
Post
L U'U L U'U BOOK 3 PAGE HAUSA NOVEL PAGE 48
..... who is studying but she has this problem. It's not like the first time she came.....not like before when she was staring at him from a distance......what would make her stop like this?. "Who is she?" She found herself asking herself after a long thought. As soon as his behavior is complete he realizes that he does not have any idea of dealing with women, he does not look deeply at them, this gives him relief that only she will succeed in his life. How did this person come into his life?, who is she?, why did she leave?, what is she doing?. These questions completely motivated her to want to see and know WHO AKHNAN is. Even though she is afraid, her heart is telling her who will succeed in owning the sheikh muhammad's step. When Nanay walked into the room with a cane, her face was bright with a smile that once again showed her old age and the calmness that her children inherited from her. His eyes are on her, he is looking at her with a kind of love and compassion waiting for other people to be in her life for many years without her having confidence in anything that affects them. He closed his eyes and grabbed her hands, he.....
💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 48*
Kuka sosai ta fashe dashi tana qoqarin boye kukanta don kada Aanaani dake zaune tana amsa waya ta jita. Ta lura daidai da kallo ma ba kai tsaye yake kallonta ba. Haka yake kallonsa akan kowacce diya mace yana qoqarin kauda idanunsa a kanki.....amma me yasa sai a yanzun haka yafi zafafarta?. Ta tabbatar ba irin wannan kallon yakewa matarsa ba......bama irin wannan kallon ya mata ba har yaja ra'ayinsa a kanta ba. Me yasa bazai.kalleta da dukkanin idanunsa ba kamar yadda ya kalli matarsa?. Ta tabbatar tana da dukkan wata siffa hali da dabi'a da yakeso game da d'iya mace......ta tabbatar indai zai kalleta yau gobe zuwa jibi.....lallai wataran zata samu kyakkyawan gurbi da muhalli a ransa. Ta sanshi ta karanci dukkan wata dabi'a tasa,tasan abinda yakeso tun daga kan sutura yanayin turare abinci da yanayi(weather)na gari dana muhalli,tayi kuma amfani da dukkan wannan ta fara samar da magana me dan tsaho a tsakaninsu,koda kuwa akan karatu ne amma taci wannan galabar. Ba irin farkon zuwanta ba.....ba kamar a baya ba da daga nesa kurum take hangensa......me zai sanya ta tsaya a iya haka?.
"Wacece ita?" Ta samu kanta da tambayar kanta bayan dogon tunanin data gama. A kaf dabi'arsa ta gama gane baya wani ra'ayin mu'amala da mata,baya zurfafa kallo a kansu,wannan ya bata relief na cewa itace kawai zatayi nasarar shiga rayuwarsa. Ta yaya wannan din ta shiga rayuwarsa?,wacece ita?,dame ta fita?,dame take taqama?. Wadannan tambayoyin gaba daya suka kwadaita mata son gani da sanin WACECE AKHNAN.
Duk da tana fargaba,zuciyarta kuma tana gaya mata koma wacece zata samu nasarar mallakar sheikh muhammad din tako ina ta cika mace tabbas......to amma kuma tana fata duk cikar da tayi ita ta fita ta kowacce fuska.
Tsam nanay ta miqe sanda yake shigowa dakin,fuskarta shimfide da murmushin nan da yake sake nuna dattakonta da tarin nutsuwar da yaranta suka gada daga gareta.
Shima nasa idanun suna kanta,yana dubanta da wani kalan tarin qauna da soyayya da tausayi na jiran wasu mutane data dinga yi a rayuwarta na tsahon shekaru ba tare da tana da tabbaci akan komai daya shafesu ba. Ya lumshe idanunsa yana kama hannayenta,yana jin wani irin sassauci da sanyi a ransa a duk sanda ya tuna cewa shine zai zama silar yankewar wannan jiran.....shine zai kusantata da nesanta.....shine zai zame mata tsani na sake rayuwa da mutanen da sukafi soyuwa a ranta.
"Zauna nanay" Ya fada yana zaunar da ita saman lallausan tuntum dake zube kan kilishin dake dakin. Bata musa masa ba,ta zauna shima ya dawo gabanta ya zauna saman qafafunsa yana dubanta.
"Na dauka kin gaji da jira kin kwanta". Murmushi tayi ta girgiza kai.
"Nace zan jiraka muhammad,munyi kewarka sosai.....zanso ace a yanzun haka a irin wannan yanayin surukata tana gefena kamar yadda kake zaune a gabana.....amma al'ada tayi mana wannan shamakin" Ta fada tana murmushi. Yau kawai sai yaji kunyar nanay ta kamashi,yadan sauke kansa qasa. Wai shine da mace?,shine ya auri wata macen?.
"Yaya take Muhammad.....gayamin" Da mamaki kadan a fuskarsa ya daga kai yana duban nanay din. Idanunta basu qaryata abinda ya fita yanzu a bakinta ba. Da gaske take tanason ganinta,wacce irin qauna ce wannan?,tun kafin tasan wadda ya kawo mata a matsayin suruka?,tun kafin taga wacece?. Babban abun,a duk lokaci itin wannan da zai dawo daga tafiya ba wanda Nanay takeji ko ta gani saishi,amma a yau maimakon zallar kulawar nan a kansa shi kadai ta soma rabata da wata?. Tun a ranar farko?.
"Lafiya alhamdulillah nanay" Kai ta gyada a hankali.
"Nace da hasnaaa ta bani ita a dazun muyi magana saita manta.....fatana daya ta kasance me fikira kamar yadda mijinta yake,ta kammala karbar horo cikin qananun kwanaki don ta iso cikin ahali" Qasa yayi da kansa kadan yana murmushi,shi duka ba wannan ba.....izzarta Allah yasa ta barta tayi abinda ya dace,yana fatan izzarta ta barta ta ajiye komai na agadez ta shiga practicing al'adu da dabi'un fada da masarautar aba jifar.
"In sha Allah nanay" Ya fada yana zama sosai wannan karon.
Hira suka shiga yi a tsakaninsu,irin hirar yaushe gamo. Hirar da take kama da hirar masoyan da sukayi nesa da juna. Abubuwa masu yawa suka tattauna,basa ma ko kallon abincin da tasa aka shirya kala kala daga nau'ikan abinciccikan alfarma na al'adarsu da tasan yafiso.
Ya bata labarai kala kala na yadda komai yazo masa. Zuciyarta ta karaya,tayi laushi sosai. Aikinsa a kullum rana tsoro yake sanyata na wanne irin qalubale wataran zai hadu dashi?,amma bata taba yarda ta nuna masa ba. Saboda ta sani,daga ranar daya fahimci abinda yake daga mata hankali,tayi imanin ya ajiye aikin kenan bazai sake waiwayarsa ba duk da yadda yakai ga son aikin. Bata burin ta zama sila ko sanadin hanashi wani jin dadi ko cikar buri na rayuwarsa.
Abu daya da take nacewa Allah akai wajen roqa masa shine MACE TA GARI. wadda zata zame masa sanyin idaniya.....wadda zata debe dukkan wani fargaba damuwa da hadari na cikin aikinsa......wadda zata bashi AMINCI ta kuma bashi NUTSUWA. Wadda zata soshi kaman yadda takeson kanta. Wadda zata tare kasa cutarwa.....wadda ba zata bari ya cutu ba tako ina.....uwa uba wadda zata iya dauke dukkan nauyinsa da lalurarsa ta d'a namiji......ta bashi abinda ya kauda kai daga bid'arsa duk da tarin buqatarsa akai.....yayi haquri ya jira halal dinsa.
"Nanay" Ya kirata da girmamawa bayan sun kammala cin abincin da ita ta dinga zuba masa har sai daya qoshi.
"Sheikh muhammad" Ta fadi da murmushi. Yakanyi murmushi a duk sanda ta kirashi irin hakan,sai yaji sunan kaman yafi dadi a bakinta.
"A duniya.....wanne buri ne kike fatan cikarsa kafin ki koma ga mahaliccinki?". Tayi shuru tambayar tana ratsawa cikin kanta. Tana da wasu burika na daban......amma ta sani inde ta riga muhammad rasuwa to zai iya cika mata su,koda bata gani da idanuwanta ba,amma a yanzun burin da take dashi shine taga 'yan uwanta.
"Muhammad......burina bana jin me cika ne" Ta fada a raunane. Matsawa gabanta yayi sosai,ya kama hannuwanta ya riqe cikin nasa.
"Kija numfashi sosai nanay,ki fadi duk wani burinki,a gaban muhammad dinki kike" Murmushi ya subuce mata dake hade da ruwan hawayen da baikai ga zuba mata ba.
"Na sani.....wannan jan gwarzon namijin,zakin d'ana" Maganan ya sashi qaramar dariya,duk da ba yau ya fara jin ta fadi haka a kanshi ba,amma murmushinta kawai ya sanya wani farinciki a zuciyarsa.
"Burina naga safiyya da safeena,duk da nasan zai wahala rayuwa ta bamu wannan damar" Ta fadi cikin alamun karaya da yanke tsammani.
"Idan na sadaki da koda wani abune daya shafesu......wannan burin naki ya cika?" Samun kanta tayi da qanqame hannunsa sosai har yaji hakan cikin jikinsa,idanunta cikin nasa sosai.
"Koda abinda ya shafesu ka hadani dashi muhammad inaji a jikina zai zamana kamar ka hadani dasu ne kai tsaye......amma anya...."
"Kisa a ranki a nan kurkusa wannan burin naki zai cika" Har cikin tsakiyar kanta sai da taji wani abu,mamaki ya hanata cewa komai da wata irin shakka data cika zuciyarta.
Tafi kowa sani.....ba maqaryaci bane......idan ya fada koda da wasa ne sai ya cika. Wannan ya sanya yake kiyaye harshensa akan fadin abubuwa sosai don baya fadin abinda bazai aikata ba. To amma idan ta gamsu da abinda ya fada fa?. Ta ina zai nemo mutanen da ko burbushinsu ba wanda ya sake gani ko ya sake jin labari shekaru kusan talatin?. Amma kuma gaskiyarsa wata abace da ko yaushe take sake nuna zahirin waye shi.
_ki yarda kawai nanay.....mu lu'u lu'u followers muna tayaki murna da haifar jarumi kuma nagartacce,ya rabbi kasa mun haifi sanyin idaniyarmu muma_🙏🏽🙏🏽
★★★Kwananta daya tak ta soma karbar wasu darussa na sabuwar rayuwar data dinke tunaninta tsaf. Wasu irin al'adu na girmamawa,sutura,yanayin magana da yanayin kula da miji da bata taba ganin irinsu ba.
Komai da ake qoqrin azata akai da koya mata mamaki yake bata. Tanason karanta da fahimtar dukka dalilan yin hakan. SARAUTA ta tabbatar gidan wani sarautar ya shigo......gidan sarautar dake da wani irin tsare tsare da tarbiyyar da a tunaninta bata dauka wani gidan sarauta zai kasance irin haka ba. Abu daya da bata gane ba shine......waye shi a masarautar tasu?. A rannan yace mata shi BAWA ne......amma tako ina maganarsa ta gaza shiga zuciyarta da ranta tayi tasiri. Ba wata alama ta bauta a tattare dashi......horon da ake bata kuma baiyi kama da koyarwar da za'a zauna ana yiwa matar bawa ba.
Sabuwar rayuwa take shiga......wata irin sabuwar rayuwa da bata taba sanin da zamanta a duniya ba. Sai a sannan ta tuna da zancan aisa.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Duk yadda kike ganin kinsan duniya da yawa,qasashe masu tarin yawa,kin cakuda da mutane qabila kala daban daban......amma akwai inda zaki shiga kiga kin koma kamar wadda batasan komai ba.....rayuwa gaba da gabanta ne.....kafi an fika,Allah ne kawai a sama" Tayi maganan ne tun farko farkon fara zuwan manemanta da sultane ke sahale musu ganinta. Ta raina daya daga cikinsu daya kasance d'an sarkin Cameroon,duk da tarin dukiyarsa da wayewarsa. A lokacin aisa taso ta aureshi......amma ta gaya mata ba'a halicci d'a namijin daya hada dukka qualities din da take buqata daga gurin namiji ba,auren wanda bai hada wadannan nargartar ba tabbas zai zama tozarci ne da qasqanci a tattare da ita,koma baya da rasa martabarta.
Wata irin kulawa ake bata.....wata irin girmamawa da tattalin da hatta su birra saida suka raina yadda suke kula da ita a agadez. Komai nata ya canza,daidai da fatarta tasan akwai wani abu daban dake faruwa a rayuwarta.
Qamshin jikinta ya zame mata qamshi na biyu dake debe mata kewa bayan qamshinsa.......qamshin turaruka na SHUWA INCENSE AND MORE( +234 704 229 3387) wani qamshi da yake sanyata dadewa cikin duvet duk safiya idan ta farka tana shaqar qamshin yana kai mata har cikin kwanyarta,yana kuma qoqarin kwashe mahaukaciyar kewarsa da takeji tana qoqarin hanata dukkan walwala. Ta dauka a kowacce rana zai shigo ya ganta......ta dauka kowacce rana zata zame masa ta ziyara,saidai abun mamaki babu shi ba dalilinsa. Ba kiransa a cikin kwana biyar din data dauka cikin gidan.
Amma a kowacce rana hasnaa da rumaisa da wasu mata da batasan su waye ba suna ziyartar gidan. Cikin kulawa take ta kowacce fuska,cikin kulawa da tattali take da wani irin gata daya sanya ta soma tambayar kanta,wacce irin rayuwa tayi a baya ne?,gata ne da kulawa ta samu?,ko kuma copy ne kawai na gatan ba original ba?.
Abun mamakin yadda kwanyarta ke kwashe komai......ita kanta me dora mata tsarin tana ganin mamaki qarara kwance saman fuskarta.
Bawai suna da wani qarfin ikon sauya mata rayuwa bane.....aah ta yarda tabi komai yadda aka tsara saboda tana buqatar fita daga gidan. Tana buqatar sanin WAYE SHI?,tana da buqatar ganin anihin rayuwarsa,hakan kuma dukka ba zata samu ba sai tayi qoqarin maida kanta yadda sukeso.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽