana subucewa. Ya maida idanunsa saman wayar,yana juyata a hankali a hannunsa.
"Wannan shine rauninta" Abinda ya fadi kenan a hankali can qasa maqoshinsa yana motsa labbansa. Yaja iska sosai ta hancinsa yana fitarwa ta bakinsa,yana jin yadda ya samu sassauci sosai,yana kuma jin yadda jikinsa yake sakewa sosai,wata kasala tana baibayeshi.
Tunda yake a duniyarshi ba wani sauti ko murya na wata d'iya mace daya taba sanyashi a irin wannan yanayin.......baima tsaya ya saurara ba ballanta ya dasa masa komai cikin kanshi. Amma ita fa?,da sauti kawai?,da dan qaramin kusancin da baiyi zurfin da zai shiga rayuwarsa can ciki ba?,saidai kusancin yana neman masa illa da baisan iyakar inda zai tsaya ba?.
"Me yasa?" Ya tambayi kansa sanda ya sauke wata qatotuwar ajiyar zuciya yana jin yadda wankansa ya baci gaba daya. Me yasa qanqanin abu a kanta yake masa tasiri?. Me yasa yakejinta kusa dashi sosai?,bai taba jin irin wannan kusancin ba. Ta tsaya masa a tunaninsa.....itace mace ta farko da zai kalli idanunta yaji wani abu. Itace mace ta farko da zaiji muryarta yaji wani yanayi na daban tattare da shi,itace mace ta farko da zai kalli jikinta yaji tamkar ana fusgarshi.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Kiran ahmad muhammad hammud almaz shine ya katse masa tunaninsa,ya shafa wayar yana amsa kiran. Da wannan tarin girmamawar suka gaisa da ahmad,girmamawar da almaz bai banbanceta data mahaifinsa ba.
"Bani minti goma zan kiraka yanzun" Yace da ahmad.
"To in sha Allah" Ya amsa masa a girmame. Wayar ya katse,sannan ya miqe a nutse ya wuce bathroom,ya tsarkake kansa ya hado da alwala ya dawo,ya tsane jikinsa sosai,wannan gargasar data lullube ko ina na jikinsa. Ya shirya kansa cikin silk Moroccan jubah,fara qal me adon golden din zare. Wani irin kyau yayi.....ajiyayyen kyau da zaka dauka wani ado yayi bawai jallabiyya bace a jikinsa. Ya sani nanay yanzu haka tana can tana jiransa,don haka ya zura flip-flops masu taushi farare ya dauki wayarsa ya soma fita a dakin,qamshinsa yana tsayawa a duk inda ya gifta tamkar bai wuce ba. Kan hanya ya kira ahmad,yana tafiya da nutsuwar nan dake sake nuna kwarjininsa.
"Ya yanayin sultane?.....ya komai yake tafiya a masarauta?" Haisam ya fadi yana bada hankalinsa ga ahmad.
"Jikinsa yana nan kamar yadda yake......ba wani ci gaba a yanayin farfadowarsa da kuma komawarsa dogon baccinsa". Kai haisam ya gyada a nutse.
"Ka nutsu ahmad da kyau......karka karkata damuwarka da sanya idanunka akan ciwon sultane kadai.....a yanzu tarkon da kake ciki yafi wanda sultane yake ciki......ba wanda ya isa ya yiwa sultane komai a yanxu.....kai din kaine abun hari......kaine abu mafi sauqin da za'a cimma,tabaka kawai yana nufin taba ran sultane ne gaba daya"
"Bani shawara....." Ahmad ya furta. A duk sanda zaiyi magana da haisam,duk yadda yakai ga sarewa,duk yadda yakai ga mutuwar jiki da rasa fata da buri......maganganun haisam kawai suna gina wannan da gini me qarko a zuciyarsa. Yana gina masa JARUMTA.......yana gina masa YAQINI har sama da yadda yake dashi a baya.
"Banason tasan komai......banason tasan rashin lafiyarsa.....duk wanda zai iya gaya mata inaso ka shaida masa abinda nace"
"Idan da bamu hadu dakai a rayuwa ba......da yanzun a wanne mataki.muke?" Ahmad ya fada a sanyaye da wani yanayi daya sanya wani irin tausayinsa shida Akhnan samun muhallin zama na sosai cikin zuciyarsa.
"Ba azzalumai bane ku,koda babu ni Allah bazai bari ku tozarta ba" Yayi furucin da wani yanayi daya sake sanyawa ahmad nutsuwa me tarin yawa a zuciyarsa.
~Dukkanin magungunan da tasha da allurai bata ji ko guda daya da yayi mata aiki ba. Bata kuma saka ran zaiyi mata aikin,saboda ba maganin daya kamata su bata kenan ba.
Ba wanda bai shigo ya mata sannu ba.......ba wanda bai nuna kulawarsa a kanta ba,amma sai takejin wannan kulawar da komai ma sunyi mata kadan. Abinda take gani saman fuskokinsu ke sake daga hankalinta. Kowaccensu daidai da noorah auta cikin walwalarsu suke,walwalat data tabbatar tana da nasaba da isowar matar captain obbo,ta sake tabbatar da hakan kuma sanda ta fito daukan ruwa mara sanyi babban parlour din,ta samesu dukkansu wasu saman sofas wasu zaune a qasa suna sake tattauna maganarta da gagarumar walimar da zasu shirya ranar data fito daga gidan koyon rayuwa da al'adun masarauta.
Da qyar ta maida kanta daki,bata kuma sake fitowa daukan ruwan ba sai a yanzu. A daddafe take takawa saboda matsanancin ciwon da kanta yake mata,gabanta ya yanke ya fadi sanda hancinta ya fara jiyo mata wannan qamshin.
Shi kadai yake da irin wannan qamshin a duk fadin duniya cikin mutanen data sani......cikin mutanen da take mu'amala dasu. Qamshinsa na dabanne,don haka wanzuwarsa a guri ma ta zama ta daban,kamar yadda koda ya iso guri komai nasa yake banbanta dana kowa. Zataso qafafunta su bata hadin kai tayi gaggawar barin gurin kafin ya iso,amma zuciyarta ta jefawa qafafunta umarnin da har ya iso gurin ta kasa tabuka komai.
Bai lura da ita ba,har sai daya kusa shiga dan walkway din da zai sake sadashi da sassan nanay mafi kusanci.
"Barka da dare" Ta fada a hankali tana fatan idanunsa yakai kanta tana rusunar da qwayar idanunta qasa.
"Yauwa......ya jikin?" Ya fada a tausashe yana dauke idonsa daya sauke a kanta zuwa gabansa.
"Alhamdulillah" Sai ya gyada kansa a nutse ya soma takawa zuwa gaba.
"Allah ya bada lafiya" Ya fadi a nutse yana sake yin nisa da inda take tsaye.
"Ameen" Ta amsa can qasa muryarta tana rawa,tana jin yadda yake qulewa,tana jin yadda yakeyin nisa da inda take tsaye. Duk takunsa saya ruwan hawaye yake saukar mata. Iya abinda zai iyayi kenan?. Me yasa kaman damuwa da lamarinta da kulawar da a baya yake d'an nuna mata sukayi qasa sosai?,me yasa suka ragu fiye da kafin tafiyarsa?.
Me yasa bazai karanci damuwarta ba kaman yadda ya saba karantar damuwar 'yan uwansa dama kowa daya damu dashi?,me yasa bazai kalli cikin idanunta ya karanto abinda ke danqare a kansa a zuciyarta ba?. Zuciyarta tayi wani irin rauni,ruwan gorar data dauko ya fara mata nauyi a hannu,ta riqeshi sosai cikin hannun nata,ta daga qafa zata fara takawa maganansa ya mata bazatar data saki ruwan a qasa.
"Ko akwai wani ciwon da kikeji?,idan akwai ki fadawa nanay,koda asibiti ne sai a sake da tests ko?" Ya fada da kulawa. Qasa tayi da kanta tana kasa hada idanu dashi,sannan ta daga kanta a hankai.
"Da sauqi.....ina samun sauqi" Kai ya jinjina yana sake komawa hanyar walkway din
"Ma sha Allah,haka akeso". Tana sake jin yana mata nisa....har zuwa sanda qamshin turarensa ne kawai ya rage a gurin banda wannan gangar jikin da wannan kyakkyawan ruhin da take mafarkin mallaka. Tsugunnawa tayi tana laluben ruwanta daya fadi,saboda hawayen da suka cika mata idanu sun hanata ganinsa,ta aza hannunta akai ta dauka ta miqe da sauri sauri tana wucewa ciki.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽